Sashe 52
Tabarmar Kashi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da sauri ta daga kai tana dubansa,shima ita yake kallo,ta tsirashi da idanu,wani lafiyayyen tashin hankali ne a kwance saman fuskarsa,ta hadiye wani abu me daci da tauri,nata bacin ran yana son yin tasirin da taketa danne masa tun awannin dazu,amma kuma sai tayi wani qaqqarfan yunquri ta kauda shi gefe,ta maye gurbinsa da lallausan murmushin da idan kayi masa nazari me kyau zakasan cewa zallar yaqe ne takeyi me masifar ciwo
"Sannu da zuwa,ka dade kuma cemin kayi da wuri zaka dawo" ta fada a shagwabe kamar yadda ta saba. Wani abu me matuqar girma ya hadiye a maqoshinsa,wanda ita kanta dake tsaye tana iya ganin yadda maqwallatonsa maqogaronsa yayi sama sannan yayi qasa,mummunar faduwar gaba da kokwanto suka lullubeshi,yayi namijin qoqarin qaqaro murmushin da yafi kama da kuka,cikin sanyin murya yace
"Eh......na dan tsaya ne,momee na raka wani guri" murmushi ta kuma saki tana gyada kai,amma kuma zuciyarta na wani irin qonewa,ba zata iya ci gaba dayi masa wannan murmushin tana kallon fuskar da take da mugun baqi a idanunta ba,don haka ta waske ta hanyar juyawa zuwa ga ledar tana cewa
"Let me see me aka kawomin" baice komai ba sai cika qofar da yayi ya juya ya fita a dakin,ta daga kanta a hankali tana sakin ledar ta fadi qasa,tabi qofar daya bar mata a bude da kallo,ruwan hawaye suna cika idanunta,dukkan wani tabbaci da yaqini yana sake samuwa a tatttare da ita.
A daren babu wani abu data iya ci,hakanan bata sake ganin adam ba,sai sintiri da motsinsa me qarfi data dinga jiyowa daga dakinsa zuwa parlor,haka ta duqunquna cikin duvet,idanunta a runtse zazzabi yanason kamata.
Sai wajen sha biyu saura sannan ya shigo dakin,har a sannan tana kwance ne kawai idanunta sun soye,babu wani alamun bacci,tana ga monitoring motsin adam din. Yana kunna fitilar dakin ta miqe tana hamma tamkar daga bacci ta tashi,ta kalleshi suka hada idanu tana mutstsuka ido
"Kada kacemin sai yanzu ka shigo?,har nayi baccin farko?" Ta fada tana qare masa kallo,daga shigowarsa gida zuwa yanzu har wata rama taga yayi,fuskarsa ta fada,ya firgice gaba daya
"Eh sai yanzu......ina wani aiki ne"
"Maimakon ka kirani na tayaka saika barni nayi bacci ni kadai?" Ta saje fada a shagwabe,kamar amma gasa zuciyarta,bata iya jin amsar daya bata ba,sai kansa daya shafa.
Saukowa tayi da niyyar zuwa tayi fitsari sannan ta daura alwala ko zataji sauqin zuciyarta,amma mararta ta riqe gam,saita zauna daga bakin gadon tana cije lebe,kanta a qasa tana ambaton sunan Allah
"Yau su waye da waye sukazo gidan nan kam?" A hankali ta daga kai ta kalleshi,yana zaune gefan gadon ko kayan jikinsa baiyi nufin cirewa ba,kai ta girgiza
"Ai yau ni kadai ka bari a gidan na wuni kamar tsohuwar mayya" ta amsa masa tana kafeshi da ido,sai ya danyi jim sannan ya zame ya kwanta kamar wanda zazzabi ke shirin saukar masa.
Koda ta dawo kwanciyar ta tayi,ta kuma saki jiki sosai kamar wadda ke bacci,tana jinsa yanata juyi,ta kwanta ya tashi ya miqe ya fita ya dawo,har zuwa sanda addu'a taci qarfin idanunta baccin da takewa kanta fata yazo.
Washegari bayan ta farka daga baccin daya dauketa bayan sallar asuba baya dakin,data fito falo sai taji motsinsa a bedroom dinsa,koda fa leqa ya yiwa komai na dakin filla filla
"Halan furniture zaka sake mana?" Ta fada tana dariya,ba fara'a ko daya a fuskarsa,sai kai daya girgiza
"Sanitation nakeyi" ya amsa mata a taqaice
"Ya kamata, shikenan yau bari na fansheka na hada mana breakfast" bata jira cewarsa ba ta juya ta fice.
Tana girkin tunani fal zuciyarta da ranta, sauqinta daya tun jiya bata fasa kiran sunan Allah a baki da zuci ba,tana samun raguwar quncin sosai da sukunin zuciya,tanason gayawa afifa,to amma ta tabbatar yadda afifa keda haushin adam komai ma zata dagulashi,ashe akwai abinda 'yaruwarta keji a jikinta shi yasa ta tsani adam har haka?,me yasa ita bata taba jin komai a kansa ba?,sai tarin yarda da aminci?,ko don ita za'a jarraba?,shi yasa komai nasa yayi tasiri a kanta?,bata taba manta yadda haduwarsu da adam ta samo asali,a b u k,yana level 400 gab dasu fara final exam,tana level 200.
Sam adam ba ajinta bane,hasali ma sãahar din tun a sannan da take da shekaru qanana she has a CHARISMA that attract many people to her,ba kowanne namiji ke iya tararta da sunan soyayya ba,amma adam din ya daukarma ransa saiya siya soyayyarta,yana da baiwar BAKI da IYA TSARA MAGANA(abubuwa biyun dake cutar 'yammatan wannan zamanin kenan game da maza),tun daga randa ya bayyana mata soyayyarsa tayi gaba a wajen ta barshi kamar sauran samarin dake yawo a kanta,ya shiga ya fita yasan komai a kanta,ya zaqulo dukkan wani abu dake burge sãahar,abinda tafiso da wanda bataso,ya maida kansa irin wannan mutumin sak,a duk inda yasan zasu hadu,sai yayi wani abu daya tabbatar zai burgeta ko kuma yana cikin likes dinta.
Ya jima yana bibiyarta da rayuwarta kafin ta daina ganinsa tsaf,abinka da zuciya da akace tanason me kyautata mata,tana kuma qin me munana mata,tun bata damu ba har ta fara jin babu dadi,basa makaranta daya da afifa,afifa na northwest a sannan,a b u k din da take kuma ita bamai kule kulen qawaye bace,tana da mugun miskilanci sosai,idan kaga sakewarta to irin iyayen nan masu zuwa da qananun yara,a nan ne zaka ga jerarrun fararen haqoranta,wannan din kuma sai ya sanya mata farinjini sosai gurin matan,gefe guda ga mazan dakeson miqa soyayyarsu a gareta,wadanda sukasan ita din me ajice kuma tafi qarfin ajin ajinsi,suna fatan koda abota ko qawance tayi dasu uwa uba tana da wata irin basira,tana da brain qwarai da gaske,wadan nan su suka sanyata zama sananniya sosai.
Sai bayan wani lokaci sannan ya dawo,ko a sannan bata sake masa yadda yakeso ba,saidai an samu improvement akan yadda suke a baya,da wannan ya samu qofa ya kuma baje duk wata basirarsa,wadda sai data kusa qarewa tasss kafin ya samu dasa qaqqarfar soyayyarsa a zuciyarta.
Bai mata qarya ba ya gaya mata wayeshi,su din ba masu shi bane,yana rayuwa ne da mamansa wadda ita ke daukar nauyin karatunsa da komai nasa,yana fargabar gidansu kamar ba zasu bashi aurenta ba,amma da yake Dr mamman girema dattijone,duk da yadda ya muhyi da yaa Saifullahi sundan nuna basaso,abinda ya tsayawa adam a rai kenan,amma dr mamman ya tsaya akayi komai,ba takurawa ba tsawwalawa,abinda ya girgiza kowa ya bawa kowa mamaki. A irin zallar kyau tsarin halitta gata da kuma aji na sãahar,ba wanda ya taba kawowa zata auri mutum me qaramin matsayi da matakin wadata a rayuwa irin ADAM. Sam ita ba wannan take dubawa ba,mutum ce da bata dauki rayuwarta da zafi can can ba, soyayya da kulawar da momee din adam ke nuna mata kawai ta isa ka kalla ka qara kalla,duk da cewa farko farkon aurensu,wata irin tsana ta yiwa afifan,qiri qiri ta nuna bata sonta,wanda ba wanda yasan meye dalili,amma dare daya komai ya canza,ta sata a jikinta da soyayyar da ko adam din bai sameta ba.
Tun asali haka kawai wata irin rashin jituwa ke a tsakanin afifa da adam,wanda sai a wanann lokacin sãahar din wasu abubuwan suka fara zuwa kanta,ta fara tariyar dalilin da abubuwan daka iya jawo haka,ciki harda wannan yanayin data tsinci kanta a ciki a yanzu.
A sauqaqe ta hada simple breakfast,ta samu ta durawa cikinta tea da chips ta miqa masa ta wuce nata dakin.
Wanka tayi ta shirya kanta cikin sauqaqan kaya,tana cikin hutu ne data dauka a gurin aiki saboda yanayin laulayinta me dauke da ciwo,don haka ta shirya kanta cikin wata simple gown,ta koma saman gado tayi kwanciyarta ba tare data sake koma masa ba,zuciyarta cike da tunanuka iri daban daban,duk da yadda taketa qoqarin hana kanta,ko don lafiyar abinda yake cikinta.
Tana jinsa yana waya sama sama amma bata iya tantance ainihin abinda yake fada,sai kai kawonsa lokaci zuwa lokaci,kusan awa biyu cikakku sannan ya tura qofar dakin nata,tana daga kwancen ta daga kai ta kalleshi,gaba daya yayi wani hajaran majaran dashi,suka hada ido,yau ko yaqen da yake ta qoqarin mata tun daga jiya zuwa yau ya kasa,sai haqora daya bude mata kawai
"Ko zaki tashi kema ayi miki sanitation din?" Idanunta tadan juya kadan,baqincikinsa yana sake cikata,ta gama fahimtar inda ya dosa tsaf,don haka hankali kwance tace masa
"Ka manta kowanne wata daga gida ina kiran masu aiki suyimin irin wannan gyaran?"
"Na sani,yau ni nake sha'awar nayi miki" ya fada adan diririce da kuma alamun zaquwa,bata sake ce masa komai ba,ta miqe tsam ta kwashe duvet dinta tayi hanyar falo,don wani sanyo sanyi takeji dake nuna alamun zazzabi yana tafe.
Tun idanunta suna kan tv tana sauraren motsinsa daga dakinta har baccin da bata samu isashe ba daren jiya yazo ya sureta,baccin da babu komai cikinsa sai takura da mafarkai marasa dadi,wannan ya sanya batayi nisa ba ta farka,mararta ta cika da fitsari,ta yaye duvet din ta sauke qafafunta qasa ta nufi bedroom dinta.
Yana zaune saman bedside drawer dinta,ya aza dukka hannayensa guda biyu saman kansa ya dafe,kamar wanda mummunan ciwon kai ya cimma,ya maida komai inda ya jawoshi,saidai dakin ba abinda yayi face hargitsewa,ta san za'a rina,don bashi da cikakkiyar nutsuwar maida mata dakinta yadda yake,kawai ta barshi ne don taga iyakacin gudun nasa ruwan,ta kuma sake badda tunaninsa.
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400
Pay at👇
1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim
Sai katura shedar biyanka anan👇
09032345899
Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070
*Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din*
+22799643131
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
*H U G U M A*
*_TABARMAR ƘASHI_*💔
https://arewabooks.com/u/huguma
Page 47
Toilet din ta wuce abinta,sai da tayi fitsarin ta sake daura alwala sannan ta fito,zuwa sannan ya sauke dafe kan nasa da yayi,ya goge hannuwansa a qirjinsa,suka hada ido,ta janye nata idanun tana bin dakin da kallo kafin ta sauke a kansa
"Sannu da zuwa,ka dade kuma cemin kayi da wuri zaka dawo" ta fada a shagwabe kamar yadda ta saba. Wani abu me matuqar girma ya hadiye a maqoshinsa,wanda ita kanta dake tsaye tana iya ganin yadda maqwallatonsa maqogaronsa yayi sama sannan yayi qasa,mummunar faduwar gaba da kokwanto suka lullubeshi,yayi namijin qoqarin qaqaro murmushin da yafi kama da kuka,cikin sanyin murya yace
"Eh......na dan tsaya ne,momee na raka wani guri" murmushi ta kuma saki tana gyada kai,amma kuma zuciyarta na wani irin qonewa,ba zata iya ci gaba dayi masa wannan murmushin tana kallon fuskar da take da mugun baqi a idanunta ba,don haka ta waske ta hanyar juyawa zuwa ga ledar tana cewa
"Let me see me aka kawomin" baice komai ba sai cika qofar da yayi ya juya ya fita a dakin,ta daga kanta a hankali tana sakin ledar ta fadi qasa,tabi qofar daya bar mata a bude da kallo,ruwan hawaye suna cika idanunta,dukkan wani tabbaci da yaqini yana sake samuwa a tatttare da ita.
A daren babu wani abu data iya ci,hakanan bata sake ganin adam ba,sai sintiri da motsinsa me qarfi data dinga jiyowa daga dakinsa zuwa parlor,haka ta duqunquna cikin duvet,idanunta a runtse zazzabi yanason kamata.
Sai wajen sha biyu saura sannan ya shigo dakin,har a sannan tana kwance ne kawai idanunta sun soye,babu wani alamun bacci,tana ga monitoring motsin adam din. Yana kunna fitilar dakin ta miqe tana hamma tamkar daga bacci ta tashi,ta kalleshi suka hada idanu tana mutstsuka ido
"Kada kacemin sai yanzu ka shigo?,har nayi baccin farko?" Ta fada tana qare masa kallo,daga shigowarsa gida zuwa yanzu har wata rama taga yayi,fuskarsa ta fada,ya firgice gaba daya
"Eh sai yanzu......ina wani aiki ne"
"Maimakon ka kirani na tayaka saika barni nayi bacci ni kadai?" Ta saje fada a shagwabe,kamar amma gasa zuciyarta,bata iya jin amsar daya bata ba,sai kansa daya shafa.
Saukowa tayi da niyyar zuwa tayi fitsari sannan ta daura alwala ko zataji sauqin zuciyarta,amma mararta ta riqe gam,saita zauna daga bakin gadon tana cije lebe,kanta a qasa tana ambaton sunan Allah
"Yau su waye da waye sukazo gidan nan kam?" A hankali ta daga kai ta kalleshi,yana zaune gefan gadon ko kayan jikinsa baiyi nufin cirewa ba,kai ta girgiza
"Ai yau ni kadai ka bari a gidan na wuni kamar tsohuwar mayya" ta amsa masa tana kafeshi da ido,sai ya danyi jim sannan ya zame ya kwanta kamar wanda zazzabi ke shirin saukar masa.
Koda ta dawo kwanciyar ta tayi,ta kuma saki jiki sosai kamar wadda ke bacci,tana jinsa yanata juyi,ta kwanta ya tashi ya miqe ya fita ya dawo,har zuwa sanda addu'a taci qarfin idanunta baccin da takewa kanta fata yazo.
Washegari bayan ta farka daga baccin daya dauketa bayan sallar asuba baya dakin,data fito falo sai taji motsinsa a bedroom dinsa,koda fa leqa ya yiwa komai na dakin filla filla
"Halan furniture zaka sake mana?" Ta fada tana dariya,ba fara'a ko daya a fuskarsa,sai kai daya girgiza
"Sanitation nakeyi" ya amsa mata a taqaice
"Ya kamata, shikenan yau bari na fansheka na hada mana breakfast" bata jira cewarsa ba ta juya ta fice.
Tana girkin tunani fal zuciyarta da ranta, sauqinta daya tun jiya bata fasa kiran sunan Allah a baki da zuci ba,tana samun raguwar quncin sosai da sukunin zuciya,tanason gayawa afifa,to amma ta tabbatar yadda afifa keda haushin adam komai ma zata dagulashi,ashe akwai abinda 'yaruwarta keji a jikinta shi yasa ta tsani adam har haka?,me yasa ita bata taba jin komai a kansa ba?,sai tarin yarda da aminci?,ko don ita za'a jarraba?,shi yasa komai nasa yayi tasiri a kanta?,bata taba manta yadda haduwarsu da adam ta samo asali,a b u k,yana level 400 gab dasu fara final exam,tana level 200.
Sam adam ba ajinta bane,hasali ma sãahar din tun a sannan da take da shekaru qanana she has a CHARISMA that attract many people to her,ba kowanne namiji ke iya tararta da sunan soyayya ba,amma adam din ya daukarma ransa saiya siya soyayyarta,yana da baiwar BAKI da IYA TSARA MAGANA(abubuwa biyun dake cutar 'yammatan wannan zamanin kenan game da maza),tun daga randa ya bayyana mata soyayyarsa tayi gaba a wajen ta barshi kamar sauran samarin dake yawo a kanta,ya shiga ya fita yasan komai a kanta,ya zaqulo dukkan wani abu dake burge sãahar,abinda tafiso da wanda bataso,ya maida kansa irin wannan mutumin sak,a duk inda yasan zasu hadu,sai yayi wani abu daya tabbatar zai burgeta ko kuma yana cikin likes dinta.
Ya jima yana bibiyarta da rayuwarta kafin ta daina ganinsa tsaf,abinka da zuciya da akace tanason me kyautata mata,tana kuma qin me munana mata,tun bata damu ba har ta fara jin babu dadi,basa makaranta daya da afifa,afifa na northwest a sannan,a b u k din da take kuma ita bamai kule kulen qawaye bace,tana da mugun miskilanci sosai,idan kaga sakewarta to irin iyayen nan masu zuwa da qananun yara,a nan ne zaka ga jerarrun fararen haqoranta,wannan din kuma sai ya sanya mata farinjini sosai gurin matan,gefe guda ga mazan dakeson miqa soyayyarsu a gareta,wadanda sukasan ita din me ajice kuma tafi qarfin ajin ajinsi,suna fatan koda abota ko qawance tayi dasu uwa uba tana da wata irin basira,tana da brain qwarai da gaske,wadan nan su suka sanyata zama sananniya sosai.
Sai bayan wani lokaci sannan ya dawo,ko a sannan bata sake masa yadda yakeso ba,saidai an samu improvement akan yadda suke a baya,da wannan ya samu qofa ya kuma baje duk wata basirarsa,wadda sai data kusa qarewa tasss kafin ya samu dasa qaqqarfar soyayyarsa a zuciyarta.
Bai mata qarya ba ya gaya mata wayeshi,su din ba masu shi bane,yana rayuwa ne da mamansa wadda ita ke daukar nauyin karatunsa da komai nasa,yana fargabar gidansu kamar ba zasu bashi aurenta ba,amma da yake Dr mamman girema dattijone,duk da yadda ya muhyi da yaa Saifullahi sundan nuna basaso,abinda ya tsayawa adam a rai kenan,amma dr mamman ya tsaya akayi komai,ba takurawa ba tsawwalawa,abinda ya girgiza kowa ya bawa kowa mamaki. A irin zallar kyau tsarin halitta gata da kuma aji na sãahar,ba wanda ya taba kawowa zata auri mutum me qaramin matsayi da matakin wadata a rayuwa irin ADAM. Sam ita ba wannan take dubawa ba,mutum ce da bata dauki rayuwarta da zafi can can ba, soyayya da kulawar da momee din adam ke nuna mata kawai ta isa ka kalla ka qara kalla,duk da cewa farko farkon aurensu,wata irin tsana ta yiwa afifan,qiri qiri ta nuna bata sonta,wanda ba wanda yasan meye dalili,amma dare daya komai ya canza,ta sata a jikinta da soyayyar da ko adam din bai sameta ba.
Tun asali haka kawai wata irin rashin jituwa ke a tsakanin afifa da adam,wanda sai a wanann lokacin sãahar din wasu abubuwan suka fara zuwa kanta,ta fara tariyar dalilin da abubuwan daka iya jawo haka,ciki harda wannan yanayin data tsinci kanta a ciki a yanzu.
A sauqaqe ta hada simple breakfast,ta samu ta durawa cikinta tea da chips ta miqa masa ta wuce nata dakin.
Wanka tayi ta shirya kanta cikin sauqaqan kaya,tana cikin hutu ne data dauka a gurin aiki saboda yanayin laulayinta me dauke da ciwo,don haka ta shirya kanta cikin wata simple gown,ta koma saman gado tayi kwanciyarta ba tare data sake koma masa ba,zuciyarta cike da tunanuka iri daban daban,duk da yadda taketa qoqarin hana kanta,ko don lafiyar abinda yake cikinta.
Tana jinsa yana waya sama sama amma bata iya tantance ainihin abinda yake fada,sai kai kawonsa lokaci zuwa lokaci,kusan awa biyu cikakku sannan ya tura qofar dakin nata,tana daga kwancen ta daga kai ta kalleshi,gaba daya yayi wani hajaran majaran dashi,suka hada ido,yau ko yaqen da yake ta qoqarin mata tun daga jiya zuwa yau ya kasa,sai haqora daya bude mata kawai
"Ko zaki tashi kema ayi miki sanitation din?" Idanunta tadan juya kadan,baqincikinsa yana sake cikata,ta gama fahimtar inda ya dosa tsaf,don haka hankali kwance tace masa
"Ka manta kowanne wata daga gida ina kiran masu aiki suyimin irin wannan gyaran?"
"Na sani,yau ni nake sha'awar nayi miki" ya fada adan diririce da kuma alamun zaquwa,bata sake ce masa komai ba,ta miqe tsam ta kwashe duvet dinta tayi hanyar falo,don wani sanyo sanyi takeji dake nuna alamun zazzabi yana tafe.
Tun idanunta suna kan tv tana sauraren motsinsa daga dakinta har baccin da bata samu isashe ba daren jiya yazo ya sureta,baccin da babu komai cikinsa sai takura da mafarkai marasa dadi,wannan ya sanya batayi nisa ba ta farka,mararta ta cika da fitsari,ta yaye duvet din ta sauke qafafunta qasa ta nufi bedroom dinta.
Yana zaune saman bedside drawer dinta,ya aza dukka hannayensa guda biyu saman kansa ya dafe,kamar wanda mummunan ciwon kai ya cimma,ya maida komai inda ya jawoshi,saidai dakin ba abinda yayi face hargitsewa,ta san za'a rina,don bashi da cikakkiyar nutsuwar maida mata dakinta yadda yake,kawai ta barshi ne don taga iyakacin gudun nasa ruwan,ta kuma sake badda tunaninsa.
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400
Pay at👇
1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim
Sai katura shedar biyanka anan👇
09032345899
Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070
*Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din*
+22799643131
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
*H U G U M A*
*_TABARMAR ƘASHI_*💔
https://arewabooks.com/u/huguma
Page 47
Toilet din ta wuce abinta,sai da tayi fitsarin ta sake daura alwala sannan ta fito,zuwa sannan ya sauke dafe kan nasa da yayi,ya goge hannuwansa a qirjinsa,suka hada ido,ta janye nata idanun tana bin dakin da kallo kafin ta sauke a kansa