Sashe 75
Tabarmar Kashi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Cikin sati guda kacal da dawowar nadeeya sukayi wani irin sabawa da sãahar,sabon da ita kanta sãahar batasan lokacin da ya faru ba,kafin cikar sati biyu sai suka zama tamkar wasu 'yan uwa. Abubuwa da yawa na kula da fadeela tare suke yinsa,idan tayi wani abun,wani abun nadeeya ce zata karba.
Wani irin qaunar sãahar nadeeya takeji har cikin ranta,bata sani ba,ko don bata taso da
'yar uwa sa'arta kamar sãahar din bane? to amma kuma akwai LABIBA da HASEENA,SU din kusan zata iva cewa sun dan rayu tare,to saidai ko kadan bataii abinda takeji game da sãahar ba,ko don ita din tana da wasu dabi'u
da kuma halaye tare da wasu qualities da bata
taba ganinsu daga gurin su biyun da suke
kamar sune dolenta ba?.
Zuwan nadeeva sai ya sanya itama ta dan
sake,takan fita zuwa gida tayi wasu awanni ta
dawo,a nan ne afifa ke tsokanarta,wai nadeeya
nason qwace mata faada,tayi maganar tana
dariya. Afifa tasan labarin nadeeya kaf daha
bakin säaharduk da basu taba ganin juna ba.
Murmushi kawai säahar ta saki
"Bestie,da alama har yau bakisan matsayinki a
guri na ba" hararar wasa ta jefa mata
"Na sani mana,tunda gashi har yau kingi
amsar mahmud yadda ya dace" zancan da ya
sanyata miqewa kenan,ta lalubi mayafinta tana
maida rolling din kanta
"An ambato maqiyin naki ko?"
"No,kawai inason na biya a wankemin kaina sannan na wuce gida,yau na yiwa fadeela algawari zan dafa mata burabusko ita da nadeeya....tashi don Allah ki kaini,saiki saukeni a gida" gyara kwanciyarta afifa tay!
"Bazan iya ba,ki dauki motar ki kawai ki dinga amfani da ita"
"Kin manta ni din nanny ce?" Ta fada tana murmushi,don zuwa yanzun ita dadin sunan ma takeji,hakanan rayuwar da takeyi din tana bata wani irin nutsuwa,ta kauce daga idanun maza kwata kwata,gidan ya zame mata kamar wata mafaka
"Kina sauri ne kawai ki gudu kada ku hadu da abba" murmushi tayi tana maida agogon hannunta
"Duka koma meye zakice bazan musa ba,tashi don Allah kafin ya dawo mu hadu" hakanan afifa ta mige,ta dauko abaya ta dora saman kayan jikinta tanata mita,ta dauki key din motar tabi bayan sãahar din.
A kitchen ta tadda maama,tayi mata sallama,sai ta waiwayo tana dubanta
"Zo nan sãahar" ta kirata tana tsame hannunta daga ruwan da take wanke alayyahu,ta yiwa baaba rabi sign saita fita a kitchen din,ta barsu su uku
"Zauna" tace da ita bayan ta jawo kujeru guda biyu dake kitchen din ta zauna a daya.
Cikin mutuwar jiki kamar wadda aka yiwa tayin zama bisa garwashin wuta ta zauna
"Wannan rayuwar ba ita nake da muradin ganin kinayi ba,nafi bugatar ganinki a dakin mijinki kamar kowacce mace,kije ki sauya tunani ki kuma canza shawara" iya abinda tace kenan da ita.
Duk da kalmomin da tayi amfani dasu ba masu yawa bane amma nauyinsu ya cika mizani taf,jiki a salube ta mige ta sake iaddada mata sallamar sannan ta fito.
Tuni har afifa ta tayar da motar ta kuma barta a kunne saita shige seat din gaba ta maida murfin ta rufe,afifan tadan juya kadan ta kalleta,saita dauke kai ba tare da tace mata komai ba ta motsa motar zuwa gaba,ta saki hon kadan,baaba habu ya taso ya bude musu yana musu fatan sauka lafiya.
Suna gogarin fita a layin motar Dr mamman girema na shigowa,ya kuma gansu,don haka yasa driver dinsa yin slow da motar har suka hade a tsakiya,ya sauke Glass din motar yana duban afifa da idanunsa dake saye da gilashin garawa ido qarfin gani
"Sannu da dawowa abba"
"Yauwa sannu,ku dawo ciki,inason ganinku" hantar cikin sãahar ce ta kada,don bata manta da awa gudan da suka share dashi a waya ba wancan satin,yau din sai da tayi kamar ba zatazo gida ba,so amma zuciyartat a damu dason ganin maamanta,wannan dalilin ya sanyata fitowa.
A gofar gate afifa ta faka motarta kalli sãahar da gaba daya takejin wani rugugin tashin hankali yana sauko mata
"'Muie ko?"
"'Na shiga uku afifa,wallahi zancan mahmud ne" wani duba afifan tayi mata
"'To ai yayi kyau" da kallo tabi afifan,ganin yadda tayi hankalinta kwance bata ma wan damu ba,ga furta sunan Allah da qarfi tana runtse idonta da sauraron bugun da zuciyarta takeyi,ta bude murfin motar tabi bayan afifan.
Tuni har ya isa falonsa yana cire hularsa ya ajiye yana zare agogon hannunsa. Kamar kaiin da aka watsawa ruwa suka samu guri qasan carfet suka zauna,yanayin fuskarsa shine ya fadar musu da gaba tun baikai ga cewa komai ba,a yadda yake da sauqin kai da kuma haba haba da iyalansa,dole yanayinsa a yau ya sanyasu a fargaba.
Sosai ya zauna saman sofa yana maida bayansa ya jinginar da kujera yana dubansu daya bayan daya
"Aishatu" yayi kiran afifa da ainihin sunanta,kai tadan daga kadan sannan ta amsa
"Na'am abba"
"Me kike jira har yanzu baki gabatar min da mijin aure ba?" Shuru ta danyi tana dawurwura,saita rasa me zatace da abban. A halin yanzu tana da samari da a qalla sun kusa mutum hudu,kuma dukkansu da aure suke sonta,saidai babu wanda ta maida hankalinta a kansa
"Na sani nasan komai,saboda haka kije na baki wata uku ki karancesu ki fitar da wanda kikeso a cikinsu"
"' In sha Allah abba" dauke dubansa yayi ya mayar kan sãahar,a jikinta taji irin duban da yayi mata,wasu daga cikin maganganunsa kuma suka dawo mata
"Na miki alfarma na kuma daga miki qafa saboda banason na matsanta miki,na kashe miki gishirwar yin aikin duk da sam aikin bai dave dake ba,amma na barki kinje kinvi saboda babu haramci sai tarin lada a cikinsa..
... okaci yayi da zaki tsaya ki fuskanci
wanda yake sonki da gaskiya.
"Ummee,a ina maganarmu ta kwana? ya muke ciki?" Yayi mata tambayar da a waienta tamkar gatse ce.
"Abba‚bamu gama fahimtar juna ba" gafarsa daya ya dora kan daya
"Ta yaya zaki fahimci juna bayan akwai nisan tazara a tsakaninku?,to ni na gama nawa,na gama fuskantarsa,hatta bincike nayi a kansa,babu wata matsala tattare da shi,abinda kawai ya rage shine ke ki fuskanceshi,don haka daga yau yana da lasisin zuwa gurinki zance a duk lokacin da ya buqaci baka,sannan damar fuskantarsa da kike da ita wata daya ne kacal,daga lokacin duk abinda naga ya dace zan iya yankewa" sanda ya sauka a zancan yayi daidai da jin tsargawar gumi me dumi daga kowanne sashe na jikinta,sai take jinta kamar ba'a zaune take dai dai ba,batu fa abba yakeyi na aure a karo na biyu cikin rayuwarta,bayan ko shekara hudu cikakku batayi ba daga fita daga siradin data afka ba,tayi zaton saita debe shekara koma ma babu wanda yayi mata sha awar yin aure bare akai ga batun yi mata tayinsa
"Ku tashi kuje,Allah yayi muku albarka,banason kuma kowacce takai magariba a waje ba tare data nufi inda ta dosa ba"
"To abba" afifa ta samu damar fadi,yayin da sãahar keta qoqarin ganin ta mige ta fita a falon ba tare da an samu matsala ta fadi qasa
ba.
"Kaini nasarawa kawai,na fasa wankin kan" abinda sãahar ta fadi kenan tana kwantar da kanta jikin kujerar tana jin toro da fargabar hukuncin da abban zai iya yankewa a wata gudan daya deba mata
"Aure fa kenan,aure da mahmud,ta karba sadakinsa.ta amsa sunan matarsa,har ta hada shimfida dash.
"A'uzu bi kalimatillahit tammati min sharri ma khalag" taji bakinta yana furtawa bayan runtse idanunta da tayi. Kadan afifa ta waiwayo ya dubeta,sai ta mayar kan titi,a irin wannan yanayin ba kasafai ta fiya son yiwa sãahar din magana ba,don haka batace komai ba har sai da suka iso katafaren gate din gidan,tana shirin fita afifa tace da ita "Take care of yourself.... kada kie ki zurafafa tunani,kinsan dai kina da ciwon kai" kai kawai ta gyadawa afifan,ba tare dat waiwayo ba ta wuce kai tsaye zuwa qaramar qofar dake manne da gate din daha gefe ta fara knocking da wani irin sanyi da mutuwar jiki kamar wadda aka yiwa mugun duka.
Allah ya taimaketa sanda ta shigo gidan nadeeva tana tare da fadeela,ta jiyo kakacinsu a dakin nadeeyan,kamar ma game suke bugawa ita da ita,sai ta sulale ta wuce dakinta ba tare data bari sun ankara da dawowarta ba,don a yanzun kadaici kawai take bugata,batason hayaniya ko doguwar hira.
Kwance kawai tayi tana saqa da warwara,ba tabbatuwar aure a kanta ba,'ah....ambatar kalmar kadai tana sanyata fargaba da razani,wai ta yaya zata iya hada muhalli da wani d'a namiji kuma wai a kirata matarsa? iya wannan tunanin kadai juya mata kwanya yakeyi tare da gara sanyata a wata dimuwa da kuma damuwa.
Gab da magariba ta shiga wanka,ta fito ta shirya cikin wata lallausar riga me hade da wandonta,ta sanya hijab tayi sallar magariba,taci gaba da zama saman abun sallar,tana jin motsi da gilmawar nadeeya da fadeela,wani lokaci harda baaba ramatu.
Tasan ba lallai su san ta dawo ba,saboda duk wani qwan lantarki me haske ta kasheshi,sai dim light kawai.
Har nadeeya ta gota dakin ¡ilkinta ya bata kamar akwai mutum,saboda kana iya jin gamshin turaren sãahar me sanyi da baya buya yana ratsa qofar zuwa hallway din.
Komawa tayi da baya ta murda qofar,sai ta bude,ta sanya kai cikin mamaki bakinta dauke da sallama,sãahar dake shirin tayar da sallar isha'i ta dakata tana amsawa
"Antvn fadee,har yaushe kika dawo haka?,muna can muna jajenki,i called you several times amma ban sameki ba? mutuniyar tana can tana dakon dawowarkita kasa zaune ta kasa tsaye tun dazun‚bakinta da labari" dan lumshe ido tayi cikin murmushi
"Nafi awa da dawowa,na shigo ne banjin dadi shi yasa na kebe"
"Ya salam! me ya sameki?" Nadeeya tayi maganar sautin muryarta na nuna tsantsar kulawa damuwa da qauna
"It's not something serious,i felt relieved"
"Really?" Kai ta gyada tana murmushi,saboda ta hangi wani irin damuwa da kulawa da ita shigen na afifa
"Bazan gayawa faadee dinki ba,if not ta zama itace patient din,please zakiyi joining dinmu muyi dinner?" Kai tadan yada gefe
"Banajin yunwa,amma zanyi qoqari ko ban fito dinner ba,zamu hadu kafin animan"
"Is okay,Allah yasa kaffara ne'ta fadi cikin mutuwar jiki ta juya ta fice tana jawa sãahar qofar. Ajiyar Zuciya ta sauke me qarfi,tana mamakin yadda suka damu da ita da al'amuranta a lokaci guda haka.
Wani irin qaunar sãahar nadeeya takeji har cikin ranta,bata sani ba,ko don bata taso da
'yar uwa sa'arta kamar sãahar din bane? to amma kuma akwai LABIBA da HASEENA,SU din kusan zata iva cewa sun dan rayu tare,to saidai ko kadan bataii abinda takeji game da sãahar ba,ko don ita din tana da wasu dabi'u
da kuma halaye tare da wasu qualities da bata
taba ganinsu daga gurin su biyun da suke
kamar sune dolenta ba?.
Zuwan nadeeva sai ya sanya itama ta dan
sake,takan fita zuwa gida tayi wasu awanni ta
dawo,a nan ne afifa ke tsokanarta,wai nadeeya
nason qwace mata faada,tayi maganar tana
dariya. Afifa tasan labarin nadeeya kaf daha
bakin säaharduk da basu taba ganin juna ba.
Murmushi kawai säahar ta saki
"Bestie,da alama har yau bakisan matsayinki a
guri na ba" hararar wasa ta jefa mata
"Na sani mana,tunda gashi har yau kingi
amsar mahmud yadda ya dace" zancan da ya
sanyata miqewa kenan,ta lalubi mayafinta tana
maida rolling din kanta
"An ambato maqiyin naki ko?"
"No,kawai inason na biya a wankemin kaina sannan na wuce gida,yau na yiwa fadeela algawari zan dafa mata burabusko ita da nadeeya....tashi don Allah ki kaini,saiki saukeni a gida" gyara kwanciyarta afifa tay!
"Bazan iya ba,ki dauki motar ki kawai ki dinga amfani da ita"
"Kin manta ni din nanny ce?" Ta fada tana murmushi,don zuwa yanzun ita dadin sunan ma takeji,hakanan rayuwar da takeyi din tana bata wani irin nutsuwa,ta kauce daga idanun maza kwata kwata,gidan ya zame mata kamar wata mafaka
"Kina sauri ne kawai ki gudu kada ku hadu da abba" murmushi tayi tana maida agogon hannunta
"Duka koma meye zakice bazan musa ba,tashi don Allah kafin ya dawo mu hadu" hakanan afifa ta mige,ta dauko abaya ta dora saman kayan jikinta tanata mita,ta dauki key din motar tabi bayan sãahar din.
A kitchen ta tadda maama,tayi mata sallama,sai ta waiwayo tana dubanta
"Zo nan sãahar" ta kirata tana tsame hannunta daga ruwan da take wanke alayyahu,ta yiwa baaba rabi sign saita fita a kitchen din,ta barsu su uku
"Zauna" tace da ita bayan ta jawo kujeru guda biyu dake kitchen din ta zauna a daya.
Cikin mutuwar jiki kamar wadda aka yiwa tayin zama bisa garwashin wuta ta zauna
"Wannan rayuwar ba ita nake da muradin ganin kinayi ba,nafi bugatar ganinki a dakin mijinki kamar kowacce mace,kije ki sauya tunani ki kuma canza shawara" iya abinda tace kenan da ita.
Duk da kalmomin da tayi amfani dasu ba masu yawa bane amma nauyinsu ya cika mizani taf,jiki a salube ta mige ta sake iaddada mata sallamar sannan ta fito.
Tuni har afifa ta tayar da motar ta kuma barta a kunne saita shige seat din gaba ta maida murfin ta rufe,afifan tadan juya kadan ta kalleta,saita dauke kai ba tare da tace mata komai ba ta motsa motar zuwa gaba,ta saki hon kadan,baaba habu ya taso ya bude musu yana musu fatan sauka lafiya.
Suna gogarin fita a layin motar Dr mamman girema na shigowa,ya kuma gansu,don haka yasa driver dinsa yin slow da motar har suka hade a tsakiya,ya sauke Glass din motar yana duban afifa da idanunsa dake saye da gilashin garawa ido qarfin gani
"Sannu da dawowa abba"
"Yauwa sannu,ku dawo ciki,inason ganinku" hantar cikin sãahar ce ta kada,don bata manta da awa gudan da suka share dashi a waya ba wancan satin,yau din sai da tayi kamar ba zatazo gida ba,so amma zuciyartat a damu dason ganin maamanta,wannan dalilin ya sanyata fitowa.
A gofar gate afifa ta faka motarta kalli sãahar da gaba daya takejin wani rugugin tashin hankali yana sauko mata
"'Muie ko?"
"'Na shiga uku afifa,wallahi zancan mahmud ne" wani duba afifan tayi mata
"'To ai yayi kyau" da kallo tabi afifan,ganin yadda tayi hankalinta kwance bata ma wan damu ba,ga furta sunan Allah da qarfi tana runtse idonta da sauraron bugun da zuciyarta takeyi,ta bude murfin motar tabi bayan afifan.
Tuni har ya isa falonsa yana cire hularsa ya ajiye yana zare agogon hannunsa. Kamar kaiin da aka watsawa ruwa suka samu guri qasan carfet suka zauna,yanayin fuskarsa shine ya fadar musu da gaba tun baikai ga cewa komai ba,a yadda yake da sauqin kai da kuma haba haba da iyalansa,dole yanayinsa a yau ya sanyasu a fargaba.
Sosai ya zauna saman sofa yana maida bayansa ya jinginar da kujera yana dubansu daya bayan daya
"Aishatu" yayi kiran afifa da ainihin sunanta,kai tadan daga kadan sannan ta amsa
"Na'am abba"
"Me kike jira har yanzu baki gabatar min da mijin aure ba?" Shuru ta danyi tana dawurwura,saita rasa me zatace da abban. A halin yanzu tana da samari da a qalla sun kusa mutum hudu,kuma dukkansu da aure suke sonta,saidai babu wanda ta maida hankalinta a kansa
"Na sani nasan komai,saboda haka kije na baki wata uku ki karancesu ki fitar da wanda kikeso a cikinsu"
"' In sha Allah abba" dauke dubansa yayi ya mayar kan sãahar,a jikinta taji irin duban da yayi mata,wasu daga cikin maganganunsa kuma suka dawo mata
"Na miki alfarma na kuma daga miki qafa saboda banason na matsanta miki,na kashe miki gishirwar yin aikin duk da sam aikin bai dave dake ba,amma na barki kinje kinvi saboda babu haramci sai tarin lada a cikinsa..
... okaci yayi da zaki tsaya ki fuskanci
wanda yake sonki da gaskiya.
"Ummee,a ina maganarmu ta kwana? ya muke ciki?" Yayi mata tambayar da a waienta tamkar gatse ce.
"Abba‚bamu gama fahimtar juna ba" gafarsa daya ya dora kan daya
"Ta yaya zaki fahimci juna bayan akwai nisan tazara a tsakaninku?,to ni na gama nawa,na gama fuskantarsa,hatta bincike nayi a kansa,babu wata matsala tattare da shi,abinda kawai ya rage shine ke ki fuskanceshi,don haka daga yau yana da lasisin zuwa gurinki zance a duk lokacin da ya buqaci baka,sannan damar fuskantarsa da kike da ita wata daya ne kacal,daga lokacin duk abinda naga ya dace zan iya yankewa" sanda ya sauka a zancan yayi daidai da jin tsargawar gumi me dumi daga kowanne sashe na jikinta,sai take jinta kamar ba'a zaune take dai dai ba,batu fa abba yakeyi na aure a karo na biyu cikin rayuwarta,bayan ko shekara hudu cikakku batayi ba daga fita daga siradin data afka ba,tayi zaton saita debe shekara koma ma babu wanda yayi mata sha awar yin aure bare akai ga batun yi mata tayinsa
"Ku tashi kuje,Allah yayi muku albarka,banason kuma kowacce takai magariba a waje ba tare data nufi inda ta dosa ba"
"To abba" afifa ta samu damar fadi,yayin da sãahar keta qoqarin ganin ta mige ta fita a falon ba tare da an samu matsala ta fadi qasa
ba.
"Kaini nasarawa kawai,na fasa wankin kan" abinda sãahar ta fadi kenan tana kwantar da kanta jikin kujerar tana jin toro da fargabar hukuncin da abban zai iya yankewa a wata gudan daya deba mata
"Aure fa kenan,aure da mahmud,ta karba sadakinsa.ta amsa sunan matarsa,har ta hada shimfida dash.
"A'uzu bi kalimatillahit tammati min sharri ma khalag" taji bakinta yana furtawa bayan runtse idanunta da tayi. Kadan afifa ta waiwayo ya dubeta,sai ta mayar kan titi,a irin wannan yanayin ba kasafai ta fiya son yiwa sãahar din magana ba,don haka batace komai ba har sai da suka iso katafaren gate din gidan,tana shirin fita afifa tace da ita "Take care of yourself.... kada kie ki zurafafa tunani,kinsan dai kina da ciwon kai" kai kawai ta gyadawa afifan,ba tare dat waiwayo ba ta wuce kai tsaye zuwa qaramar qofar dake manne da gate din daha gefe ta fara knocking da wani irin sanyi da mutuwar jiki kamar wadda aka yiwa mugun duka.
Allah ya taimaketa sanda ta shigo gidan nadeeva tana tare da fadeela,ta jiyo kakacinsu a dakin nadeeyan,kamar ma game suke bugawa ita da ita,sai ta sulale ta wuce dakinta ba tare data bari sun ankara da dawowarta ba,don a yanzun kadaici kawai take bugata,batason hayaniya ko doguwar hira.
Kwance kawai tayi tana saqa da warwara,ba tabbatuwar aure a kanta ba,'ah....ambatar kalmar kadai tana sanyata fargaba da razani,wai ta yaya zata iya hada muhalli da wani d'a namiji kuma wai a kirata matarsa? iya wannan tunanin kadai juya mata kwanya yakeyi tare da gara sanyata a wata dimuwa da kuma damuwa.
Gab da magariba ta shiga wanka,ta fito ta shirya cikin wata lallausar riga me hade da wandonta,ta sanya hijab tayi sallar magariba,taci gaba da zama saman abun sallar,tana jin motsi da gilmawar nadeeya da fadeela,wani lokaci harda baaba ramatu.
Tasan ba lallai su san ta dawo ba,saboda duk wani qwan lantarki me haske ta kasheshi,sai dim light kawai.
Har nadeeya ta gota dakin ¡ilkinta ya bata kamar akwai mutum,saboda kana iya jin gamshin turaren sãahar me sanyi da baya buya yana ratsa qofar zuwa hallway din.
Komawa tayi da baya ta murda qofar,sai ta bude,ta sanya kai cikin mamaki bakinta dauke da sallama,sãahar dake shirin tayar da sallar isha'i ta dakata tana amsawa
"Antvn fadee,har yaushe kika dawo haka?,muna can muna jajenki,i called you several times amma ban sameki ba? mutuniyar tana can tana dakon dawowarkita kasa zaune ta kasa tsaye tun dazun‚bakinta da labari" dan lumshe ido tayi cikin murmushi
"Nafi awa da dawowa,na shigo ne banjin dadi shi yasa na kebe"
"Ya salam! me ya sameki?" Nadeeya tayi maganar sautin muryarta na nuna tsantsar kulawa damuwa da qauna
"It's not something serious,i felt relieved"
"Really?" Kai ta gyada tana murmushi,saboda ta hangi wani irin damuwa da kulawa da ita shigen na afifa
"Bazan gayawa faadee dinki ba,if not ta zama itace patient din,please zakiyi joining dinmu muyi dinner?" Kai tadan yada gefe
"Banajin yunwa,amma zanyi qoqari ko ban fito dinner ba,zamu hadu kafin animan"
"Is okay,Allah yasa kaffara ne'ta fadi cikin mutuwar jiki ta juya ta fice tana jawa sãahar qofar. Ajiyar Zuciya ta sauke me qarfi,tana mamakin yadda suka damu da ita da al'amuranta a lokaci guda haka.