← Book details Tabarmar Kashi Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 68 OF 171

Sashe 68

Tabarmar Kashi Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

"Ba abinda kika yimin fa amma kike cewa nayi haquri"

"A'ah,kince bakya sona,na dauka nayi miki wani abun" kai ta girgiza da sauri,saita shagwabe mata

"Abby ne ya tafi ya barni,bayan yace bazai sake tafiya ba dani ba" siraran hannuwan yarinyar ta kamo tana kallonsu,babu wata qiba sam,kamar bata cin wani abu da zai gina mata jiki,duk da daular da take ciki,saidai kyau da gogewar fata kawai

"Abbynki ba zaiyi qarya ba,lallai uzurin da sai yayi tafiyar ne kuma ba tare da ke ba ya kamashi,but na tabbatar bazai dade sosai ba" murmushi ya qwacewa fadeela

"Shima haka yacemin"

"So....you must trust him" kai fadeela ta jinjina tana murmushi

"Wait.....yanzun kinci abinci?" Kai ta girgiza fuskarta na sake narkewa,ido sãahar ta zaro

"Eehhhh,bakyason abby ya dawo yaga kin zama qatuwa?,baby fadeela ta zama 'yar lukuta?" Dariya fadeelan ta saki,yadda sãahar din ke bubba hannayenta tana mata sign na qiba

"Inaso auntie,inaso"

"Good,chubby fadeela"

"Yes anty,not slimy,a chubby,a daina tsokanata a school"

"Aha,oya gate up" tayi furucin tana miqa mata hannunta,sai tayi hanzarin dora nata hannun,cikin kulawa sãahar ta riqeta sosai ta sauko da ita tana karantar yadda walwala da farinciki ya maye gurbin bacin rai data dawo ta sameta a ciki,wani irin nau'in tausayinta ya sake saukar mata,saita ajjiyeta saman lallausan carfet din dake gaban gadonta,itama ta zauna akai,ta fara diban abincin tana bata a baki.

"Kin iya feeding mutum like my abby" murmushi sãahar tayi

"Really?" Kai ta gyada mata

"Okay,nayi alqawarin zaifi na Abby din naki gaba kadan. Wani dariya me cike da nishadi fadeelan ta saki, sãahar ta tsaya kawai tana kallonta,an gaya mata tana da wuyar sabo sosai,nannys dinta suna jimawa kafin ta fara sakin jikin dasu,duk da ba wani dogon zango sukeyi ba a gidan,amma sai gashi ita lokaci guda ta sake sosai da ita.

uhmmm,ga sabuwar nanny a sheqar da batasan ta waye ba, za'a dore kuwa?,to lokaci shi zai nuna mana,asha hutun weekend lafiya,fatan alkhairi a gareku gaba daya,masu comments ina gani na gode sosai,gurin amsa comment dinne baya dannuwa,but am really appreciating

*HUGUMA*

*_TABARMAR KASHI_*

Page 61

Tsaf ta gyara gurin bayan ta gama bata abincin,duk da akwai wadda ke da alhakin hakan amma bata jira ba,ta shiga toilet dinta ta wanke hannunta,ta zari towel din dake ajiye musamman saboda goge hannu tana gogewa
baaba ramatu ta shigo.
Tayi mamakin yawan abincin da taga taci
"Ke ai baki iya bayarwa ba,new nanny ta fiki iyawa" baki ta kama tana dariya "'yeee,zakici qaniyarki,yau nice ban iya bada abinci ba?,tun kina koyar yadda akecin abincin to ni nake baki don gidanku" dariya ta saki tana buga tsalle a gadon,abinda yasa sãahar murmushi kenan tana dan binta da kallo,abinda ta karanta,yarinyar nada sauqin kai,sanann irin mutanen nan ne masu son abinda zai nishadantar dasu,a yadda ta karanta gasa da minti arba'in a tarayyarsu,tana bugatar kulawa da zata dace da hankalinta.

A dakin ta barsu,ta dauki excuse don ta kintsa kanta da dakinta. Tana shiga ta zare mayafin jikinta ta ajjiye saman gado tana furzar da iska daga bakinta,yarinyar ta shiga ranta lokaci guda fiye da yadda tayi zaton zata kasance,wani abu takeji game da ita a ranta,tana jin kamar daga jininta ta fito.
Sai data gama shirya kayanta a wardrobe tsaf ta fidda komai ta ajjiyeshi a muhallinsa,bath stuff dinta ta kaisu bandaki,sannan ta zare kayan jikinta ta shiga bandaki tayi wanka. Koda ta fito cikin wata doguwar riga ta lallausar auduga ta shirya,ta
gabatar da sallah,zuwa lokacin dakin ya fara
kama qamshin turarukanta masu sanyin
qamshi.

Hijabinta ta zare ta tsaya bakin mudubi
tana taje gashinta,ta gama tana hadeshi akayi
knocking,ta qarasa a nutse ya yafa qaramin
hijab ta bude gofar.
Me dafa abincin sashence,itama sanye da
uniform dinta,saidai su nasu akwai banbancin
color dana sashen hajiya qarama dana sauran
ma'aikatan dake gidan,nasu din fari ne qal da
ratsin bagi

"Its time for dinner maa" ta fada cikin
rusunawa

"Alright,thank you" ta fada cikin sauqin kanta da ba kasafai yake bayyana tattare da ita ba.

Ciki ta koma ta fidda slippers din da aka bata cikin wata jaka,wanda qa'ida ne na dukka ma'aikacin da zai fara aiki cikin gidan,ta sanya a qafafunta,saita kashe wayarta ta jona a charge da nufin sanda zata dawo ya cika,sai tayi kiran dukkan wanda ya kamata,don batason suyi kiranta bayan bata nan,ta maida qaramin hijabin daya sauka har kusan qugunta sannan ta fito a dakin.
Kai tsaye dakin fadeela ta koma,ta sameta sunata rigima da baaba ramatu akan kayan da zata sanya, kowa da yake gidan ya saba da wannan agenda din nasu,sosai take maidata kamar kakarta. Cikin hikima da dabara ta fidda mata wasu kayan,da lallashi ta sakata ta sanyasu,bayan tayi mata alqawarin bata zabin kayan baccin duk da takeson sakawa,sannan suka fito cin abincin ita da fadeela da baaba ramatu.
A gasa sãahar ta sauko musu dasu,sabanin yadda suka saka ci a saman table. Sãahar ta buda abincin tana gare masa kallo. Abinci ne yankunan Europe da Asia,saita ajiye murfin warmer din tana duban fuskokinsu. Ba wani karsashi a fuskar baaba ramatu,amma fadeelan har zumudin a zuba mata takeyi. Damar zubawa ta bawa baaba ramatu,ita kuma ta zubawa fadeela,sannan ta zauna ta bata da kanta kamar wancan lokacin,sai data tabbatar ta qoshi sannan ta zauna sosai,kadan ta tsakura ta ture,don ba jituwa tsakaninta da abinci, especially ma abincin dare, tafi qaunar coffee fiye da komai a rayuwarta.
Suna daki tana shirya fadeelan wadda taketa gogarin bata labarin abby dinta, magana daya biyu saita sakoshi, murmushi kawai sãahar ke binta dashi,tunda batasan komai a kai ba,kawai dai tana ji a zuciyarta cewa yarinyar ta rabauta da uba daya san darajar diyarshi,yake bata dukkan kulawa,ya kuma damu da damuwarta. Ruwa me dumi sosai tayi mata wankan dashi,ta shiryata cikin wasu kayan bacci masu taushi dai dai da shekarunta,ta sake mata gashinta yadda zatafi in dadin kwanciya.

Har wani lumshe idanu fadeela keyi,tana jin dadi sosai a jikinta

"Aunty nanny kin iya wanka wallahi" dole dariyar da saahar batayi niyya ba ta qwace mata,ta rige siraran hannuwan fadeelan

"'Wankan ma akwai wanda yafi wani dadi?" Kai ta gyada

"Sosai,na abby da naki yafi dadi, amma shi abby sai ya daina yimin, waina girma,sai randa na fadi bani da lafiya shine yakemin" ta garasa maganar cikin karyewar murya dake nuna itama tasan halin ciwon da take ciki
"Aunty nanny,abby yace wai zan warke watarana hakane?" Qwalla ce ta cika idanuwan sãahar,saita jawo ta ta zaunar da ita saman cinyoyinta

"In sha Allah, kina addu'a?"
§ . 865 4C16
"' Ai ban iya ba" fuskarta ta dago ta shafa, komai nata siriri,saita saki murmushi
"Zan koya miki,zamu dinga sallah abby's chubby" magaleta tayi tana dariya saboda sunan ya mata dadi. Dai dai lokacin aka turo gofar dakin fadeelan.
Dukkansu suka daga kai suna duban me shigowar,mommy qarama ce,cikin wasu kayan bacci da suka zubu,tayi rolling da wani qaramin mayafi kalar kayan,ikinta sai fidda qasaitaccen qamshi yakeyi. Miqewa fadeela tayi ta isa gurinta,saita miga hannu ta ruqota suka qaraso cikin dakin
"Mummy amma abby bazai kori wannan nanny din ba ko?,ita ina sonta sosai" ta fadi tana dora kanta akan cinyar hajiya garama. Hannu ta dora saman kanta tana shafawa,idanunta akan fuskar säahar
Нд
"'Indai ta kiyaye doka da qa'idoji,sannan ta riqe alkinta ta kula dake yadda akace mata"
"Mommy tana kula dani sosai" tayi maganar da accent na quruciya a muryarta
"Okay,jiki wajen baaba ramatu kice ta baki kayan dana bata ajiya", fellawa tayi da gudu ta fice, saita tattaro hankalinta kan säahar.
Idanu tadan kafeta dashi,wasu lokutan takanji shakka da kokwanto akan yarinyar,tana da wani irin kwarjini da bata ganinsa saman fuskar kaf ma'ikatan gidan sai ita,sannan daga shigowarta zuwa yanzu ta fahimci kwata kwata bata rawar jikin da dukka maaikacin daya shigo gidan yakeyi,kamar zai kwanta a hanyarta tabi ta kansa,dazu data kira mrs sadeega ta gaya mata haka yanayin ta mrs sadeeqa ta gaya mata haka yanayinta yake,bata da son yawa surutu da kuma hayaniya,MISKILA CE.
Ад
miskilar data fadi shi yafi qara kwanta mata,saboda tasan muddin tana da wanna dabi'ar ba zata saba da kowa ba,ba kuma zata zauna tayi hira da kowa ba akan abinda ya shafi gidan ba,aikinta kawai zata yita yi babu waiwaye ba duban kowa.
Wata jaka ta ajjiye mata tana Kallonta
"Ya lafiyar fadeelan?”

"Alhamdulillah" ta amsa mata a taqaice tana kwashe cosmetics din yarinyar data bazasu a gasa

"Madallah,wadannan...
...sune magungunan
Chapter 68 · 0% Book details