← Book details Tabarmar Kashi Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 94 OF 171

Sashe 94

Tabarmar Kashi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Maji tace a wuce da ita sashenta ta huta,ita
'yar gida ce a gurinta basai an bata wahala ba,kuma ko yaushe zasu kasance tare" sagon da baaba ramatu ta matso ta shaidawa hajiya garama kenan qasa qasa. Kai ta jinjina,a gasan ranta zuciyarta tana bata tabbas akwai dalilin da yasa shifa ta aikata hakan,amma koma meye har yanzu sauran akaloli suna hannunta,kuma ita zata ci daga da yin nasar kamar yadda tayi a baya.

Tunda ta tsoma gafarta a sashen jikinta da hancinta ta TABBATAR mata wani guri ne daya banbanta da kowanne sashe na gidan,guri ne me tsari da koda idanunta suna a lullube amma hakan bai hanata ganin lallausan carfet dan gasar turkey da qafafunta ke nutsewa a ciki ba. Qamshin da wajen ke fiddawa kawai ya isa ya saukarwa da zuciya tare da ruhi salaama,uwa uba dukka hayaniyar gidan sam sam babu ita a nan,bisa alama ma sun baro mutanen dake dauke da hayaniyar a can baya,sai wani irin shuru da sautin muryoyin da basu wuce biyar zuwa shida ba dake magana da sauti mara hayaniya.

Bata gushe ba tana biye da hajiya qarama dake ci gaba da cusa Kai zuwa hallway din da dakunan baccin sashen suke a jere,wanda aka sake narka kudi aka masa mugun gyara na fitar hayyaci,duk kuwa sa cewa babu abinda ya sameshi, amma a yanzun an masa gyaran da zai dace da rayuwar maaurata.

Zuciyarta dake qirjinta takejin kamar ana hurawa wuta saboda ruwan kudin da taga toufeeq din ya barnatarwa gurin,bayan ta samu dukkan bayanai da huijoji masu qarfi daje bayyana mata cewa ba auren soyayya yayi ba,auren sadaukarwa ne ga diyarsa fadeela,a qalla tafi shekara goma batasha maganin hawan jininta ba,amma a yau batajin zata iya kwana ba tare da tasha din ba.

Wasi wasi yaso cika zuciyarta taf,tunda suke mata aiki tsahon shekarun basu taba kawo mata labarin da ba haka yake ba,amma a yau ta shiga tantama,yadda taga komai ya canza,tayi imanin muddin babu son ron taoufeeq bata zaton akwai wanda ya isa ya sakashi yiwa bangaren irin wanna tsarin da kowa zaiyi burin kasancewarsa a ciki.

Bata fahimci cewa babu kowa a tare da ita ba sai bayan shudewar mintuna goma da sumaira ta shigo tana gaya mata yaa Saifullahi ya bada dokar kada wanda ya zauna. Hannun sumaira ta riqe da kyau,qwalla na sauko mata.
A irin wannan gigitaccen yanayin da take ciki inama acw afifanta tana kusa da ita? itace qwarin gwiwarta,saidai kuma inaaa,zagin soyayya ya sanya dukkan wani qarfi nasa ya nesantata da afifan,tana can itama domin fuskantar sabuwar rayuwa, rayuwar da säahar ke mata fatan ta zama me tsananin zaqi,ba me daci ba kamar yadda ta fuskanci tata.

Bude gofar da taji alamun anyi a
karo na biyu ya sanyata kasa kunne. A nutse take takowa zuwa cikin dakin, idanunta akan rufaffiyar fuskar sãahar,zuciya nata yi mata saqe saqen abubuwan da zata iya aiwatarwa a kanta,saidai duk abinda zuciyar ke gaya mata tana ganin bai dace da ya faru a wannan muhallin ba,a kuma dai dai wannan lokacin ba.

*HUGUMA*

*_TABARMAR KASHI_*

Book 02 Page 12

Gyaran murya ta danyi,idanunta akan
sãahar tana sake takowa kusa da da ita,daga
gefan lallausar sofa bed ta zauna tana
dubanta da kyau
"Maraba da shigowa mahmud JARMA
family,na tayaki murna qwarai bisa samun
wannan nasara da kikayi,sannan kuma ina
miki alhinin cewa....nasararki zata kasance
ta gajeran zango ce,sakamakon toufeeq ba mallakinki bane,dukka tsahon rainon
da nayi masa,na raineshi ne don ya zama
mallakina,wato mallakin 'vata meenal haseena"
wani dan banzan haushi maganar hajiya
qarama ta saukar a zuciyarta,tayi qoqarin
tsaida hawayenta tana son fahimtar abinda
matar take fadi, idanunta na kallon tafukan
hannayenta ba tare data yaye rufin kanta ba

"Na jinjina miki yadda kika shirya komai ya
kuma tabbata lokaci kadan bayan tafiyata,to
amma ki sani,sauyawarki daga sunan nanny
boyi boyi zuwa ga matar auren toufeeq
babu abinda zai canza daga dokoki da
tsare tsaren gidan nan,fatan da nake miki
ki iya kiyayewa,sannan ki jirayi sakamakon
da zai biyo baya nan da kwanaki bakwai
masu zuwa,batun jikata fadeela,banason
ki fiya zaqewa cikin lamuranta saboda
shine samun lafiyarki,kiji kigi ji ki gani kigi
gani,na barki lafiya,asha amarci lafiya" tana
kaiwa nan ta mige,saidai taku uku kacal
tayi sãahar da zuciyarta ke a dugunzume
ta gaza daurewa kalaman hajiya qaramar,ta
tunzura qwarai,itama irinsa ce kenan? me tarin
Izza taqama da izgili,ashe ga inda ya debo dabi'arsa,lallai akwai wani boyayyen abu cikin taku da rayuwar matar cikin gidan,jikinta da zuciyarta sun gama aminta da hakan,adam ya yiwa rayuwa ruhi zuciya da gangar jikinta mugun horon da yasa nan da nan take iya fahimtar wani abu daga wasu mutane da dama.

"Inda kinsan abinda ke qasan zuciyata da baki bata bakinki kina wannan b'ab'atun ba.don haka na roqeki ki kama girmanki,zan nanata miki tun a daren farko na cikin gidan nan saboda daga ke har shi ba zamanku nazo yi ba" zallar madarar mamaki ya saukar mata.wani abu yayi mata tsawa a kanta,ta waiwayo tana son tabbatar da abinda kunnuwanta suke jiye mata,sai sukayi idanu hudu da saahar data dage hular kanta,wanda hakan ya bawa kyakkyawar fuskarta data sake wani sassanyan kyau saboda gyara data ci kamar babu gobe,da kuma haske da annurin
AMARCI dake sauka a fuska da jikin kowacce diya mace data amsa wannan sunan. Kamar ko yaushe yanzun ma kwarjini tayi mata,amma hakan bai hana hajiya qarama ritsata da ido ba,tana mamakin qarfin halin yarinyar.

Tabbas dole ta shiga cikin mutanen da take
targeting,ta yiwa kanta wannan alqawarin,sai ta gyada kanta ta juya ta fice a hankali daga dakin.

Qaramin tsaki säahar ta sauke bataii
zata zauna matar ta sanya mata wata
damuwa,ita sam bata cikin damuwarta bare
tace zata takura mata,ba ita ba,koda shi kansa
toufeeg din ba zata yarda ya zamar mata
damuwa ba bare wata ganwar mahaifi data
fuskanci zuciyarta akwai ayar tambaya.

Ta jima zaune a gurin tana saga da
warwarar yadda zata tafi da rayuwarta cikin
gidan,zata bawa kowa girma,amma sam ba zata dauki raini cin zarafi ko cin fuska ba. A
yadda taji gidan ya fara shuru ya tabbatar
mata dare ya fara yi,sai ta dubi agogon
dake jikin bangon dakin nata,fitsari takeji
sosai hakanan ta tabbatar wadan nan kayan
jikin nata ba zasu barta sakewa ba,don haka
ta miqe ta zare rigar saman,tanar doguwar
rigar wadda ta fidda shape dinta qwarai da
gaske,tun daga girji zuwa qugunta,ta tattareta ta nufi qofar da take tunani bandaki ce da zummar idan ta fito tasan yadda zatayi ta raba kanta da rigar itama yadda zatafi jin dadin kwanciya.

Ya kusa mintuna talatin zaune
cikin motar tasa bayan fitowarsa daga gurin maji,a yau addu'o'in da yasha a bakinta zai iya cewa bai taba jin makamantasu ba daga bakinta.farincikin da ya gani kwance a fuskarta ya taba zuciyarsa,duk yadda yake zaton ta dauki auren ya wuce nan,ta mashi wani babban matsayi da yayi imanin ba nan kusa ta ajiyeshi ba. Motar na a kunne ac naci gaba da aikinta,hakanan fitilun cikin motar. Sanye yake da wani baqin yadi da aka yiwa dinki tamkar na buzaven qasar nijer,dinkin ya zauna matuqa da gaske a jikinsa, kamar yadda baqin yadda ya kwantawa farar fatarsa ya sake fidda ainihin haske da kyanta tare da bayyana zallar hutu da in dadi hadi da kulawar da take samu,bagar sumarsa ta ainihin halfcast na nannade saman kansa tana bada wani sheqi me kyau da sassanyan gamshi kamar ko yaushe.
Waiwayawa yayi a nutse ya kalli tarin ledojin alfarma dake gefansa,wanda duka maji ce ta bashi tace ya shiga gurin iyalinsa dashi,don shi babu abinda ya riqo a hannunsa,duk da yanajin sanda abokansu ke hadawa sajjad,sunyi la'akari da cewa shi din tsohon aure ne,sunsan zai tanadi abinda ya kamata ba sai an gaya masa ba. Su kansu kayan qarin nauyi ne a wajensa,don ya tabbatar tilas ya sadasu da wadda aka siya saboda ita kodon cika kima da martabar maji.
Sashen nasa ya sake saukewa

idanunsa a karo na barkatai,sam baya gaunar shiga sai don babu yadda zaiyi,a duk sanda ya tuna cewa akwai wata mace a ciki me amsa sunan matarsa duk sai yaji kamar dai an takureshi ne kawai. A karo na gaba da qarfi yaja tsakin hadi da balle murfin motar a zafafe ya fito,jibril dake jingine jikin motar ya qaraso da sauri,kafin yace komai toufeeq din ya rigashi magantuwa

"Ka gayawa Jacob ya shigomin da kayan cikin falo, ka kashe motar na sallameka,sai kuma da safe"

"Sir,da safe kuma? na dauka zakaje hutu ko?, ko don madam" jibril din ya fada zuciya daya yana murmushi,saidai kallon da toufeeq din yayi masa ya tabbatar ya tafka baranbarama,sai yayi saurin jan bakinsa ya tsuke yana yunqurin bude daya side din ya fiddo kayan kamar yadda ya umarta.

Hannayensa zube a aljihun wandonsa yake qarewa falon kallo,ya sake jan qaramin tsaki, komai nashi sajjad ya canza masa,duk da kyawun da sassan ya qara ya kuma zuna favourite colours dinsa,to amma shikam bai shiryawa dukka wadan nan abubuwan ba. Da kansa ya gaji da tsaiwa,ya sunkuya ya kwashe kayan da jacob ya shigo masa da su,ya nufi hallway din da zai sadashi da dakunan baccinsu,ransa yana sake baci,komai a yanzun sai yayi sharing da wani,gurin mallakinsa ne a baya,shi daya yake shiga yayi rayuwarsa,idan zao shekara bai fito ba motsin kowa bazai dameshi ba,amma a yanxun bashi da wannan tabbacin.

Tsaye tayi a gaban madubi bayan fitowarta daga toilet din tana kallon fuskarta data fito sosai saboda qananun kitson da aka zauna aka yarfawa gashinta me santsi,abinda zata iva cewa tsahon rayuwarta ba zatace ga lokacin da irin hakan ta faru ba,hasalima kwata kwata kitsonta baya wuce manyan kalba guda hudu,saboda tsaho da santsin gashinta, amma a yanzun an samu wata gwana jarababbiyar iya kama gashi ta kitse mata kan tsaf,kuma hakan ba qaramin qarawa fuskarta kyau yayi ba,jelolin kitson gaba daya sun kwanta sosai a gadon bayanta har tsakiyar bayan nata. Hannu ta sanya tana qogarin zuge zip din rigarta wanda afifa ce dama ta zuge matan,da qyar hannun nata yakai,ta fara jan zip din ya fara saukowa,har yakai rabi taji an taba qofar,saita tsaya cak tana kallon madubi dake haska mata bakin gofa,tanason tantance qofar dakin nata aka taba ko kuma sauran qofofin dake wajen.
Chapter 94 · 0% Book details