← Book details Tabarmar Kashi Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 21 OF 171

Sashe 21

Tabarmar Kashi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Dogon tsaki taja,sannan ta juya tana fita a dakin bayan ta dauki wayarta,ta kuma goge duk wani miscall na mahmud da saqonsa da ya shigo bayan taqi daga wayar.

Still maama da afifa na zaune suna hira a parlor din,saita wuce saman dining tana duba abincin da baaba rabi ta ajjiye mata. Cikin wanda ta zuba din ta sake tsakurar wani,duk da bashi da yawa amma ba zai iya shiga cikinta duk ba,hakanan yanayinta yake,sanda tana qarama maaman tasha kaita asibiti,ayita bata multivitamin ko cikinta zai bude a samu cin abincinta ya qaru,saidai babu wani ci gaba,dole aka rabu da ita hakanan bayan sun fahimci halittarta ce a hakan.

Sanda ta kammala itama qasan ta sauko ta saka baki a hirar tasu,duk da kusan rabin hankalinta yana kan wayarta,ta shiga Instagram account dinta tana dubawa.

Har ta gota wani post saita dawo da baya a hankali. Hoto ne da aka yiwa cikakken daukan daya bala'in fita tarrrr,kana ganin hoton zakasan cewa da babbar waya akayi,irin wayoyin da sukasan haqqin fidda hoto da kyau.

_i'd never met anyone so quiet and beautiful simultaneously like him,his personality match his beautiful face MT JARMA_ Rubutun dake qasan photon kenan,sai tarin comments rututu,wanda kusan rabinsa na mata ne.

Wani bacin rai ne yazowa sãahar iya wuya,ta fita gaba daya daga Instagram din,wasu abubuwan ba shakka laifin mata ne,irin comment data dinga gani a qasan photon kwata kwata babu tsari babu kuma aji bare kamun kai irin na 'ya'ya mata,kamar a duniya shi daya Allah ya bawa baiwar kyau?,ba dole ya dinga buga wannan iskancin ba, muddin a zahirance irin wannan rawan kan da digimin matan suke masa,ranta ya baci sosai,har afifa ta kula ta tambayeta,amma sai tace ba komai,ta jawo saman wayar ta kashe data dinta gaba daya,dai dai sanda yaa zaid yayi sallama cikin falon,yana riqe da jakar abba,abban yana biye dashi a baya.

Cikin girmamawa kowa ke qoqarin masa sannu da zuwa,mutum me cikar kamala da kuma nuna qauna da sakewa da iyalinsa,yana da faran faran sakin fuska da kuma barkwanci,amma muddin zakayi ba dai dai ba da gangan da ganganci to fa baya lamunta,a nan ne zaka ga aihin Color dinsa.

Sassansa ya wuce daga nan ta qofar data hada sassan biyu,maama tabi bayansa ta barsu da zaid din yana tambayar sãahar ya aikin

"Lafiya" ta amsa masa a taqaice shima,afifa dake zaune daga gefanta dariyar da taketa dannewa ta taso mata

"Adai dinga jin tsoron Allah ana fadin gaskiya,atoh" waiwayawa tayi ta kalli afifan,kaman zatayi magana saita fasa ta maida idanunta ga wayarta

"Tell me,me ya faru?,da alama akwai magana tunda permanent assistant dinki ke dariya" shuru ta danyi kamar ba zatayi magana ba,sai kuma ta buda baki sound na bacin rai yana dan fita kadan a muryarta

"Bashi da kirki yaa zaid,he was trying to insult me as kamar ina neman wani abu da kamfaninsu" dan zuba mata ido zaid yayi sannan ya saki murmushi

"Try to relieve your anger dear,ki nutsu ki fuskanceshi,ki kuma fuskanci aikinki,ba don shi kadai kike zaune a kamfanin ba right?" Kai ta gyada

"So no need ki damu kanki,do all the right things,amma don't be rude to him,ya girmeki,show some respect zaki samawa yaa muhyi din mutunci,ki zama me kawaici yadda na sanki,kada ki bari qananun abubuwa su dinga bata ranki,kin fahimta?" Nutsuwa taji tana saukar mata,Allah ya sani yadda yayyenta suke nuna qauna da kulawa a gareta ya sanya itama take qaunarsu,take kuma qoqarin bin dukka umarninsu,yanzun maganar da sukayi da yaa zaid din ya samar mata da relief sosai,sai ta dan sake sukaci gaba da hira,har zuwa sanda akayi kiran magrib,ya fita masallaci shida abba,su kuma suka wuce ciki ita da afifa.

Ba kasafai take tashi daga saman abun salla da wuri ba duk bayan sallar magarib har sai tayi isha'i,kamar yadda takeyi bayan asuba har alfijir ya keto,saboda gurabene na amsar addu'a sosai.

FURAR DANKO
Billyn Abdul

-ZAFIN KAI
Mamuhgee

-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma

-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo

Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400

Pay at👇

1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim
Sai katura shedar biyanka anan👇

09032345899

Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070

VIP🔥💯
Zafin kai 3k
Furar danko 3k
Tabarmar kashi 3k
Bakon munafuki 3k

*Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din*

+22799643131

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*

*THANKS FOR CHOOSING US*🥰

Zafafa🫶🔥
..

[8/14, 1:31 PM] KYAUTA: *H U G U M A*

*_TABARMAR ƘASHI_*💔
https://arewabooks.com/u/huguma

Page 19
_____________________________
*_TAHO KI GANI_*👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽

_shin kinsan da zaman wannan kuwa?,ko kina can kina bulayin neman inda zaki samu ingantattun kayan mata da SUPPLEMENT masu inganci cikin musulmin farashi?_

*Turqashi,ga biyan buqata ga sauqi*!

*ZAHRA DANGE* 👉🏽 _face behind LADY APHRODISIAC AND MORE_

*dealer in all kind of supplement and herbal aphrodisiacs kayan mata*
*Kayan mu will make you last on bed and permanently end the pain and embarrassment of weak eraction and premature ejaculation*

*Muna hadin bridal package*
*postnatal combination of natural herb's and supplement*

*Akwai hadin uwar gida mai da tsuhuwa yarinya*

*Akwai hadi na infection (sanyi herbs)*

*Akwai Zuma Mai saukar DA niima nan take tare da dandano Na mussaman*

*Muna kalolin gumbar Kamar gumbar madara, gumbar Aya, gumbar ridi, gumbar kasko, yar kicihi, Alhaji ba nan kake ba d.s*

*Akwai kalolin tsimi kamar Dan la'asar, tabaje, tsimin yar gata d.s*

*Muna DA kalolin gari nasha kamar sa buzu kuwa, sinadarin aya, abin sirri ne, emergency, rakumi DA akala, runbun dadi, kinfi Amarya d.s.*

*Muna special kaza, danbu,ciccibi, Yan shila,zuciya d.s*

*Akwai Na matsi different types DA sabulu na tsalki.*

*TA BANGAREN SUPPLEMENT*

*muna da na gyaran skin da kuma herbal aphrodisiacs supplement*

*Akwaisu Juliet eve, royal jelly, ultimate maca, suprodine, frozen detox, frozen collegen, majakani,amirna, khusus, dara,cantik ayu, pesona d.s*

*We have capsules, pills, chocolate, and different coffee that will make you sweet, firm, tight, young, beautiful and healthy.*

*Akwai different oils both siyan d'aya ko sari*

*Muna nan a garin SOKOTO sannan muna tura kaya ko ina a fadin duniya yaje maka cikin aminci IN SHA ALLAH*🌐

*_ZAKU IYA TUNTUBARTA KAI TSAYE TA WANNAN NUMBER WAYAR_*

07034400732

*_SIYAN NA GARI MAI DA KUDI GIDA_*👌🏽👌🏽👌🏽

*Tasted and trusted*💪🏽💪🏽💪🏽
_______________________________

Afifa na kwance rub da ciki a saman gadonsu,tana kallo ta system din sãahar din,furera mataimakiyar baaba rabi ce tayi knocking,afifa dake kallo tayi mata izini,ta turo qofar dakin a shigo,cikin girmamawa tace

"Maama tace a gayawa ummee,alhaji yana nemanta a sassansa" sãahar da takai ayar qarshe cikin surar da take karantawa ta maida qur'anin ta rufe

"Gani nan zuwa" ta amsawa furera,ta miqe zata fice,afifa ta nuna mata plates din da sukasha kankana tace ta wuce kitchen dashi.

Qur'anin ta mayar gurinsa,ta nade abun sallar sannan ta zura wasu slippers masu taushi a qafafunta tana mamakin kiran abban a irin wannan lokacin. Ko hijabin jikinta bata cire ba ta juya ta fice,afifa ta bita da kallo tana dariya qasa qasa,yau akwai daru kenan,sai ta gyara kwanciyarta sosai tana jiran dawowar rigimammiyar tata.

A nutse tayi sallama abban ya bata umarnin qarasowa,ta zare slipper dinta ta shigo,ta zauna daga qasa gefe guda. Dubanta yayi ba tare da ya ajjiye wayarsa dake hannunsa ba

"Ummin abba,ki duba setting room,kina da baqo". Jin maganar tayi kamar anyi jifa da abu ne nauyi cikin zuzzurfan rami,ya fada kansa tsaye ne ba tare da wata damuwa ko ganin nauyin maganar a tattare dashi,saita shiga ko kwanto,kodai bataji da kyau bane

"Na'am abba?,afifa dai ko?" A natse ya dago ya kalleta sosai wannan karon cikin idanunta

"Khadijatou nace" jikinta ne ya sanyaya gaba daya da yadda abban ya kira ainihin sunanta,wanda ta manta rabon daya kirata hakan,dukka gabobinta kamar an bi an doddokesu haka taji,ta tattara dukka qwarin gwiwarta,ta samu ta yunqura ta miqe,tana jin kamar iska na yawo da ita daga hagunta zuwa dama,daga gaba zuwa baya. Har takai qofa muryar abban ta sake cimmata

"Idan kinje ki dawo zamuyi magana dake" kai ta gyada masa kamar me ciwon baki,ta zura takalminta da a yanzu takejin kamar qafafunta ba zasu iya riqesu ba ta fice.

Minti daya ma ya isa ya kaita setting room din gidan,wanda babban qayataccen parlor ne dake farfajiyar gidansu,wanda a nan abban ke ganawa da baqinsa,to amma a yadda jikinta ya zama wani matacce,sai data debi mintuna biyu harda doriya sannan ta qarasa,zuciyarta cike fal da mamaki da kuma tunanin waye wannan?,me kuma yazoyi mata?.

Muryar ya zaid ta fara ji sanda take dage labulen parlor din,suka hada ido dashi,yana zaune hannun kujera suna hira da baqon dake saye cikin wata dakakkiyar shadda,qamshin turarensa ya cika falon,a sake sosai suke hira da ya zaid kamar sun dade da sanin juna,suna hada ido ya miqe

"Gata nan ma ta iso,sai nace ka gaida gida" ya furta yana miqa masa hannunsa sukayi musabaha,sannan ya zagayeta ya fice daga parlor din.

Shuru parlor din ya dauka,yayin da taci gaba da tsaiwa a wajen kamar an dasata,bata fita ba bata kuma qarasa shigowa ba bare ta samu muhallin zama. Hakan ya baiwa mahmud abba gana damar kallonta da kyau,duk da cewa cikin hijab take amma sassanyan kyawun nan nata bai gaza fitowa fili ba muraran,wata qaunarta ta qara linkuwa cikin ransa,batayi laifi ba idan tayi jan aji me yawa,ta cancanta,tako ina ta cancanci dukkan wata izza da ginshira,saidai inda dubban matan dake binsa zasuya wahalar da yakesha akanta,tabbas da sun dara,da kuma yasha kunya

"Me kake buqata?,me kake nema a gurina?" Ta tambayeshi kanta tsaye,don ta gundira da kallon da yake mata,kamar yadda taji ta tsani zaman falon.

Murmushi ya saki sannan ya miqe tsaye yana mata nuni da kujera

"Inaga zaifi kyau ki samu guri ki zauna,karki gaji da tsaiwar" ya fada yana murmushi,har cikin ransa yana jin dadin ganinta da wanzuwarsu guri guda

"Kada ka damu da tsaiwata ko zamana,kai tsaye ka fadamin abinda kake ya kawoka, inason komawa ciki,nabar ayyuka da yawa " murmushi ya saki yana goye hannayensa a qijinsa

"Ayyah,sorry,ina fatan ba aikin office ne ya gajiyarmin dake ba" idanunta tadan lumshe sannan ta budesu,ta gundura matuqa,da zai taimaketa daya taqaita komai da komai ya sallameta ta wuce ciki abinta
Chapter 21 · 0% Book details