← Book details Tabarmar Kashi Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 80 OF 171

Sashe 80

Tabarmar Kashi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Idan kin isa ki kusanceta da taqi daya tak!,kiga yadda sunanki zai sauya" ya fada cikin tsawa da matsanancin fada

"Bazan kusanceta a zahiri ba,amma zan kusanceta ta hanyar da duniya zata sake shaidawa diyata ce halak malak'

"Go ahead. karki fasa,zan nuna miki other side dina da baki taba gani ba,stupid idiot" ya fadi yana wurgar da wayaryasa hannunsa ya shafi sumar kansa da qarfi hadi da yarfar da hannunsa.

"Ka dinga yawan ambaton Allah duk sanda zuciyarka ta zafafa" daya daga cikin maganganun maji suka fado masa a ransa,sai ya koma da baya da baya ya zauna gefan sofa din,qafafunsa a qasa,ya lumshe idanunsa yana kiran

"Hasbunallahu wani'imal wakil,wala'udwana illa alazzalimin,ya hayyu ya qayyumu birahmatika astagis, aslih li sha'any kullah,fala takilni ila nafsy darfata ainin" a hankali sai numfashinsa dava fara canzawa sakamakon tuna wace ameesha da tabon da ta barwa rayuwarsa ya fara daidaita.

Duban sãahar data shirya tea din nadeeya tayi

"Don Allah anty N,taimakeni,magana mukeyi me muhimmanci da maji banason ta katse,ki migawa yaa moha din,yana ta baya idan kuma ta falonsa zaki shiga ki tambaya guards zasu saita miki" duban nadeeyan tayi,sai taji ta kasa musanta mata. Ba sau daya ba ba sau biyu ba,a kwanaki goman da yayi da dawowa tana nemanta alfarma taje su gaisa,har ta gaji ta daina,batason taji wani abu a ranta kota dauka wani abune na daban,don haka ta gyada kanta tana gyara yafen dan mayafin pakistani dress din dake kanta,wanda ya lullube asirin sumarta me tsaho cika santsi da kuma laushi,ta juya a hankali tana fita a kitchen din

"Maji tace tanaso yau ku gaisa, wana biyu bataga fuskar diyarta ba,kamar ma tace akwai maganar da zakuyi,zan rige wayar harki dawo"

"Alright" ta fada tana murmushi,haka nan itama Allah ya sanya mata gaunar matar kamar yadda take gaunarta,tana burgeta,tana da wata irin kamala da dattako sosal.

Haka nan takejin gafafunta babu nauyi sanda ta nufi gofar bayan da zata sadata da farfajiyar da yake din, taci gaba da takawa a nutsen,sassanyar iskar dake gurin tana kada turaren iikinta zuwa kowanne sashe na wajen.

Kafin ta garaso ta hangi mutum zaune saman bagar sofa din da aka yiwa farar shimfida,saidai bata iya ganinsa fuskarsa saboda yayi qasa da kansa. Tana sake kusanto gurin tana kasa sarrafa idanunta daga dauke dubanta daqa kansa,cikin jikinta takejin kamar tana dosar wani mutum ne data taba saninsa ko ganinsa,a haka har ya rage saura taqi kadan ta cimmasa,ta bude bakinta da taji ya soma rawa da nufin yin sallama,dai dai lokacin da ya daga fararen manyan idanunsa da suka rune zuwa kalar jaaa.

*HUGUMA*

* TABARMAR KASHI_*

Page 71

Guri guda idanunsu suka hade,wani abu me matugar garfi ya fusgeta,ya kuma ratsata tun daga tsakiyar kanta har zuwa tafin qafafunta,a hankali tray din dake hannunta ya sulale yayi d'ai d'ai a gasa,bata bawa kanta wani option ba da ya wuce juyawa cikin hanzari da sassarfa tana barin gurin.

Ko motsawa baiyi ba daga inda yake zaunen,tamkar an dasa shi a wajen ya bita da kallo harta qule ta bacewa ganinsa. Kaf tunaninsa ya katse ya kuma tsinke,babu abinda ke kai kawo a fuska da kuma zuciyarsa sai fuskarta,his ex president......me takeyi a gidan? wayo ya kawota cikin gidan?. A hankali ya sauke dubansa kan farantin da yayi d'ai d'ai a gurin,komai ya kama gabansa,tunanin da ya darsu a ransa ya sanyashi zaro wayarsa ya sake kiran number nadeeya,bugu daya ta dauka

"Waye kika aiko ya kawomin coffee?"

"Am sorry yaaya,muna magana ne da maii nannyn fadeela ne"

"Nanny?" Ya tambayeta da wani irin murya

"Eh yaa,am sorry ya mohai didn't intend to offend you" bai tsaya ce mata komai ba ya kashe wayar kawai

"What if itama ta shigo rayuwar su ne ta cutar masa da fadeela?" Shine kawai abinda ya samu zuciyarsa na jaddada masa,dukkan alamu sun nuna she's not in need bare yace hakan va sanyata aikatau,bata fito daga gidan da suke da qaramin qarfi ba bare yace a buqace take,ko kuma ta cancanci tayi aiki a wani guri, qaramin aiki ma irin wannan, she's well educated,tana da qualifications din da zata iya samun aiki ako ina Nigeria da waienta,amma sai ta zauna yin aikin nanny?no...ko daya zuciyarsa bata kwanta masa da hakan ba,kai tsaye ya tashi a wajen,ya bulla ta falonsa ya shiga ya dauki wayarsa ya fara neman layin mommy qarama.

Da gyar ta isa dakinta saboda wani irin bugawa da zuciyarta keyi,kamar zata balle qirjinta ta fito ko kuma ta amayota ta baki.

Gefan gado ta samu ta zauna tana maida numfashi,idanunta dukka a rufe,tana ganin shacin inuwarsa ta cikin duhun rufaffun idanunta

"Yaa moha,shine toufeeq? daddyn fadeela? ‚yayan nadeeya?" Ta yiwa kanta da kanta tambayar,wanda motsin fadeela da sunan kiranta da takeyi tun kafin ta shigo dakin ya sanyata bude idanuwan nata,sai ta mige da hanzari ta fada toilet ta maida gofar ta rufe.

Tsaye tayi a jikin gofar tana jin sautin siriryar muryar yarinyar tana kiranta,sai zuciyarta ta gaza jurewa da shurun da tayi mata

"Anty N idan kin fito maji na jiranki" saita sake mata gyaran muryar alamar ta amsa

'i love you anty" ta fada tana dariya ta fice.
Hawaye masu zafi ne taji sun taru mata a ido,yarinyar ta saba gaya mata wanann kalmar duk sanda ta danyi wasu awanni bata ganta ba,a yanzun data gaya matan sai takeiin kamar furucin da zai shiga tsakaninta da ita kenan na qarshe ita fadeelan ......koda wasa batajin zata iya lamuntar zama gida daya da MT jarma,mutumin da ya wulaqantata,ya tozartata,yaci mutuncinta,mutumin da baisan darajar dan adam ba,sai taji tana jajantawa fadeela,yarinyar batayi sa'ar uba ba sam,ta fito daga tsatson da bai dace da halayyar yarinyar ba.

Wani kuzari ne yazo mata da ya sanyata bude gofar dakin ta fito,ta nufi qofar dakin ta murza mata key sannan ta dawo da sauri ta jawo luggage dinta ta fara zuba kayanta a ciki.

Cikin mintuna galilan ta gama hada dukka kayanta waje guda,dama ba wasu kaya masu yawa take bari cikin gidan ba,tunda kowanne sati tana zuwa gida ta maida wasu ta dauko wasu,ta zari Vail dinta dake saman couch ta nannade kanta zuwa wuyanta,ta jawo luggage din ta bude qofar dakin fa fito.

Tana sako gofarta a hallway din suka bangaji juna ita da nadeeya wadda ga biyota da iPad din ta bata maji din kamar yadda maji ta bugata. Da sauri nadeeya taja baya tana kallonta mamaki kadan na nunawa saman fuskarta

"Ina zuwa haka da akwati da yammar nan?"
Sosai tayi gogarin dadaita muryarta

"Gida zan koma nadeeya" razani ne ya nuna
sosai a fuskarta,sai lokacin ta samu damar
qarewa birkitaccen yanayin sãahar din kallo

"'Gida kamar vaaya anty N,me ya faru?"
Hannun nadeeya ta laluba ta sanya mata key din dakin a hannunta

"Kuyi haquri,bazan iya ci gaba da zama tare daku ba"

"Me kike cewa säahar? don Allah me

mukayi miki? …baaba ramatu!" Nadeeya ta
gwalawa baaba kira a rude ganin sãahar ta
ja luggage dinta tana barin hallway din zuwa
falonsu,wanda daga shi sai babban falonsu sai
fita daga sashen gaba daya.

Kiran baaba ramatu din da tayi yaja
hankalin fadeela ta fito daga dakin nadeeya
din

"Baaba,wai anty nanny ce kawai ta hada
kayanta wai gida zata koma"
"Subhanallahi,me ya faru?,me akayi mata?"

"Wallahi ban sani ba baaba" nadeeya ta bata
amsa ita da fadeelan suna rige rigen cimmata.
A falon garshe suka tareta har baaba
ramatun

"Haba Khadija,me ya faru haka rana tsaka zaki
ce gida zaki koma"

"'Ba komai baaba,na ajiye aikin ne" teddy din hannunta fadeela ta yar,ta kama hannun sãahar ta rige tsam

"Don Allah anty karki taft,idan kuma zaki tafin bari na dauko kayana mu tafi tare" zuciyarta ta sosu da yadda taga yarinyar ta rude lokaci daya,sai ta tsugunna a gabanta tana riqe da hannayenta

"Tafiya ta zama dole faddee na,kiyi haquri kinji,babu komai, sister nadeeya tana tare da ke,zata kula da ke,hakama baaba ramatu" saita zame hannun zata miqe,amma fadeelan taqi sakinta,ta fara hawaye tana cewa

"Allah ni bazan zauna bake zanbi"

"Am sorry my faddee" ta fada tana shafa sumarta da ta gama gyara mata ita dazu da azahar,tayi mata ado da wasu pink din ribbons.

Zame hannunta tayi ta soma nufar waje,tana qwararawa kanta gwiwa daga raunin da zuciyarta ke shirin yi,batason ta karaya har taji ba zata iya tafiya ta barsu ba,tanason ta tsira da mutuncinta,wanda ta tabbatar idan tana gidan a qarqashinsa babu inda mutuncinta zaije,tunda har ya nemi take mata kima da martabar ta a muhallin da ba nashi ba....yaya kenan zai faru a yanzun da zata zamanto qarqashin ci da sha da inuwar gidansa?.

Iska me zafi ya furzar daga bakinsa sanda ya gama jin komai daga bakin hajiya garama,zuciyarsa bata nutsu ba,yafi gasgata akwai manufa cikin shigowarta rayuwarsu,don haka zuciyarsa tafi aminta da sallamarta daga gidan,koda ko wanne irin kulawa take bawa fadeelan.

A hankali kunnuwansa suka fara jiyo masa sautin kukan fadeelan,ya mige a nutse yana riqe da wayarsa a aljihunsa,ya kuma tunkari barandarsa ta inda yake iya ganin komai dake faruwa a farfajiyar gidan.

Itace a gaba janye da luggage dinta,fadeela na biye da ita,nadeeya da baaba ramatu kuma suna biye da su cikin hanzari da alama suna nufin dakatar da ita ne,sauran maaikatan gidan kuma sunyi carko carko cikin damuwa,kowa ya kasa aikata komai,saboda basusan maqasudin abinda ke faruwa ba.

Ransa ya sosu da ganin yadda fadeelan ke binta gudu gudu sauri sauri,amma ko sau daya bata tsaya ba bare ta waiwayo ta dubi kukan da takeyi ba
"Fadeela!" Ya kirata a tsawace,abinda bai taba yi ba tsahon rayuwarsu shi da ita.

Dukkansu suka tsaya cak,har saahar din da kiran nasa yayi wata irin tsawa a tsakiyar kanta,ta kuma runtse ido tana fatan Allah ya sanya ba dukan fadeelan zaiyi ba.

A zafafe yake takowa har ya iso gurin

"Tashi ki wuce ciki!" Ya fadi da muguwar tsawar da ta sanya nadeeya ja baya da sauri ta koma bayan baaba ramatu ta boye,saboda a yau din gaba daya a birkice take ganin yaa moha din.

"Abby tafiya zatayi ta barmu,me mukayi mata,don Allah ka bata haquri"
Chapter 80 · 0% Book details