Sashe 55
Tabarmar Kashi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wayar tana ringing adam dake bakin qofa yana dannota iya qarfinsa tare da qoqarin bankadeta ya bude qofar,ta runtse ido tana sakin kuka,bakinta fal addu'ar kada Allah ya bashi ikon cimmata har sai ummin ta dauka,muddin bata dauka da wuri ba tasan cewa kashinta ya bushe,a yadda ta zubar da jinin nan,babu wani cikakken qarfi yanzu haka a jikinta da zata iya ci gaba da tare qofar.
Ringing din ya tsaya,muryar ummin ta bayyana radau tare da yin sallama
"Zasu kasheni,zai kasheni" abinda ta fada kenan cikin qaraji,saboda nasarar bankado qofar da adam din ya samuyi,dalilin da ya sanyata faduwa gefe qasa warwas,taku biyu ya isa gabanta,yasa hannunsa ya damqe bakinta da kyau,ta inda babu damar da zatayi magana,ya zubamata ido da wani irin kallo na zallar rashin imani yana duban fuskarta tare da ja mata zazzafan gargadi da idanun nasa,sannan ya miqa hannu ya dauki wayar da har zuwa lokacin ummi ke fama cewa hello hello jin shuru ba'a sake magana ba.
Kiran ya kashe sannan ya sakar mata baki,ya koma saman toilet ya zauna yana maida numfashi,ransa a matuqar bace
"Kin ginawa kanki da kanki rami,zakisan cewa bani da imani" yana fadin hakan ya kamata,saidai taqi miqewa tsaye sam,bai damu ba ya riqe hannunta da kyau ya fara janta a qasa kamar kayan wanki,bai ajjiyeta ko a ina ba sai a gaban likitan
"Kayi mata allurar bacci,ka hada mata data 'yan shaye shaye me qarfin" tana ji tana gani ya danneta aka hada ruguntsumin alluran aka dirka mata,a hankali jikinta ya fara saki,saidai idanuwanta basu daina zubar da ruwan hawaye ba,hakanan bakinta bai fasa fadin
"Allah ya isa,Allah ya sakamin,Allah ka yimin sakayya".
Bai ko dubeta ba ya jawo stool gabanta ya zauna,yayi kiran ummi. Bugu daya ta daga a matuqar rikice
"Me yake faruwa da sãahar din?"
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un,muna cikin mummunan tashin hankali" ya fada da muryar kuka wadda a wajen ya qirqireta
"Me ya faru?"
"Ibtila'i ne ya samemu,na fita lafiya na dawo na tarar da ita cikin wani yanayi,ina shigowa kawai ta cakumeni ta fara fadin mugu azzalumi,ka cuceni zaka kasheni,Allah ya isa,Allah ya sakamin,ina tsammanin mummunan gamo tayi,don cewa tayi waita ganni da wata muna aikata alfasha,bayan kuma ni dawowata kenan daga tafiya,kwanana uku bana garin,yanzun haka gata ta sume,da qyar na samo kanta,duk tayi fashe fashe a dakinta" salati ummi ta saki tana sallalami cikin matuqar tashin hankali
"Yanzun tana ina?"
"Gamu a gida,amma na yiwa wani malami waya yana kan hanyar zuwa"
"Ganinan nima" ta fada a gaggauce tana kashe kiran.
Iska ya furzar daga bakinsa,sannan cikin hanzari ya fara kiran wata number wayar daban. Bugu uku aka daga,sai ya miqe yana fita a dakin,yana amsa wayar a gaggauce.
Sake lumshewa idanunta sukayi hade da wani zazzafan hawaye,zuwa lokacin sama sama takejin komai,hakanan dishi dishi take ganin abubuwa,amma duk da haka kwanyarta bata daina aiki ba,bata kuma daina haska mata girman cin amanar da adam yake Shirin aikata mata ba,wadda tafi abinda ya aikata mata a baya girma da muni. Kafin ya dawo bacci tuni yaci qarfinta.
Sanda ta farka ta ganta ne kawai kaca kaca cikin shirgi da shara,tana yashe a qasa cikin dattin,gaba daya dakin ya kacame,hatta da mirror da wanda ke jikin sif din a farfashe yake,duk wani kayan ado da qawa dake dakin wanda hannu zai iya kaiwa gareshi a fashe yake.
Cikin mamaki ta miqe ta zauna tana jin kallon ko ina,ita daya ce qwallin qwal a ciki,saita zabura ta miqe ta sauri ta nufi bakin qofa,tana fatan ta samu qofar a bude.
Tana isa bakin qofar muryar ummi ta fara jiyowa,wannan ya sanya da azama ta dora hannunta kan handle din ta fara jijjigashi tana fadin
"Ki taimakeni..... kasheni yakeson yi,ki budemin,ki tafi dani don Allah" ta furta iyakar budewar muryarta,wadda bata da wani amo sam sam kasancewarta mai sanyin murya tun asali.
Adam dake zaune qasan kujera wurjajan ya daga jajajyen idanunsa da sukayi jajur ya kalli qofar,kamar yadda idanun ummi dake sharce hawaye itama suke duban qofar
"To hajiya kinji irin takeyi,kuma duk sharrinsu ne" cewar wanda ke zaune daura da adam din,cikin babbar rugar malum malum harda rawani,da kuma tsayayyen gemun da wala'alla ciko ne akayi masa yayi irin wannan cikar,hannunsa kuma zabgegiyar tasbaha ce yake ta janta daya nabin daya
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un,wannan wacce irin jarabawa ce ta saukarmiki sãahar da qananun da ko ashirin basu haura ba?" Ta fada cikin kuka
"Hajiya kar ayi sabo,shi lamarin ubangiji haka yake,jarrabawa kuma babu ta inda bata saukarwa bawa" malamin qaryar ya fada yana shafa gemunsa cikin nuna zallar taqawar da babu ita ko kusa ko alama cikin zuciyarsa
"Yanzu ba yadda za'a yi na ganta?" Da sauri ya girgiza kai
"Ai hajiya muddin aka rabata da wannan dakin ba abinda bazai iya faruwa ba,zasu iya dauketa ma a nemeta a rasata,shi kansa likitan da kikaga ya fita yanzu saida Allah yasa bacci ya dauketa ya iyayi mata gwaje gwajen da yayi,shima kuma yaga alamun tabuwar kwanya kadan,duk da hakan na iya yiwuwa duk cikin sharrinsu ne".
A yadda suka tsara komai abune mawuyaci ka fahimci cewa shiri ne irin na adam da muqarrabansa,cikin kwana daya tal ya maidata mahaukaciyar qarfi da yaji,kusan kullum a nan ummi ke yini,gudun tonuwar asirinsa yasa aka dinga yawaita yi mata allurar bacci da aka cakudata da allurar sanya maye,abinda ya qara nakasta garkuwar jikinta,ya zamana ko cikakken zama bata iyayi,data zauna din sai bacci,kota dinga bin kowa da kallo kamar sokuwa,sukayi amfani da wannan damar sukace maganin da malamin yakeyi mata ne ya fara aiki a jikinta.
Fadin irin tashin hankalin da iyalan Dr mamman jarma suka shiga a qasar saudiyya sakamakon mummunan labarin tabuwar qwaqwalwar sãahar da suka samu bata baki ne,kada ma afifa taji labari,wadda a jikinta ta dinga jin cewa ba haka bane,hauka yana da sila da kuma sanadi idan ma har haukanne,koda ta sanadiyyar jinnu ne suna nuna wasu alamomi kafin sukai ga taba lafiya kwanyar mutum,tunda suke da sãahar basu taba ganin wani abu na daban tattare da ita ba da yake da alaqa da irin wannan lalurar.
Mutane ne masu tsananun dattako da yarda da Allah wahidun ahadun,sun yi imani suna qofar waraka,qofar karbar dukkan addu'ar me neman,wajen biyan buqatar duk wani mabaraci,dukkaninsu sai suka duqufa da addu'a ta nema mata sassauci da waraka,tana da gata me yawa da soyayyar iyaye da yayye,hakanan qananun yaran da suka kasance 'ya'yan 'yan uwanta suna tsananin sonta,saboda ita din mutum ce me son yara qwarai,akwai soyayya da sabo sosai a tsakaninsu.
Kwanakin da suke gabansu na ranar dawowa Nigeria sai suka zame musu kwanaki mafiya tsaho,duk da haka basu bari sunyi asarar kwanakin ba,sunci gaba da addu'a da ibada,tare da samin information na halin da ake ciki a wajen ummi.
**************Ta fuskanci duk wani abu da zatayi babu abinda zai hana adam aiwatar da abinda ya shirya mata,hakanan a yadda ya tsara din ta tabbata cikakkiyar mahaukaci ga idon kowa,tana jin muryoyin 'yan uwa makusanta daga parlor din gidan masu zuwa dubiya gurin ummi,saidai ta zame ta kwanta lamo tana jinsu,don zuwa lokacin tayi kukan da batasan iya adadinsa ba,bai kuma qara mata komai ba hakanan bai rage ba,don ba abinda adam ya fasa,saidai yana gaya mata a kullum,zabin fitarta daga wannan yanayin ko tabbatuwarta a ciki yana hannunta,ta sallameshi shima a ranar zai sallameta kowa ya kama gabansa.
Kwata kwata daina tanka masa tayi,saidai ya qaraci maganarsa ya tashi ya miqe ya fice,abinda yake sake dugunzuma ransa kenan tare da qara masa bacin rai a kanta
"Banda ina tsoron na qarasa gawar daba tawa ba,tabbas da sai nayi miki dukan da zaki raina kanki,amma ko a hakan ma muje zuwa wai mahaukaci ya hau kura" ya miqe yayi fatali da gantalelallen abincin da ya kawo mata,ya samu kyakkyawan mazauni akan qafafunta,zafin abincin ya ratsata,amma bata iya janye qafafun nata ba saboda wani azabtaccen ciwon kai da take fama dashi,ko gani bata iyayi sosai. Da zugin ya isheta saita zame kawai ta kwanta a wajen tana maida numfashi,babu abinda zuciyarta ke ayyano mata sai irin rayuwar da sukayi ita da adam a baya,yadda ya kula da ita ya tattalata,amma zuwa wannan lokacin ya juye ya koma mata wani irin baqirin shaidanin kumurcin maciji me cike da guba da kuma dafi.
Lokacin data fuskanci jinin cikin da cisge mata ta qarfi da yaji ya dauke,sai tayi wanka ta daura babban towel tayi sallah,baya rufe bandakin,don bazai iya jigilar gyara gurin ba idan ta bata. Darajar sallar data fara yi sai ta fara samun nutsuwa cikin ruhinta,daga mugun likitan har annamimin malamin,duk sanda sukazo saidai tabisu da ido,kowa ya gama mugun alkaba'insa ya fice,me allura yayi,me kawo tofin qarya ya kawo ya ajjiye saboda adam din yanason ya tara evidence na cewa yana kula da ita,kuma tabbas lalurarta akwai aljanu a ciki.
Ko sau daya bata taba bata ba a lissafin kwanakin daya ragewa ahalinta su dawo,ranar da take sanya ran kwanaki biyu ko daya suka rage musu su dawo,bayan likitan ya gama dirka mata allurar ba tare da sunbi takan matsanancin ciwon kan dake gallabarta ba,wanda ya sake sanyawa ta zuqe ta rame ta koma 'yar firit,sai sassanyan kyantannan da har yanzu yana nan shinfide a fuskarta.
Page 50
*H U G U M A*
*_TABARMAR ƘASHI_*💔
Page 50
Idanunta a lullumshe,tana ganinsa dishi dishi,amma ranta cike fal da baqinciki da kuma zallar bacin rai na hana mata samun salla,don tana gama alwala kafin takai ga tayar da sallar suka shigo mata
"Kaji tsoron Allah" ta samu ta fusgi kalmomin daga bakinta,cikin sautin galabaita,a fusace ya dawo gabanta ya tsaya,ya sa hannu ya matse fuskarta cikin hannunsa da kyau,wani zafi ya ratsa fatarta,ta runtse idanunta a galabaice
"Ke zan cewa kiji tsoron Allah,muguwa wadda bataso a qaru da ita,kina ta sakani ina sake asarar ragowar kudin hannuna gurin siya miki alluran da zasu ladabtarmin da ke,na rantse miki da Allah bazan taba barinki ki kubuta ba har sai kin fiddomin da jakata" yana kaiwa wannan ya jefar da ita ya fice yana huci.
Ringing din ya tsaya,muryar ummin ta bayyana radau tare da yin sallama
"Zasu kasheni,zai kasheni" abinda ta fada kenan cikin qaraji,saboda nasarar bankado qofar da adam din ya samuyi,dalilin da ya sanyata faduwa gefe qasa warwas,taku biyu ya isa gabanta,yasa hannunsa ya damqe bakinta da kyau,ta inda babu damar da zatayi magana,ya zubamata ido da wani irin kallo na zallar rashin imani yana duban fuskarta tare da ja mata zazzafan gargadi da idanun nasa,sannan ya miqa hannu ya dauki wayar da har zuwa lokacin ummi ke fama cewa hello hello jin shuru ba'a sake magana ba.
Kiran ya kashe sannan ya sakar mata baki,ya koma saman toilet ya zauna yana maida numfashi,ransa a matuqar bace
"Kin ginawa kanki da kanki rami,zakisan cewa bani da imani" yana fadin hakan ya kamata,saidai taqi miqewa tsaye sam,bai damu ba ya riqe hannunta da kyau ya fara janta a qasa kamar kayan wanki,bai ajjiyeta ko a ina ba sai a gaban likitan
"Kayi mata allurar bacci,ka hada mata data 'yan shaye shaye me qarfin" tana ji tana gani ya danneta aka hada ruguntsumin alluran aka dirka mata,a hankali jikinta ya fara saki,saidai idanuwanta basu daina zubar da ruwan hawaye ba,hakanan bakinta bai fasa fadin
"Allah ya isa,Allah ya sakamin,Allah ka yimin sakayya".
Bai ko dubeta ba ya jawo stool gabanta ya zauna,yayi kiran ummi. Bugu daya ta daga a matuqar rikice
"Me yake faruwa da sãahar din?"
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un,muna cikin mummunan tashin hankali" ya fada da muryar kuka wadda a wajen ya qirqireta
"Me ya faru?"
"Ibtila'i ne ya samemu,na fita lafiya na dawo na tarar da ita cikin wani yanayi,ina shigowa kawai ta cakumeni ta fara fadin mugu azzalumi,ka cuceni zaka kasheni,Allah ya isa,Allah ya sakamin,ina tsammanin mummunan gamo tayi,don cewa tayi waita ganni da wata muna aikata alfasha,bayan kuma ni dawowata kenan daga tafiya,kwanana uku bana garin,yanzun haka gata ta sume,da qyar na samo kanta,duk tayi fashe fashe a dakinta" salati ummi ta saki tana sallalami cikin matuqar tashin hankali
"Yanzun tana ina?"
"Gamu a gida,amma na yiwa wani malami waya yana kan hanyar zuwa"
"Ganinan nima" ta fada a gaggauce tana kashe kiran.
Iska ya furzar daga bakinsa,sannan cikin hanzari ya fara kiran wata number wayar daban. Bugu uku aka daga,sai ya miqe yana fita a dakin,yana amsa wayar a gaggauce.
Sake lumshewa idanunta sukayi hade da wani zazzafan hawaye,zuwa lokacin sama sama takejin komai,hakanan dishi dishi take ganin abubuwa,amma duk da haka kwanyarta bata daina aiki ba,bata kuma daina haska mata girman cin amanar da adam yake Shirin aikata mata ba,wadda tafi abinda ya aikata mata a baya girma da muni. Kafin ya dawo bacci tuni yaci qarfinta.
Sanda ta farka ta ganta ne kawai kaca kaca cikin shirgi da shara,tana yashe a qasa cikin dattin,gaba daya dakin ya kacame,hatta da mirror da wanda ke jikin sif din a farfashe yake,duk wani kayan ado da qawa dake dakin wanda hannu zai iya kaiwa gareshi a fashe yake.
Cikin mamaki ta miqe ta zauna tana jin kallon ko ina,ita daya ce qwallin qwal a ciki,saita zabura ta miqe ta sauri ta nufi bakin qofa,tana fatan ta samu qofar a bude.
Tana isa bakin qofar muryar ummi ta fara jiyowa,wannan ya sanya da azama ta dora hannunta kan handle din ta fara jijjigashi tana fadin
"Ki taimakeni..... kasheni yakeson yi,ki budemin,ki tafi dani don Allah" ta furta iyakar budewar muryarta,wadda bata da wani amo sam sam kasancewarta mai sanyin murya tun asali.
Adam dake zaune qasan kujera wurjajan ya daga jajajyen idanunsa da sukayi jajur ya kalli qofar,kamar yadda idanun ummi dake sharce hawaye itama suke duban qofar
"To hajiya kinji irin takeyi,kuma duk sharrinsu ne" cewar wanda ke zaune daura da adam din,cikin babbar rugar malum malum harda rawani,da kuma tsayayyen gemun da wala'alla ciko ne akayi masa yayi irin wannan cikar,hannunsa kuma zabgegiyar tasbaha ce yake ta janta daya nabin daya
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un,wannan wacce irin jarabawa ce ta saukarmiki sãahar da qananun da ko ashirin basu haura ba?" Ta fada cikin kuka
"Hajiya kar ayi sabo,shi lamarin ubangiji haka yake,jarrabawa kuma babu ta inda bata saukarwa bawa" malamin qaryar ya fada yana shafa gemunsa cikin nuna zallar taqawar da babu ita ko kusa ko alama cikin zuciyarsa
"Yanzu ba yadda za'a yi na ganta?" Da sauri ya girgiza kai
"Ai hajiya muddin aka rabata da wannan dakin ba abinda bazai iya faruwa ba,zasu iya dauketa ma a nemeta a rasata,shi kansa likitan da kikaga ya fita yanzu saida Allah yasa bacci ya dauketa ya iyayi mata gwaje gwajen da yayi,shima kuma yaga alamun tabuwar kwanya kadan,duk da hakan na iya yiwuwa duk cikin sharrinsu ne".
A yadda suka tsara komai abune mawuyaci ka fahimci cewa shiri ne irin na adam da muqarrabansa,cikin kwana daya tal ya maidata mahaukaciyar qarfi da yaji,kusan kullum a nan ummi ke yini,gudun tonuwar asirinsa yasa aka dinga yawaita yi mata allurar bacci da aka cakudata da allurar sanya maye,abinda ya qara nakasta garkuwar jikinta,ya zamana ko cikakken zama bata iyayi,data zauna din sai bacci,kota dinga bin kowa da kallo kamar sokuwa,sukayi amfani da wannan damar sukace maganin da malamin yakeyi mata ne ya fara aiki a jikinta.
Fadin irin tashin hankalin da iyalan Dr mamman jarma suka shiga a qasar saudiyya sakamakon mummunan labarin tabuwar qwaqwalwar sãahar da suka samu bata baki ne,kada ma afifa taji labari,wadda a jikinta ta dinga jin cewa ba haka bane,hauka yana da sila da kuma sanadi idan ma har haukanne,koda ta sanadiyyar jinnu ne suna nuna wasu alamomi kafin sukai ga taba lafiya kwanyar mutum,tunda suke da sãahar basu taba ganin wani abu na daban tattare da ita ba da yake da alaqa da irin wannan lalurar.
Mutane ne masu tsananun dattako da yarda da Allah wahidun ahadun,sun yi imani suna qofar waraka,qofar karbar dukkan addu'ar me neman,wajen biyan buqatar duk wani mabaraci,dukkaninsu sai suka duqufa da addu'a ta nema mata sassauci da waraka,tana da gata me yawa da soyayyar iyaye da yayye,hakanan qananun yaran da suka kasance 'ya'yan 'yan uwanta suna tsananin sonta,saboda ita din mutum ce me son yara qwarai,akwai soyayya da sabo sosai a tsakaninsu.
Kwanakin da suke gabansu na ranar dawowa Nigeria sai suka zame musu kwanaki mafiya tsaho,duk da haka basu bari sunyi asarar kwanakin ba,sunci gaba da addu'a da ibada,tare da samin information na halin da ake ciki a wajen ummi.
**************Ta fuskanci duk wani abu da zatayi babu abinda zai hana adam aiwatar da abinda ya shirya mata,hakanan a yadda ya tsara din ta tabbata cikakkiyar mahaukaci ga idon kowa,tana jin muryoyin 'yan uwa makusanta daga parlor din gidan masu zuwa dubiya gurin ummi,saidai ta zame ta kwanta lamo tana jinsu,don zuwa lokacin tayi kukan da batasan iya adadinsa ba,bai kuma qara mata komai ba hakanan bai rage ba,don ba abinda adam ya fasa,saidai yana gaya mata a kullum,zabin fitarta daga wannan yanayin ko tabbatuwarta a ciki yana hannunta,ta sallameshi shima a ranar zai sallameta kowa ya kama gabansa.
Kwata kwata daina tanka masa tayi,saidai ya qaraci maganarsa ya tashi ya miqe ya fice,abinda yake sake dugunzuma ransa kenan tare da qara masa bacin rai a kanta
"Banda ina tsoron na qarasa gawar daba tawa ba,tabbas da sai nayi miki dukan da zaki raina kanki,amma ko a hakan ma muje zuwa wai mahaukaci ya hau kura" ya miqe yayi fatali da gantalelallen abincin da ya kawo mata,ya samu kyakkyawan mazauni akan qafafunta,zafin abincin ya ratsata,amma bata iya janye qafafun nata ba saboda wani azabtaccen ciwon kai da take fama dashi,ko gani bata iyayi sosai. Da zugin ya isheta saita zame kawai ta kwanta a wajen tana maida numfashi,babu abinda zuciyarta ke ayyano mata sai irin rayuwar da sukayi ita da adam a baya,yadda ya kula da ita ya tattalata,amma zuwa wannan lokacin ya juye ya koma mata wani irin baqirin shaidanin kumurcin maciji me cike da guba da kuma dafi.
Lokacin data fuskanci jinin cikin da cisge mata ta qarfi da yaji ya dauke,sai tayi wanka ta daura babban towel tayi sallah,baya rufe bandakin,don bazai iya jigilar gyara gurin ba idan ta bata. Darajar sallar data fara yi sai ta fara samun nutsuwa cikin ruhinta,daga mugun likitan har annamimin malamin,duk sanda sukazo saidai tabisu da ido,kowa ya gama mugun alkaba'insa ya fice,me allura yayi,me kawo tofin qarya ya kawo ya ajjiye saboda adam din yanason ya tara evidence na cewa yana kula da ita,kuma tabbas lalurarta akwai aljanu a ciki.
Ko sau daya bata taba bata ba a lissafin kwanakin daya ragewa ahalinta su dawo,ranar da take sanya ran kwanaki biyu ko daya suka rage musu su dawo,bayan likitan ya gama dirka mata allurar ba tare da sunbi takan matsanancin ciwon kan dake gallabarta ba,wanda ya sake sanyawa ta zuqe ta rame ta koma 'yar firit,sai sassanyan kyantannan da har yanzu yana nan shinfide a fuskarta.
Page 50
*H U G U M A*
*_TABARMAR ƘASHI_*💔
Page 50
Idanunta a lullumshe,tana ganinsa dishi dishi,amma ranta cike fal da baqinciki da kuma zallar bacin rai na hana mata samun salla,don tana gama alwala kafin takai ga tayar da sallar suka shigo mata
"Kaji tsoron Allah" ta samu ta fusgi kalmomin daga bakinta,cikin sautin galabaita,a fusace ya dawo gabanta ya tsaya,ya sa hannu ya matse fuskarta cikin hannunsa da kyau,wani zafi ya ratsa fatarta,ta runtse idanunta a galabaice
"Ke zan cewa kiji tsoron Allah,muguwa wadda bataso a qaru da ita,kina ta sakani ina sake asarar ragowar kudin hannuna gurin siya miki alluran da zasu ladabtarmin da ke,na rantse miki da Allah bazan taba barinki ki kubuta ba har sai kin fiddomin da jakata" yana kaiwa wannan ya jefar da ita ya fice yana huci.