Sashe 62
Tabarmar Kashi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
_NOTE:wadannan matsalolin da suke babbar masifa ce suna nan suna ruruwa cikin al'umma,a yanzu dan qanwarki ko dan yayarki yana iya cin zarafinki,uwarsa ta goya masa baya,saboda suna yiwa dangin nan dan ihsanin da bai taka kara ya karya ba,su kansu masu fada aji a dangin sai kaga sun zama hoto,basu da wani amfani saboda ba kowa suke iya juyawa ba,sun wulaqantar da kansu saboda suna tsoron wasu sashe,idan sunyi ba dai dai ba basu isa su hukuntasu ba,ke kuma uwa wallahi wallahi kanki kikewa baqar dabara,kin nunawa 'ya'yanki kowa baida mutunci,babu me gaya musu suji,saboda kema a haka kika taso,kina ganin kinfi qarfin a baki shawara ko a tsawatarmiki,kin ruguza iyalinki da hannunki,bayan babu ranki haka zasuci wahala,saboda masuyi don ganin idanunkin guduwa zasuyi su barsu,kina qabari ke kuma kina amsar query akan tarbiyyar da kika yiwa yaranki,kina qabari ana nan duniya ana alawadai da halin yaranki,abinda kina raye babu me iya fada,kin mutu kin barwa dangi masifa,qila akwai mata a cikinsu,sai kiga yarinya ta kasa zaman gidan miji,ta kasa biyayyar aure saboda a tarbiyyar da uwarta tayi mata batasan biyayya ba saidai ita a bita,sai tsananin rabo yake zaunar dasu,to duka mu sani,dake uwa da kika zama shashasha sauna,wadda ke iya bari diyan cikinta su wulaqanta 'yan uwanta saboda yunwar ilimin addini da qarancinsa,dasu dangi da suke ganin barna su kasa tsaiwa a gyara saboda kowa yana tsoron fadin gaskiya,ta silar haka zumunci ya gurgunce,wallahi wallahi kowa sai ya tsaya yayi bayani gaban Allah,da wanda aka cuta da wansa yayi cutar,Allah ka bamu dacewa,ka bamu ikon tsaiwa akan gaskiya akan mutum ko wayeshi,komai girma da matsayinsa,ka rabamu da kwadayin abun hannun kowa,ka wadatamu da wadatar zuci daga gurinka👏🏽_
Page 56
*H U G U M A*
*_TABARMAR ƘASHI_*💔
Page 56
Cikin lokacin kowa qoqari yake ya faranta ran sãahar,tamkar rige rige akeyi,kowa yana bakin qoqarin ganin ya sanyata walwala,dukkansu sun fahimci depression ya fara kamata,ta soma wasu attitude da suke bayyana hakan. Anty farheen ita ta tashi tsayin daka a kanta,daga qarshe ta karbeta daga hannun maama,duk da maaman taso a barta da diyarta,to amma farheen din nada wani irin kirki da tausayi,dole ta haqura ta bar mata ita.
Zamanta hannun farheen yasa ta qaru da abubuwa masu tarin yawa,sannan ta taimaka mata wajen mantawa da wasu abubuwan,tare da fara dawowa cikin saitinta. A lokacin ya muhyiddeen ya samu wani aiki a Scotland,sai duka suka tattara har sãahar din suka wuce can. Koda sukaje din asibiti me kyau farheen tasa yaa muhyi ya duba musu suka fara zuwa ita da sãahar din,akwai sashen guiding and counselling masu kula da matsaloli irin wadan nan da hanyoyin kubutar da tunani daga wannan damuwar,abinka da qasashen da sukaci gaba,watanni kadan saiga sãahar din ta koma dariyarta da walwalarta,ta sake murjewa,gayu ya sake zama a jikinta fiye da kima saboda tasirin zamanta da anty farheen,idan ka ganta saita bala'in burgeki ke da kika diya mace ma,nan da nan anty farheen tayi amfani da wannan damar ta nema mata makaranta da kanta,ta dora karatun mastering degree dinta.
Cikin shekarun komai yazo ya wuce,saidai babu ta yadda za'a ji ciwo sannan a warke ba tare da ya barwa mutum tabo ba,koda a gangar jiki ne bare kuma a guri me matuqar muhimmanci da sammatsi irin ZUCIYA,zalincin adama gareta yasa ta hadu sa ciwon kai mai matuqar tsanani sanadin alluran da aka dingayi mata ba bisa qa'ida ba,wanda inda ace anci gaba da yinsu,tsaf kwanyarta zata juye cewar likita,wannan tabon shine abinda ya haifarwa da sãahar tsanar maza,tsana me tsanani,babu halitta da takewa bahagon kallo irinsu,ta tsani taji kalmar soyayya,kalmar AURE kuwa tana sanyata jin wani tashin hankali,kwatankwacin mutumin da yaqi ya tunkaro shi,duk wani abu da zai sanyata hulda da maza ta datseshi,wannan ne yasa tunda suka dawo Nigeria tayi zamanta wajen anty farheen dake ji da ita,take kuma sake maidata macen da idan aka kalla sai an sake juyawa an kalla cikin hikima. Batason kowa yayi mata zancan aiki,shi yasa taqi fidda results nata data samu,results me kyau da yayi bala'in burge yayyenta,duk da dama tunda can sunsan ita din bata da wasa ta fannin karatu,hakanan tana da kwanyar da dukka cikin gidan ita da yaa Saifullahi keda irinta,duk da sauran suma ba daga baya ba,wannan yasa kowanne yake riqe da wani babban matsayi,ya kuma tara dukiyar da a qananun shekarunsu idan aka gaya maka yawanta zakayi mamaki,dukka cikinsu babu rago,babu kuma koma baya.
A wancan lokacin sati guda dr mamman yace su zain su saki adam,su barshi da halinsa,yayi imanin bazai gama rayuwa a daron duniya ya wanye qalau ba tare da Allah ya hukuntashi ba,duk kuma yadda sukaso hukuntashi hukuncin Allah shine gaba da nasu. Hatta da afifa bata bayar da goyon baya ba,ita inda son samu ne,akai adam din muhallin da hatta hasken rana baya shiga gurin ayi masa daurin rai da rai.
Sun bar dr mamman aka cewa an sakeshi,amma basu barsu ba saida sukayi watanni uku cur suna karban hukunci a hannun sajoji,kafin sannan kuwa gaba dayansu ba wanda baiji a jikinsa ba,duk wani abu da sukasan ya mallaka ta silarsu sun karbeshi,ciki harda gidan da momee ke zaune,da wanda suka rayu shi da sãahar,sai a sannan suka gane cewa gidan ashe shima ya saidashi,ta yadda idan yabar qasar saidai sãahar taji ana batun ta tashi ga masu gida. Tuni suka sayar da gida,su kuma ainihin wadanda suka siya a wajensa dama baikai ga basu takardun ba,ya karba kudinne kawai,nufinsa sai ranar da zasu bar qasar ya danqa musu ya qara gaba,sukace ba zasu yarda ba,yaa zain yace su nema kudinsu a hannun dan damfarar da suka bawa. Sunsan tako ina family din dr mamman girema ba abun wasa bane,sunfi kuma qarfin wannan gidan bare suce cuwa cuwa sukayi,don haka suka karkata akalar tuhumarsu ga adam wanda a sannan ko gidan da zai kwanta a ciki ya huce tarin gajiyar da sojojin suka hada musu ya kuma yi jinyar raunukan jikinsa bashi dashi.
A sannan tuni abba ya samawa raihanatu karatu a maryam abacha American university dake garin maradi a jahar nijer,tana can ta dora karatunta daga inda ta tsaya,babban burinta kenan a rayuwa,wanda momee tasha gaya mata bazai taba cika ba,ba zata dinga adashin da batasan ranar kwasarsa ba.
*Dama hausawa sukance ALHAKI KWAIKWIYO NE,ME SHI YAKE BI*
_DUK INDA ZA'A JE AZO KA TABBATAR KAI AKA CUTA,KARKA ZAMA KAINE WANDA KAYI WANANN CUTAR,A RABUWAR AURE 'YAN UWANA MATA,KARKI YADDA IDAN TA KAMA A RABUN YA ZAMANA KECE ME MATSALA KO KECE AZZALUMAR, WALLAHI KIKA BARI HAKA TA FARU KUMA KIKA FITO SAIKIN RAINA KANKI,MUDDIN KE AKA ZALUNTA,KARKIYI KAICO,KADA KUMA KIYI BAQINCIKI,DOMIN ALLAH BAYA KI GYANGADI BARE BACCI_
*_wannan kenan_*
*_Dawowa labari_*
Juyawa ta sakeyi a karo na babu adadi bayan gama dukka wannan bitar da qwaqwalwarta tayi,gefan da afifa ke kwance ta kalla,kusan wasu matsalolin tare suka fuskancesu ita da afifan,amma sau tari sai taji inama itace afifan?,inama bata taba sanin wani adam ba bare ya shiga rayuwarta ya cutar da ita haka ba?. Tsaki taja qasa qasa bayan fargar da ita da zuicyarta tayi,saita miqe ta sauko daga gadon a hankali ta nufi toilet,cikin ranta tana sake jin yaqini da qwarin gwiwar cewa,ya zame mata tabbas tayi wani abu,har yanzu batajin cewa tayi warkewar da zata doshi wani aikin ko kuma aure,dole tayi hobbasar da zata sake nesantata daga dukkan wata mu'alama da zata sake hadata da azzalumar halittar maza,marasa tausayi da jin qai,marasa amana kuma,dole ta yiwa kanta wannan aikin.
Daren gaba daya ta raya,da tarin addu'o'in ta da buqatunta jingim wajen Allah,ko kafin ta kammala ma wata irin nutsuwa ta maye gurbin bacin rai da fargabar dake motsa zuciyarta,albarkacin wannan kuma a nan saman abun sallar daddadan bacci ya saceta.
Afifa ta rigata tashi sallar asuba,batayi mamakin ganinta a kwance a nan ba,saboda ba kowanne dare ne take iya kwanciya ta shareshi dukka tana bacci ba,saita qarasa cikin tausayawa da qauna ta tabata tana kiran sunanta. Idanunta ta bude tana kallon afifa
"Ya shehiya sãahar,a tashi ayi sallar asuba,Allah ya amsa addu'ar nan,ina fatan kin sakani a ciki,Allah ya kawo masoyi na gari" qaramin murmushi tayi duk da cewa daga bacci ta tashi,hakan kuma ya sake qarawa fuskarta kyau,sai da tayi brush ta daura alwala ta fito sannan ta amsa mata
"Allah ya kakkawo,saidai ita afifa akwai wanda take jira" bata tsaya jin amsarta ta tayar da sallah ta barta da baki a bude tana cewa dariya nason kamata
"Kajimin yarinya zatamin sharri?".
Dukka wani azkar data saba yi sai data yishi,haka kawai taji idanunta babu wani sauran bacci,duk da cewa ba wani baccin kirki ta samu ba adaren jiyan,don haka ta shafa addu'o'inta ta nade abun sallar,ta dauki wayarta ta koma saman gadon su,tana kallon afifa da idanunta ke rufe,da alama bacci ne sosai a kanta, saita ja duvet itama tana shirin rufa,dai dai lokacin da tex din ahmad ke shigowa wayarta.
Ko bata buda ba tasan saqon barka da safiya ne,taja qaramin tsaki,tana tunanin sai yaushe zai gaji da naci yace ya haqura da ita?,ba amsa,don haka ta share saqon bayan ta buda wayar.
Watsapp tahau zata buda wani qaramin document na addu'o'i da anty farheen ta turo mata,yana da dan nauyi,don haka da tayi clicking akai,sai ta fita da zummar rage jira kafin ya kammala buduwa.
Haka kawai ta samu kanta da buda jerin list na mutanen da sukayi status a safiyar ranar,duk da cewa kuwa ba dabi'arta bane hakan. Sunan mr sadeeqa yana sama sama,auntie din su nurain 'ya'yan yaa Saifullahi. Sam ta mance da matar a rayuwarta,duk da cewa tana da kirki qwarai,tun kafin tayi aure lokacin da takanje gidan yaa Saifullahi din,wani lokaci ita ke kaisu school da safe,a nan suka dan saba da ita saboda matuqar kirkinta,sai kuma dabi'arsu tason yara tazo daya,wannan ya sanya suka dan saba suke gaisawa,har sukayi exchanging numbers.
Batasan ya akayi ba hannunta ya taba status din mrs sadeeqa,take ya bude,hotone na wata baby girl,duk da cewa hoton ya danyi blurry kadan,amma hakan bazai hanaka iya gane kyan yarinyar ba,tayi rubutu a qasan hoton kamar haka
_she has being suffering and battling epilepsy,she is looking for a good nanny,praying for an easy recovery my class cute angel_😥😥.
Page 56
*H U G U M A*
*_TABARMAR ƘASHI_*💔
Page 56
Cikin lokacin kowa qoqari yake ya faranta ran sãahar,tamkar rige rige akeyi,kowa yana bakin qoqarin ganin ya sanyata walwala,dukkansu sun fahimci depression ya fara kamata,ta soma wasu attitude da suke bayyana hakan. Anty farheen ita ta tashi tsayin daka a kanta,daga qarshe ta karbeta daga hannun maama,duk da maaman taso a barta da diyarta,to amma farheen din nada wani irin kirki da tausayi,dole ta haqura ta bar mata ita.
Zamanta hannun farheen yasa ta qaru da abubuwa masu tarin yawa,sannan ta taimaka mata wajen mantawa da wasu abubuwan,tare da fara dawowa cikin saitinta. A lokacin ya muhyiddeen ya samu wani aiki a Scotland,sai duka suka tattara har sãahar din suka wuce can. Koda sukaje din asibiti me kyau farheen tasa yaa muhyi ya duba musu suka fara zuwa ita da sãahar din,akwai sashen guiding and counselling masu kula da matsaloli irin wadan nan da hanyoyin kubutar da tunani daga wannan damuwar,abinka da qasashen da sukaci gaba,watanni kadan saiga sãahar din ta koma dariyarta da walwalarta,ta sake murjewa,gayu ya sake zama a jikinta fiye da kima saboda tasirin zamanta da anty farheen,idan ka ganta saita bala'in burgeki ke da kika diya mace ma,nan da nan anty farheen tayi amfani da wannan damar ta nema mata makaranta da kanta,ta dora karatun mastering degree dinta.
Cikin shekarun komai yazo ya wuce,saidai babu ta yadda za'a ji ciwo sannan a warke ba tare da ya barwa mutum tabo ba,koda a gangar jiki ne bare kuma a guri me matuqar muhimmanci da sammatsi irin ZUCIYA,zalincin adama gareta yasa ta hadu sa ciwon kai mai matuqar tsanani sanadin alluran da aka dingayi mata ba bisa qa'ida ba,wanda inda ace anci gaba da yinsu,tsaf kwanyarta zata juye cewar likita,wannan tabon shine abinda ya haifarwa da sãahar tsanar maza,tsana me tsanani,babu halitta da takewa bahagon kallo irinsu,ta tsani taji kalmar soyayya,kalmar AURE kuwa tana sanyata jin wani tashin hankali,kwatankwacin mutumin da yaqi ya tunkaro shi,duk wani abu da zai sanyata hulda da maza ta datseshi,wannan ne yasa tunda suka dawo Nigeria tayi zamanta wajen anty farheen dake ji da ita,take kuma sake maidata macen da idan aka kalla sai an sake juyawa an kalla cikin hikima. Batason kowa yayi mata zancan aiki,shi yasa taqi fidda results nata data samu,results me kyau da yayi bala'in burge yayyenta,duk da dama tunda can sunsan ita din bata da wasa ta fannin karatu,hakanan tana da kwanyar da dukka cikin gidan ita da yaa Saifullahi keda irinta,duk da sauran suma ba daga baya ba,wannan yasa kowanne yake riqe da wani babban matsayi,ya kuma tara dukiyar da a qananun shekarunsu idan aka gaya maka yawanta zakayi mamaki,dukka cikinsu babu rago,babu kuma koma baya.
A wancan lokacin sati guda dr mamman yace su zain su saki adam,su barshi da halinsa,yayi imanin bazai gama rayuwa a daron duniya ya wanye qalau ba tare da Allah ya hukuntashi ba,duk kuma yadda sukaso hukuntashi hukuncin Allah shine gaba da nasu. Hatta da afifa bata bayar da goyon baya ba,ita inda son samu ne,akai adam din muhallin da hatta hasken rana baya shiga gurin ayi masa daurin rai da rai.
Sun bar dr mamman aka cewa an sakeshi,amma basu barsu ba saida sukayi watanni uku cur suna karban hukunci a hannun sajoji,kafin sannan kuwa gaba dayansu ba wanda baiji a jikinsa ba,duk wani abu da sukasan ya mallaka ta silarsu sun karbeshi,ciki harda gidan da momee ke zaune,da wanda suka rayu shi da sãahar,sai a sannan suka gane cewa gidan ashe shima ya saidashi,ta yadda idan yabar qasar saidai sãahar taji ana batun ta tashi ga masu gida. Tuni suka sayar da gida,su kuma ainihin wadanda suka siya a wajensa dama baikai ga basu takardun ba,ya karba kudinne kawai,nufinsa sai ranar da zasu bar qasar ya danqa musu ya qara gaba,sukace ba zasu yarda ba,yaa zain yace su nema kudinsu a hannun dan damfarar da suka bawa. Sunsan tako ina family din dr mamman girema ba abun wasa bane,sunfi kuma qarfin wannan gidan bare suce cuwa cuwa sukayi,don haka suka karkata akalar tuhumarsu ga adam wanda a sannan ko gidan da zai kwanta a ciki ya huce tarin gajiyar da sojojin suka hada musu ya kuma yi jinyar raunukan jikinsa bashi dashi.
A sannan tuni abba ya samawa raihanatu karatu a maryam abacha American university dake garin maradi a jahar nijer,tana can ta dora karatunta daga inda ta tsaya,babban burinta kenan a rayuwa,wanda momee tasha gaya mata bazai taba cika ba,ba zata dinga adashin da batasan ranar kwasarsa ba.
*Dama hausawa sukance ALHAKI KWAIKWIYO NE,ME SHI YAKE BI*
_DUK INDA ZA'A JE AZO KA TABBATAR KAI AKA CUTA,KARKA ZAMA KAINE WANDA KAYI WANANN CUTAR,A RABUWAR AURE 'YAN UWANA MATA,KARKI YADDA IDAN TA KAMA A RABUN YA ZAMANA KECE ME MATSALA KO KECE AZZALUMAR, WALLAHI KIKA BARI HAKA TA FARU KUMA KIKA FITO SAIKIN RAINA KANKI,MUDDIN KE AKA ZALUNTA,KARKIYI KAICO,KADA KUMA KIYI BAQINCIKI,DOMIN ALLAH BAYA KI GYANGADI BARE BACCI_
*_wannan kenan_*
*_Dawowa labari_*
Juyawa ta sakeyi a karo na babu adadi bayan gama dukka wannan bitar da qwaqwalwarta tayi,gefan da afifa ke kwance ta kalla,kusan wasu matsalolin tare suka fuskancesu ita da afifan,amma sau tari sai taji inama itace afifan?,inama bata taba sanin wani adam ba bare ya shiga rayuwarta ya cutar da ita haka ba?. Tsaki taja qasa qasa bayan fargar da ita da zuicyarta tayi,saita miqe ta sauko daga gadon a hankali ta nufi toilet,cikin ranta tana sake jin yaqini da qwarin gwiwar cewa,ya zame mata tabbas tayi wani abu,har yanzu batajin cewa tayi warkewar da zata doshi wani aikin ko kuma aure,dole tayi hobbasar da zata sake nesantata daga dukkan wata mu'alama da zata sake hadata da azzalumar halittar maza,marasa tausayi da jin qai,marasa amana kuma,dole ta yiwa kanta wannan aikin.
Daren gaba daya ta raya,da tarin addu'o'in ta da buqatunta jingim wajen Allah,ko kafin ta kammala ma wata irin nutsuwa ta maye gurbin bacin rai da fargabar dake motsa zuciyarta,albarkacin wannan kuma a nan saman abun sallar daddadan bacci ya saceta.
Afifa ta rigata tashi sallar asuba,batayi mamakin ganinta a kwance a nan ba,saboda ba kowanne dare ne take iya kwanciya ta shareshi dukka tana bacci ba,saita qarasa cikin tausayawa da qauna ta tabata tana kiran sunanta. Idanunta ta bude tana kallon afifa
"Ya shehiya sãahar,a tashi ayi sallar asuba,Allah ya amsa addu'ar nan,ina fatan kin sakani a ciki,Allah ya kawo masoyi na gari" qaramin murmushi tayi duk da cewa daga bacci ta tashi,hakan kuma ya sake qarawa fuskarta kyau,sai da tayi brush ta daura alwala ta fito sannan ta amsa mata
"Allah ya kakkawo,saidai ita afifa akwai wanda take jira" bata tsaya jin amsarta ta tayar da sallah ta barta da baki a bude tana cewa dariya nason kamata
"Kajimin yarinya zatamin sharri?".
Dukka wani azkar data saba yi sai data yishi,haka kawai taji idanunta babu wani sauran bacci,duk da cewa ba wani baccin kirki ta samu ba adaren jiyan,don haka ta shafa addu'o'inta ta nade abun sallar,ta dauki wayarta ta koma saman gadon su,tana kallon afifa da idanunta ke rufe,da alama bacci ne sosai a kanta, saita ja duvet itama tana shirin rufa,dai dai lokacin da tex din ahmad ke shigowa wayarta.
Ko bata buda ba tasan saqon barka da safiya ne,taja qaramin tsaki,tana tunanin sai yaushe zai gaji da naci yace ya haqura da ita?,ba amsa,don haka ta share saqon bayan ta buda wayar.
Watsapp tahau zata buda wani qaramin document na addu'o'i da anty farheen ta turo mata,yana da dan nauyi,don haka da tayi clicking akai,sai ta fita da zummar rage jira kafin ya kammala buduwa.
Haka kawai ta samu kanta da buda jerin list na mutanen da sukayi status a safiyar ranar,duk da cewa kuwa ba dabi'arta bane hakan. Sunan mr sadeeqa yana sama sama,auntie din su nurain 'ya'yan yaa Saifullahi. Sam ta mance da matar a rayuwarta,duk da cewa tana da kirki qwarai,tun kafin tayi aure lokacin da takanje gidan yaa Saifullahi din,wani lokaci ita ke kaisu school da safe,a nan suka dan saba da ita saboda matuqar kirkinta,sai kuma dabi'arsu tason yara tazo daya,wannan ya sanya suka dan saba suke gaisawa,har sukayi exchanging numbers.
Batasan ya akayi ba hannunta ya taba status din mrs sadeeqa,take ya bude,hotone na wata baby girl,duk da cewa hoton ya danyi blurry kadan,amma hakan bazai hanaka iya gane kyan yarinyar ba,tayi rubutu a qasan hoton kamar haka
_she has being suffering and battling epilepsy,she is looking for a good nanny,praying for an easy recovery my class cute angel_😥😥.