← Book details Tabarmar Kashi Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 95 OF 171

Sashe 95

Tabarmar Kashi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

A hankali qofar ta bude,ya bayyana daga bakin qofar da daurarriyar fuskar nan tasa,tashin farko qamshin da dakin ke fiddawa ya marabci hancinsa kafin a sannu idanunsa su suka a bayanta da fara qal don brassiere dinta ta bayyana. Sosai ta razana don batayi tunanin ganinsa ba wannan lokacin,tunawa tayi da zugaggen zip dinta data tabbatar a vadda ya sauka har brassiere dinta za'a iya gani,wanann tunanin ya sanyata juyawa da sauri kamar numfashinta zai dauke ba tare data tuna yadda rigar ta fidda tudun qirjinta ba da kyau.

Kamar daukewar majigin tv,gushewar baya zuwa bayyanar qirjinta ga idanunsa duka sun faru cikin abinda baiyi damanda second uku ba,bazaice ga yadda akay ba ya samu idanunsa dumu dumu suna kallon qirjin nata ba da suke a cike,farar fatar dake lullube ko ta ina ta jikinta ta bayyana daga samansu tana nuna mizanin cika da suke da ita. Wani mugun fusga ya yiwa numfashinsa da idanun nasa ma gaba daya yana sanya qarfin zuciya dana ruhi gurin janye kallonsa daga kanta. Yayin da sãahar din gaba daya ta qarasa rudewa,ta fisgi dankwalinta dake ajjiye saman madubin ta yafa ranta a bace.

Tamkar baiga komai ba ya sanya kansa cikin dakin yana furta sallama can qasa,kanshi tsaye yake takowa dakin tamkar dai mallakinsa bawai nata ba,bai tsaya ba har sai da ya isa kusa da bedside drawer ya zube dukka ledojin a kai ba tare da ya dauki ko daya ba,sannan ya juya abinsa zai fice daga dakin. Kasa jurewa tayi,tadan daga muryarta kadan

"Ba kowanne daki bane mallakinka a yanzu,kafin shiga kowanne daki a gidan nan ya zama dole ka nema izini" tsaiwar mashi maganar tayi masa bisa kansa,har ya rage saurin tafiyar tasa,sai kuma yaci gaba da ficewar,saboda wata kasala dake sauka a kowanne sashe na jikinsa,muddin kuma yace zai tsaya cewa wani abu,a matsayinta na me aure na biyu dole zata fuskanci wani sauyi tattare dashi, wanda hakan mugun abun kunya kasawa da kuma gazawace a tattare dashi but yayi alqawarin zai saita mata bakinta da wasu dabi'u nata,bazai yarda da rashin girmamawa ba,she can live duk yadda taso,amma dole tasan girmansa.

Tsuka tayi ta murguda bakinta saboda baqincikin da ya cikata,batasan tsautsayin da ya sanyata barin qofarta a bude ba,bata taba kawowa wai zai shigo ba wannan shine dalili,amma dole daga wannan karon ta tabbatar bai sake shiga mata daki ba. Har tayi banza da ledojin daya shigo dasu,sai kuma taga duk abinda ta bari ya lalace zai shiga sahu ne na almubazzaranci.

Short note din data gani jikin wata
leda ya bata tabbacin babu abinda ya siya da kansa ko daya,dukka sagon maji ne.
Murmushi ya subuce mata,tana qaunar mata sosai har cikin ranta,sonta majin take da gaske har hakan baya iya boyuwa,ta miqe ta adana komai ta dawo ta rage kayan jikinta ta kwanta.

"HUGUMA*

•_TABARMAR KASHI_*

Book 02Page 13

Cikin nutsuwarsa ya gama komai na shirin bacci,saidai gaba days baccin ya gagara zuwa a idanunsa,ganin dazun yayi affecting tunaninsa sosai,abinda bai taba kawowa cikin ransa zai zama wani abu har haka ba. Da kansa ya buda qofar dakinsa ya wuce kitchen ya hada coffee ba tare daya bi takan abincin dake jere a dining ba,aikin jacob kenan, baya wasa da aikinsa,duk wata hidima da ake muddin yana qasar yana kuma gari baya fashin dafa masa abinci,ko a yanzun duk hidimar da akeyi cikin gidan part dinsa baisan anayi ba,shi yasa yakeji da jacob din shi da wanda yake tsaftace masa sashensa.basu da wasa sam a aikinsu

Dakinsa ya dawo,ya buda balcony
din dake manne dashi,duk da cewar dare ne amma bai damu da hakan ba,bacci kawai yake nemawa idanunsa tare da hutu da nutsuwar
ruhi da gangar jiki.

Kurba daya yayi masa kamar lokutan
baya ya ajjiye saman dan qaramin table din dake a gefansa,tun daga waccan ranar daya dandani taste din coffe dinta kowanne ya daina masa dadi a harshensa,saidai yasha Black tea Kawaltunda bava snan madara kwata kwata,ko ya gwada shan madaran da nufin ko zai yi masa irin taste din milk tea dinta
sai yaji gaba daya basu hada hanya ba.

Tafin hannayensa ya hada yana murzawa
guri guda da sauri da sauri,lokaci guda ya dakata yana furzar da iska daga bakinsa,dai dai lokacin da wayarsa tayi qara. Mamakin wanda zai kirashi a dai dai wannan lokacin da sha daya na dare tayi ya kamashi,ya qarasa inda ya aje wayar a hankali ya dauka yana duba me kiran,sai kuma kiran ya katse,sagon da ya gani da number sajjad yaja hankalinsa,yayi sliding ya bude wayar ya shiga saqon

_Duk wani nutsuwa farinciki walwala da kwanciyar hankali yana tattare da diya mace muddin ka dace,ka raya darenka na yau da kyau da soyayya da kawo jituwa da fahimtar juna tsakaninka da iyalinka,zaka fahimci inda maganata ta dosa_ tsaki yaja,sajjad yana bashi ciwon kai,baisan mata bane,amma yana da tabbacin zai dawo daga mararin gardin da yake ganin ya samu. Muddin diya macace tabbas wataran sai ta bashi madacin da zai maye gurbin zaqin zumar data lasa masa a harshensa,duk kuwa da cewa baya taba yiwa wani wannan fatan bare sajjad din da dadi wuya ko tsananin yana tsaye tare dashi.

Kira ne ya shigo wayar tasa lokacin da kwanyarsa ke shirin nutsawa duniyar tunani.
A nutse ya dauki wayar ba tare da tantama shakka ko mamakin kiran da akayi masan a dai dai wannan lokacin ba,saboda waya ce da dukka kiran da zai biyo ta cikinta ya tabbatar kira ne me muhimmanci da ya shafi duk wani makusanci a gareshi.

Cikin lallausar muryarsa da ta gara yin wani irin sanyi saboda yanayin da yakeji yana bibiyar kowace gaba ta jikinsa. Saidai a maimakon amsar sallamar,sai sautin kukanta cikin siriryar muryartan me matugar siranta qwaral ta maye gurbi. Wayar yadan cira yana duba number din ya tabbatar babu wanda zai kirashi da number wannan qasar sai mutum daya wato HASEENA

"Yaa toufeeq wai da gaske ne?,da gaske ne don Allah?, kayi aure?" Tambayar tata ta daure masa kai,meye manufar wannan tambayar? duk da ya jima zuciyarsa da hasashensa suna son kaishi gurin,amma sai ya jaddadawa kansa ba hakan bane,saboda sam baya fatan yarinyar ta jefa kanta shingen da bazata iya samun aminci ba a cikinsa

"Yaa toufeeq,wallahi bazan iya jurewa ba,yaa toufeeq kai na yiwa zuciya tanadi,dukka tsahon shekarun nan,mommy ce takeyimin burki" sai ta sake sakin kukan da yake nuna ciwone daga zuciyarta na gasken gaske yake motsawa. Mamaki gaba daya ya sanyashi kasa cewa komai, yarinyar da yake kallonta bata da maraba da nadeeya a gurinsa saboda rainonsu da hajiya qaraman tayi? ‚bugu da qari sam babu hira da tayi kamanceceniya da wannan a tsakaninsa da ita

"Relax meenal,calm down" ya fada ta sigar lallashi,saboda gaba daya abun nata yana daukarsa ne kamar wani wasan kwaikwayo

"Ta yaya zan iya kwantar da hankalina yaa toufeeq,kasan yadda kake a zuciyata?"

"Are you okay?" Ya samu kansa da tambayarta kai tsaye wannan karon,saboda gaba daya mamaki ya gama cikashi

"I lost what i love most,i can't keep calm"

"Kisha magani ki kwanta,Allah ya sawwaqe" ya fadi yana sauke wayar a nutse daga kunnensa. Kafin ya kashe yana iya jin yadda take kiran sunansa,ya sake kallon wayar yana sake tabbatarwa kansa kodai akwai abinda tasha,ko kuma lallai dole ya dauki tsattsauran mataki a kanta,muddin dai meenal zata ce tana sonsa,to ba shakka raini ya fara shiga tsakaninsu kenan saboda yadda yake treating nata like nadeeya.

Qarar shigowar tex ya sake sanyashi
waiwayawa ga wayar. Dukka saqon ya gama bayyana saman screen din, kasancewarsa gajeran sago bame tsayi ba
BARKA DA WARHAKA ANGON NANA
KHADIJA,KA MOREWA WANNAN DAREN
TARE D AMARYARKA,AMMA KA SANI
AMEESHA NA NAN DAWOWA CIKIN
RAYUWARKA,SABODA BA ZATA IYA BARWA WATA KAI BA HAVE A NICE NIGHT_ Samun kansa yayi da maimaita karanta saqon,a hankali a hankali wani abu me zafi yana taba zuciyarsa, emotions dinsa marasa dadi sunason motsawa,how and when ameesha ta samu wannan courage din da zata masa saqo haka kai tsaye?,saboda ya daga mata qafa? ya bata damar taje ta rayu ta tuba?. Har ya dauki wayarsa da zummar nusar da ita kuskurenta,sai kalmar

"La haula wala quwwata illa billahil aliyyul azeem" ta subuce daga harshensa. A hankali yaji yana komawa daidai dinsa,sai ya maida akalarsa zuwa blocking number tata,sannan ya goge saqon,ya jefa wayar a aljihunsa yana migewa daga gurin,yana ji a zuciyarsa bashi da lokacinta Sam,bama yanzu ba,har abada baya jin zata sake samun lokacinsa,bawai ita kadai ba,dukka wata diya mace ma idan ka debe jininsa dinnan daya zama lazim ya rayu dasu,yake kuma da yaqinin babu cutarwa a tsakaninsu har abada.

Cikin wani yanayi yake fita dag balcony din har ya riski lafiyayyen bedroom din nasa,cikin qanqanin lokaci ya gama shirin kwanciya,ya maida hasken dakin zuwa dim light,idanunsa na lumshe yana jin kewar rashi ganin fadeela saboda cinkoson gidan,yau din tun sassafe da ya fita yabar musu gidan,duk da sashen nasa baisan me cikin gidan ke ciki ba,amma sai yakejin kamar hayaniyar gidan a tsakiyar kansa take. Bacci yake da bugatar yi sosai,to amma yanayin da yake ciki ya tabbatar idan baiyi wasa ba zaici wuya ko ya dade a haka,wannan ya sanya yana daga kwancen ya miqa hannunsa ya jawo wata mp4 me siffar qwallo fara qal ya kunnata,take sautin karatun alqur ani me girma ya karade dakin da muryar sheik mahir almu'aiqaly,karatun ya fara saukar masa da nutsuwa sosai a zuciya ruhi dama gangar jikinsa,sannu a hankali baccin da bai taba zata ba yayi awon gaba dashi.

_sai muce asuba ta gari angon nana kadija_
Chapter 95 · 0% Book details