Sashe 70
Tabarmar Kashi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A nata bangaren ayyukan fadeela gaba daya nishadi suka sanyata,sun debe mata kewar yara sosai,sun kuma nesantata da dukkan wani namiji kamar yadda take da muradi,tana jinta kamar a killace,babu idanun kowa a kanta,ta samu cikakkiyar nutsuwa da gamsuwa cikin gidan,hajiya qarama da takejin kamar zata zame mata matsala ko akwai wani illa tare da ita,saita fuskanci ba wani damuwa tayi da sassan ba,saita share kwanaki ma bata shigo ba,sai idan fadeela taje mata. To amma,shin da gaske fadeelan jikarta ce?,idan jikarta ce ta yaya mu'amala irin wannan zata wanzu tsakanin jika da kaaka?,tanason sanin labarinsu,tana son sanin ainihin wacece hajiya garama a wajen fadeela,to amma ita din bata cikin sahun mutanen da suke shiga lamuran da sukayi yaqinin basu shafi rayuwarsu ba.
*****K'arfe biyar da wasu yan mintuna na yammacin ranar ne,dai dai sanda madaidaiciyar motar me kyau ke shigowa cikin gidan,wanda da shigowarta da isowar masu aikin gidan duka duka bazaiyi minti biyu ba,cikin gaggawa kowanne ya iso,saboda sanin mamallakiyar motar,kowa yana gudun tsira da mutuncinsa.
Bude murfin motar tayi,sannan ta qwalawa daya daga cikinsu kira,matsowa tayi da gaggawa,bakinta dake tauna chewing gum ta motsa
"Daukarmin hand bag dita"
"Tom" ta fada tana buda daya side din da jakar take ta dauka ta riqe
"Kai jama'a,mutum ba uban kowa ba sai shegen ji da kai da izzar banza" tayi gorafi gasa qasa,saidai ya fidda sautin gunaguni
"Me kike cewa?" Labiba ta tambaya taba juyowa,murmushi tadan saki a rikice
"Bab.....babu komai,cewa nayi maraba da dawowa" bata sake cewa komai ba ta fita a motartabar musu aikin kashewa da rufeta hadi da rigo mata key din. Cikin jin kai take takawa,sanye da wani skinny jeans da yabi jikinta sosai ya lafe, kamar a jikin nata aka dinkashi,manyan mazaunanta da suke da wani irin dan banzan tsini sun fita sosai,saidai kuma shafaffen qirjinta dake boye a t shirt din jikinta ya kawo cikas waien cikar adon da akesonyi da bayyana abinda akeson a bayyana din. Kitson attache ne a kanta daya zuba har gadon baya,ya bullo da qasan gantalelallen mayafin data yane kanta dashi wanda iyakarsa wuyanta.
Har ta doshi sassan hajiya qarama suka shaida mata ta fita, amma ba nisa tayi ba,saita sauya akalarta ta wuce sassan fadeela,tanason ta saba da yarinyar,to amma matsalar ita batasan yadda zata shawo kanta su shaqu ba.
Dai dai lokacin da sãahar ke zaune a madaidaicin falonsu na biyu,suna zaune qasan carfet ita da fadeelan, ita tana cin abinci sãahar din na monitoring dinta,a daya bangaren tana duba homeworks din da aka basu ranar a makaranta.
Sanye take da brown din chiffon gown budaddiya sosai,sai kanta data yafawa vail na plain chiffon din shima brown da bai garasa na jikin rigar haske ba, kyakkyawar fuskarta tayi fresh,tes take fatarta na nan da glowing dinta,babu digon ko tabo ballantana qurji,pink lips dinta sai shegin lips balm sukeyi,zara zara yatsunta take sanyawa tana buda book din page by page tana ganin performance din fadeelan a homeworks dinta na baya.
Sau biyu tana buda baki da niyyar yin magana tana dora mata yatsa akan lips tace
"Shshshsh" tasan tanason yin Santi ne akan abincin da takeci, wanda säahar dince yau ta dafa. A karo na uku data hanata saita langabar da kai
"Please aunty ki barni nace wani abu mana" yadda tayi maganar yayi masifar baiwa sãahar dariya,saita rufe littafin tana murmushi idanunta akan fadeela
"Say it fadee"
"Wallahi anty ban tabacin abinci me dadin wannan ba,kamar daga aljanna aka kawosa" ba shiri dariya sosai ta kubcewa saahar,saita miga hannu ta dauki pillow ta saka mata daga gefanta
"'Bari na tareki kada santi yasa ki fadi" dariya itama ta saki sukaci gaba da yi tare
"Please aunty nanny,zaki ci gaba da dafamin abinci?,harda wanda zanje school dashi don
Allah,nasan abincina sai yafi na kowa dadi" idanu ta lumshe tana gyada kai,a yadda takejin fadeela kamar jininta babu hidimar da bazata ivayi mata ba
"Alright,amma idan satin nan ya wuce baki gama haddace suratul a'alah ba,to zan daina,kin yarda?"
"'Na yarda aunty,nayi algawarin jibi zan gama" ido ta ya fidda tana dubanta da mamaki
"Really?" Kai ta jijiga mata alamun da gaske take.
"Hi fadeela" muryar labiba dake tsaye a kansu ta ratsa kunnuwansu,dukkaninsu babu wanda yasan da shigowarta bare wanzuwarta a gurin.
Daga kansu sukayi kusan lokaci guda suka
dubeta,dai dai lokacin idanunsu suka gauraya
da juna ita da sãahar.
Dan ja baya kadan tayi cikin yanayin dake
nuna qaramar razana
"Ya salam" ta furta can gasan ranta,tana
hadiye wani abu me tauri a maqoshinta,a
ina aka samo wannan cikin gidan?" Ta yiwa
kanta tambayar da batasan amsarta ba,zataso
ta jefa tambayar ga baquwar fuskar,amma
idanunta zuwa fuskarta suna fidda wani irin
kwarini.
Sãahar ce ta fara janye idanun nata daga
kanta,ranta yana dan baci da yadda ta riskesu
gatsau kai tsaye tayi musu kuma tsaye a
ka,saita maida idanunta ga duba littafin
hannun nata ba tare data sake dagowa ta
dubeta ba,saidai a jikinta tana jin kamar tasan
fuskar,kamar ta taba ganinta a wani waje.
Tana jinta ta isa gaban fadeela ta zauna
tana ta janta da surutu,lokaci lokaci idanunta
suna satar kallon sãahar,wadda bata sake
duban sashenta ba,koda ace suna da dabi ar
yahudawa,a qalla tunda musulmi ne su tay!
musu sallama sanda ta riskesu
"Na gama anty" fadeela ta fada bayan ta ajiye
gorar ruwan hannunta
"Good bari na dauko miki hijab,qur ani zamu
fara yi" saita kife littafin ta mige zuwa dakin
fadeelan. Kallo labiba ta bita dashi hankalinta yana tashi, ko ita da take mace ta tabbatar
ta kuma yaqini hakanan ta sallama wannan
din ta cika mace wani abu me cakude da
kishi da tashin hankalin wanzuwarta a gidan
yazo yayi mata tsaye,sai ta maida dubanta ga
fadeela dake qoqarin dauke plate din da taga gama cin abincin tana tattare inda ta bata da
tissue,abinda bata taba gani yarinyar tayi ba "Wacece wannan uktie?" Duban labiban kawai
tayi,da yake itama miskilar kanta ce,kafin tace
komai baaba ramatu ta shigo falon,hannunta
dauke da humidifier da tasan sãahar na
yawan ajjiyeta a gurin saboda tsananin son
qamshinta,waccan ta lalace ta sauyo musu
wata,tana respecting duk wasu buqatu na
sãahar din,don zata iya cewa tsahon zamanta
a gidan,bata taba jin dadin zama da wani
mutum a gidan ba kamarta
"'Barka da dawowa" baaba ramatu ta fadi tana
duban labiba
"Yaushe akayi baquwa a gidan nan?" Ta jefa mata tambayar ba tare data amsa marabar ta
ba
"Ba baquwa bace,kawai ita ke kula da fadeela
yanzun" a take fuskar labiban ta washe,ta saki
garamar dariya.
"A'ah ramatu,kice nanny ce kawai,basai kin
wahalar da harshenki ba" tayi furucin dukka
a kunnen säahar data qaraso gurin hannunta
dauke da gogaggen hijabin fadeela,cikin
wadanda ta dinko mata da kudinta,saboda
tazo ta risketa bata da jiba ko daya,sai wani
fingilalle V shape na uniform dinta.
Hada idanu sukayi da labiban,sai sauran
maganar ta magale mata a magoshi,ta mige
daga zaman da tayi tana fadin
"Zan jira mommy a sassanta, fadeela enjoy
your new nanny" saita dan daafa kan
fadeelan ta soma takawa tana barin falon.
Ran baaba ramatu ba dadi ta ajjiye
humidifier din,tasan halin kowa a gidan,don
kusan kowa a gabanta yayi girmansa, ta samu
guri ta zauna lokacin da sãahar ke sanyawa
fadeela hijab din nata,daga can qasan
zuciyarta tana fassara kallon da kalaman labiba. Ta fahimci ma'anarsu fes,to amma abinda ya bata mamaki daga haduwar farko ko maganar farko babu a tsakaninsu me ya haifar da wannan matsanancin kishin cikin qwayar idanunta?
"Wannan itace labiba, kuma za'a iya cewa ita din ganwa ce ga mahaifin fadeela,wato
'yar matar babansa ce,tana da wasu halaye marasa kyau wani lokacin,sai kinyi haquri da ita" a nutse ta daga kai ta kalli baaba ramatu,saita saki kyakkyawar murmushin nan nata da ba kasafai take yinsa ba,ta taka tana debo litattafansu
"Karki damu baaba ramatu,haquri da ita bai zama dole ba,tunda bani da case da ita" jinjina kai baaba ramatu tayi,tasan sarai tana da kawaici da kuma sanyin hali,hakanan bata da kwaramniya ko hayaniya,amma labiban fa?,tayi imanin koda bata shiga gonarta ba ita zata shiga tata,saidai fatan Allah ya kiyaye.
*HUGUMA*
*_TABARMAR KASHI_**
Page 63
Sasai wuyanta ke cike da wani qatoton abu,sashen hajiya qaraman taso wucewa amma saita kasa,ta samu kujera ta zauna a nan farfajiyar gidan tana jan numfashi tana fesarwa,ba abinda ke gilma mata cikin idanunta sai kyakkyawar surarta,kamewarta da uban kwarjin da zai hana ta takata yadda taso. Ta yaya zaman wannan cikin gidan zai yiwu?,kuma a matsayin me kula da halittar da toufeeq yafiso duk duniya fiye da komai da kowa?,ta yaya zata bari su dinga gwama numfashi tare dashi?,anya idanun hajiya garama ba rufewa yayi ba kuwa harta amshi wannan surar a mazaunin nanny?.
Qafa daya kan daya tana kadata makeken gate din gidan dake da rassa biyu daya daga cikin reshen(enter) wato shigowa ya bude,ta zubawa gun idanu tana fatan hajiya qarama dince ta dawo. Ita dince kuwa,bata iya haqurin jumurin tsaiwar motar bama ta miqe ta bi bayan motar har zuwa parking lot na gidan,dai dai sanda motar ke tsaiwa,tasa hannu ya bude seat din baya wanda tasan a nan hajiya qarama din ke zama driver yana tuqata,ta shiga ta zauna idanunta akan hajiyan dake amsa waya da dukka hankalinta
"Nooo. karki damu MY BABY,duka duka watannin guda nawa ne? ki kwantar da hankalinki ki kammala karatunki,na miki algawarin duk lokacin da nazo bikin yayeku dake din zan taho,na miki wannan algawarin" girjin labiba ne ya buga,a duk sanda taji tana waya da BABY din,sai ta samu fargaba irin wannan,sunan da ita kanta me sunan ba qaramin barazana bane ga kunnuwanta da rayuwarta
"Alright.....kada ki damu da wannan,ki maida hankali kiyi karatu sosai ki fita da result din da yafi qarfin raini... okay,bye,i love you" saita katse wayar murmushi me kama da dariya kwance akan fuskarta,soyayyarta tana sake ratsata,burinta a kanta yana sake hauhawa,lokaci kawai take jira,kuma mutuwa ce kadai zata shiga tsakaninta da cikar wannan burin nata
"'Ya akayi labiba?" Ta waiwaya gareta bayan ta saka wayar a jakarta, numfashi ta ja ta hadiye yawu
"Mommy, nazo na samu andauki wata me kama da aljanu wai a mazaunin nanny"
"Shine me?" Tavi tambayar hankalinta kwance
*****K'arfe biyar da wasu yan mintuna na yammacin ranar ne,dai dai sanda madaidaiciyar motar me kyau ke shigowa cikin gidan,wanda da shigowarta da isowar masu aikin gidan duka duka bazaiyi minti biyu ba,cikin gaggawa kowanne ya iso,saboda sanin mamallakiyar motar,kowa yana gudun tsira da mutuncinsa.
Bude murfin motar tayi,sannan ta qwalawa daya daga cikinsu kira,matsowa tayi da gaggawa,bakinta dake tauna chewing gum ta motsa
"Daukarmin hand bag dita"
"Tom" ta fada tana buda daya side din da jakar take ta dauka ta riqe
"Kai jama'a,mutum ba uban kowa ba sai shegen ji da kai da izzar banza" tayi gorafi gasa qasa,saidai ya fidda sautin gunaguni
"Me kike cewa?" Labiba ta tambaya taba juyowa,murmushi tadan saki a rikice
"Bab.....babu komai,cewa nayi maraba da dawowa" bata sake cewa komai ba ta fita a motartabar musu aikin kashewa da rufeta hadi da rigo mata key din. Cikin jin kai take takawa,sanye da wani skinny jeans da yabi jikinta sosai ya lafe, kamar a jikin nata aka dinkashi,manyan mazaunanta da suke da wani irin dan banzan tsini sun fita sosai,saidai kuma shafaffen qirjinta dake boye a t shirt din jikinta ya kawo cikas waien cikar adon da akesonyi da bayyana abinda akeson a bayyana din. Kitson attache ne a kanta daya zuba har gadon baya,ya bullo da qasan gantalelallen mayafin data yane kanta dashi wanda iyakarsa wuyanta.
Har ta doshi sassan hajiya qarama suka shaida mata ta fita, amma ba nisa tayi ba,saita sauya akalarta ta wuce sassan fadeela,tanason ta saba da yarinyar,to amma matsalar ita batasan yadda zata shawo kanta su shaqu ba.
Dai dai lokacin da sãahar ke zaune a madaidaicin falonsu na biyu,suna zaune qasan carfet ita da fadeelan, ita tana cin abinci sãahar din na monitoring dinta,a daya bangaren tana duba homeworks din da aka basu ranar a makaranta.
Sanye take da brown din chiffon gown budaddiya sosai,sai kanta data yafawa vail na plain chiffon din shima brown da bai garasa na jikin rigar haske ba, kyakkyawar fuskarta tayi fresh,tes take fatarta na nan da glowing dinta,babu digon ko tabo ballantana qurji,pink lips dinta sai shegin lips balm sukeyi,zara zara yatsunta take sanyawa tana buda book din page by page tana ganin performance din fadeelan a homeworks dinta na baya.
Sau biyu tana buda baki da niyyar yin magana tana dora mata yatsa akan lips tace
"Shshshsh" tasan tanason yin Santi ne akan abincin da takeci, wanda säahar dince yau ta dafa. A karo na uku data hanata saita langabar da kai
"Please aunty ki barni nace wani abu mana" yadda tayi maganar yayi masifar baiwa sãahar dariya,saita rufe littafin tana murmushi idanunta akan fadeela
"Say it fadee"
"Wallahi anty ban tabacin abinci me dadin wannan ba,kamar daga aljanna aka kawosa" ba shiri dariya sosai ta kubcewa saahar,saita miga hannu ta dauki pillow ta saka mata daga gefanta
"'Bari na tareki kada santi yasa ki fadi" dariya itama ta saki sukaci gaba da yi tare
"Please aunty nanny,zaki ci gaba da dafamin abinci?,harda wanda zanje school dashi don
Allah,nasan abincina sai yafi na kowa dadi" idanu ta lumshe tana gyada kai,a yadda takejin fadeela kamar jininta babu hidimar da bazata ivayi mata ba
"Alright,amma idan satin nan ya wuce baki gama haddace suratul a'alah ba,to zan daina,kin yarda?"
"'Na yarda aunty,nayi algawarin jibi zan gama" ido ta ya fidda tana dubanta da mamaki
"Really?" Kai ta jijiga mata alamun da gaske take.
"Hi fadeela" muryar labiba dake tsaye a kansu ta ratsa kunnuwansu,dukkaninsu babu wanda yasan da shigowarta bare wanzuwarta a gurin.
Daga kansu sukayi kusan lokaci guda suka
dubeta,dai dai lokacin idanunsu suka gauraya
da juna ita da sãahar.
Dan ja baya kadan tayi cikin yanayin dake
nuna qaramar razana
"Ya salam" ta furta can gasan ranta,tana
hadiye wani abu me tauri a maqoshinta,a
ina aka samo wannan cikin gidan?" Ta yiwa
kanta tambayar da batasan amsarta ba,zataso
ta jefa tambayar ga baquwar fuskar,amma
idanunta zuwa fuskarta suna fidda wani irin
kwarini.
Sãahar ce ta fara janye idanun nata daga
kanta,ranta yana dan baci da yadda ta riskesu
gatsau kai tsaye tayi musu kuma tsaye a
ka,saita maida idanunta ga duba littafin
hannun nata ba tare data sake dagowa ta
dubeta ba,saidai a jikinta tana jin kamar tasan
fuskar,kamar ta taba ganinta a wani waje.
Tana jinta ta isa gaban fadeela ta zauna
tana ta janta da surutu,lokaci lokaci idanunta
suna satar kallon sãahar,wadda bata sake
duban sashenta ba,koda ace suna da dabi ar
yahudawa,a qalla tunda musulmi ne su tay!
musu sallama sanda ta riskesu
"Na gama anty" fadeela ta fada bayan ta ajiye
gorar ruwan hannunta
"Good bari na dauko miki hijab,qur ani zamu
fara yi" saita kife littafin ta mige zuwa dakin
fadeelan. Kallo labiba ta bita dashi hankalinta yana tashi, ko ita da take mace ta tabbatar
ta kuma yaqini hakanan ta sallama wannan
din ta cika mace wani abu me cakude da
kishi da tashin hankalin wanzuwarta a gidan
yazo yayi mata tsaye,sai ta maida dubanta ga
fadeela dake qoqarin dauke plate din da taga gama cin abincin tana tattare inda ta bata da
tissue,abinda bata taba gani yarinyar tayi ba "Wacece wannan uktie?" Duban labiban kawai
tayi,da yake itama miskilar kanta ce,kafin tace
komai baaba ramatu ta shigo falon,hannunta
dauke da humidifier da tasan sãahar na
yawan ajjiyeta a gurin saboda tsananin son
qamshinta,waccan ta lalace ta sauyo musu
wata,tana respecting duk wasu buqatu na
sãahar din,don zata iya cewa tsahon zamanta
a gidan,bata taba jin dadin zama da wani
mutum a gidan ba kamarta
"'Barka da dawowa" baaba ramatu ta fadi tana
duban labiba
"Yaushe akayi baquwa a gidan nan?" Ta jefa mata tambayar ba tare data amsa marabar ta
ba
"Ba baquwa bace,kawai ita ke kula da fadeela
yanzun" a take fuskar labiban ta washe,ta saki
garamar dariya.
"A'ah ramatu,kice nanny ce kawai,basai kin
wahalar da harshenki ba" tayi furucin dukka
a kunnen säahar data qaraso gurin hannunta
dauke da gogaggen hijabin fadeela,cikin
wadanda ta dinko mata da kudinta,saboda
tazo ta risketa bata da jiba ko daya,sai wani
fingilalle V shape na uniform dinta.
Hada idanu sukayi da labiban,sai sauran
maganar ta magale mata a magoshi,ta mige
daga zaman da tayi tana fadin
"Zan jira mommy a sassanta, fadeela enjoy
your new nanny" saita dan daafa kan
fadeelan ta soma takawa tana barin falon.
Ran baaba ramatu ba dadi ta ajjiye
humidifier din,tasan halin kowa a gidan,don
kusan kowa a gabanta yayi girmansa, ta samu
guri ta zauna lokacin da sãahar ke sanyawa
fadeela hijab din nata,daga can qasan
zuciyarta tana fassara kallon da kalaman labiba. Ta fahimci ma'anarsu fes,to amma abinda ya bata mamaki daga haduwar farko ko maganar farko babu a tsakaninsu me ya haifar da wannan matsanancin kishin cikin qwayar idanunta?
"Wannan itace labiba, kuma za'a iya cewa ita din ganwa ce ga mahaifin fadeela,wato
'yar matar babansa ce,tana da wasu halaye marasa kyau wani lokacin,sai kinyi haquri da ita" a nutse ta daga kai ta kalli baaba ramatu,saita saki kyakkyawar murmushin nan nata da ba kasafai take yinsa ba,ta taka tana debo litattafansu
"Karki damu baaba ramatu,haquri da ita bai zama dole ba,tunda bani da case da ita" jinjina kai baaba ramatu tayi,tasan sarai tana da kawaici da kuma sanyin hali,hakanan bata da kwaramniya ko hayaniya,amma labiban fa?,tayi imanin koda bata shiga gonarta ba ita zata shiga tata,saidai fatan Allah ya kiyaye.
*HUGUMA*
*_TABARMAR KASHI_**
Page 63
Sasai wuyanta ke cike da wani qatoton abu,sashen hajiya qaraman taso wucewa amma saita kasa,ta samu kujera ta zauna a nan farfajiyar gidan tana jan numfashi tana fesarwa,ba abinda ke gilma mata cikin idanunta sai kyakkyawar surarta,kamewarta da uban kwarjin da zai hana ta takata yadda taso. Ta yaya zaman wannan cikin gidan zai yiwu?,kuma a matsayin me kula da halittar da toufeeq yafiso duk duniya fiye da komai da kowa?,ta yaya zata bari su dinga gwama numfashi tare dashi?,anya idanun hajiya garama ba rufewa yayi ba kuwa harta amshi wannan surar a mazaunin nanny?.
Qafa daya kan daya tana kadata makeken gate din gidan dake da rassa biyu daya daga cikin reshen(enter) wato shigowa ya bude,ta zubawa gun idanu tana fatan hajiya qarama dince ta dawo. Ita dince kuwa,bata iya haqurin jumurin tsaiwar motar bama ta miqe ta bi bayan motar har zuwa parking lot na gidan,dai dai sanda motar ke tsaiwa,tasa hannu ya bude seat din baya wanda tasan a nan hajiya qarama din ke zama driver yana tuqata,ta shiga ta zauna idanunta akan hajiyan dake amsa waya da dukka hankalinta
"Nooo. karki damu MY BABY,duka duka watannin guda nawa ne? ki kwantar da hankalinki ki kammala karatunki,na miki algawarin duk lokacin da nazo bikin yayeku dake din zan taho,na miki wannan algawarin" girjin labiba ne ya buga,a duk sanda taji tana waya da BABY din,sai ta samu fargaba irin wannan,sunan da ita kanta me sunan ba qaramin barazana bane ga kunnuwanta da rayuwarta
"Alright.....kada ki damu da wannan,ki maida hankali kiyi karatu sosai ki fita da result din da yafi qarfin raini... okay,bye,i love you" saita katse wayar murmushi me kama da dariya kwance akan fuskarta,soyayyarta tana sake ratsata,burinta a kanta yana sake hauhawa,lokaci kawai take jira,kuma mutuwa ce kadai zata shiga tsakaninta da cikar wannan burin nata
"'Ya akayi labiba?" Ta waiwaya gareta bayan ta saka wayar a jakarta, numfashi ta ja ta hadiye yawu
"Mommy, nazo na samu andauki wata me kama da aljanu wai a mazaunin nanny"
"Shine me?" Tavi tambayar hankalinta kwance