← Book details Tabarmar Kashi Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 10 OF 171

Sashe 10

Tabarmar Kashi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Aje wayar kawai tayi gefe ba tare data bi bayan afifa ba,tasan zata gama fushinta ta huce ne,infact ma a yanzu hutawa takesonyi,idan ta tashi koma meye taji dashi. Ta sauke ajiyar zuciya ta kwanta sosai a tsagin hannun damanta kamar yadda ta saba,ta lumshe manyan idanunta a hankali,eyelashes dinta masu tsaho da baqi suka yiwa kyawawan tsagar idanunta rumfa.

*********K'arfe takwas da mintuna na dare agogon dake maqale a bangon falon ya nuna,farheen na tsaye daga dining area tana hadawa yaa muhyi fruit salad,daga qasan falon kuma,can saman qawatacce kuma lallausan carfet din da aka yiwa Parlor din ado dashi,sãahar ce zaune,sanye cikin wata farar long sleeve shirt turtle neck da aka yiwa adon flowers qananu daga wajen qirjin da pink flowers,kanta babu dankwali sai band data matse gashinta daketa qyalli yana daukar idanu,duk da cewa dare ne,amma hakan bazai hanaka jin sassanyan qamshin da jikinta yake fitarwa ba,wanda ya riga ya gama runewa a jikin fatarta komai gumi da zafi,fuskarta tayi wani fresh farinta me surkin ja ya bayyana sosai,duk kuwa da cewa ko dan kunne babu a kunnuwanta amma hakan baya hanaka hango baiwar kyan da Allah ya bata. Aleena na zaune tsakiyar qafafunta,khalifa kuma yana zaune daga gefanta tana masa homework. Lokaci lokaci farheen na daga kai tana dubansu sannan taci gaba da aikinta,yanayin yadda sãahar din ke matuqar son yara zai baka mamaki,a haka a ido sam batayi kama da meson yara ba.

Sallamar yaa muhyi cikin Parlor din ita ta tashi karatun,khalipha yayi gurinsa da gudu aleena ta fara daga masa hannu tana bangale masa da dariya,dole ya qaraso ya dauketa,ya zauna saman kujera yana ji dasu duka su biyun,da khalipha dake surutu,da aleena dake gwaranci.

"sannu da zuwa yaa" sãahar ta fada tana miqewa tsaye da zummar barin falon. Waiwayowa yayi yana dan karkata hankalinsa a kanta

"Barkanki khadijatou"

"Ya aikin?" Ta sake fada tana duqawa ta dauki wayarta

"Alhamdulillah.....zan shiga ciki yanzu zan watsa ruwa,after one hour ki sameni"

"Okay" ta fada tana jinjina kai,sai ta juya ta wuce zuwa dakinta tana jiyo 'yar hayaniyarsu da yaran.

Saman sofa bed ta zauna tana gwada kiran afifa wadda ta dauki fushi da ita,bugu biyu ta daga

"Me kika kirani kice min?"

"Relax mana" ta fada very calm

"Dadina dake hayaniya sa saurin daukan temper"

"Eheeen,ya muke dake?" Maganar ta saka sãahar sakin qaramin murmushi saman kyakkyawar fuskarta,tasan magana ce kawai afifa keson gaya mata

"Koma ya muke din ba wani abu bane,nayi miki laifi kiyi haquri,am sorry" ajiyar zuciya afifa ta sauke,sãahar din tana da wata baiwa cikin halaye da dabi'unta,tasan dukka hanyar da zata zauna da kowa da zamantakewa ya hadasu,hakanan tasan hanya mafi sauqi na sauke mutum daga kan fishinsa nan take

"Is ok"

"Everything will be alright......but for now please,ki manta da issue dinsa.... mahmud ko?" Ta fada calmly. Idanu afifa ta fidda kamar tana gabanta

"Ya salam...... you can't remember his name sãahar,Allahu yahdik" ta qarashe maganar tana dafe goshinta

"Whatever afifa,i need space don Allah,ki dakatar dashi"

"Zan gwada"

"Zaki gwada..... like how?"

"You are more than you think,ya dauki al'amarinki da girma sãahar,ba lallai don na mishi bayani ya fahimta ba"

"Ya rage nashi" ta fada very careless tana dage kafadunta. Ita gaba daya al'amarin maza baya burgeta sam,ko meye zasuyi,shin meye bata gani ba?,wanne hali nasu ne yayi mata saura?,hirar gaba daya bata burgeta don haka ta sako wani topic din daban.

Sai da suka cinye awa dayan da yaa muhyi din ya bata sannan ta ajjiye wayar,ta shiga bandaki ta daura alwala,ta dawo ta fidda abaya ta dora saman rigar jikinta,ta yane kanta da mayafin abayar.

Duk da agurguje ba tare kuma da nufin tayi kwalliya ba ta shirya,amma kyanta ya fita sosai,zakayi tsammanin zama tayi tayi wata kwalliya ta musamman,tana da baiwar komai ta raɓa a jikinta yi mata kyau yakeyi.

Cikin takardu ta sameshi,gefansa ta zauna tana wasa da yatsun aleena dake zaune jingine da pillow don kada takai ga faduwa,ya dubeta yana ture takardun gabansa,ya zaro wani file mara nauyi,saidai ya banbanta da dukka takardun wajen,bangonsa fari ne tas,anyi masa ado da zaiba,kallo daya zakasan na musamman ne ko kuma yana dauke da wasu muhimman bayanai.

Budawa yayi daya bayan daya yana dan dubawa cikin nazari,daga bangon farko har zuwa bangon qarshe,sannan ya maidashi ya rufe,ya ajjiye shi a tsakaninsu yana kiran sunanta idanunsa a kanta

"Na'am yaaa"

"Kiyi haquri na miki laifi,na karba takardun amsar aiki daga MT GROUP OF COMPANY,ba tare dana jira jin hukuncin da kika yanke ba,am sorry na miki katsalandan" kanta ta daga a hankali,ta sauke dubanta ga yaa muhyi din tana jin wani abu me nauyi yana sauka saman kanta zuwa qirjinta,wani abun kuma da bata tantance meye ba yana mamaye qirjinta,maganganun nasa sunyi mata nauyi qwarai,saboda bata zaci jinsu a wannan lokacin ba,saidai abu daya da take tunawa,yaa muhyi din yafi qarfin komai a wajenta,ta tabbatar shi din masoyi ne me qaunar dukka wani abu da zai baiwa zuciya da rayuwarta farinciki,bijirewa saka hannun karbar aikin dai dai yake da ta tozartashi

"Ga file din ki wuce dashi daki,ki duba sosai ki saka hannu a duk inda ya dace,amma kafin sannan,har yanzu kina da chance,idan kikaji baki nutsu ba ko baki gamsu ba,kada ki damu ki dawo da dukka takardun" ya fada yana miqa mata su.

Hannu ta miqa itama ta karba,sannan ta miqe cikin sanyi da mutuwar jiki,kamar wadda aka bibbigewa gwiwoyi ta doshi qofar fita,yaa muhyi din ya rakata da kallo har sai data bacewa ganinsa. Kansa ya jinjina,cikin ransa yana fatan saituwar al'amuranta,yana jin kamar ya runtse idanu ya bude yaga sãahar dinsu ta baya ta dawo,ba wannan sãahar din da duk wani buri na rayuwa ya fice daga rayuwarta sa tunaninta ba da mugun gudun tsiya,sanadin wani abu daya shude shekara biyu baya.

Kamar wani abun tsoro haka ta ajjiye file din saman madubi,ta koma gefan gado ta zauna,ta dafe gefe da gefe da dukka tafukan hannayenta tana kallon file din daga inda take zaune tamkar wadda ke nazarin karatu daga allon computer,tako ina tana jin sanyin jiki,mutuwar jiki dama rashin karsashi,saidai ko daya cikin istikharar data sanya a gaba takeyi bataji a ranta ta fasa aikin kota watsar da tayin yaa muhyi ba.

FURAR DANKO
Billyn Abdul

-ZAFIN KAI
Mamuhgee

-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma

-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo

Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400

Pay at👇

1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim
Sai katura shedar biyanka anan👇

09032345899

Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070

VIP🔥💯
Zafin kai 3k
Furar danko 3k
Tabarmar kashi 3k
Bakon munafuki 3k

*Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din*

+22799643131

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*

*THANKS FOR CHOOSING US*🥰

Zafafa🫶🔥

[8/4, 1:54 PM] KYAUTA: *H U G U M A*

_*TABARMAR ƘASHI*_💔

*Arewabooks: huguma*
https://arewabooks.com/u/huguma

Page 09

Kwana file din yayi a nan,bayan sallahr asuba ta kammala azkar dinta ta jawoshi tana zaune daga saman abun sallarta,ta buda a hankali ta fara karantawa kamar yadda yaa muhyi yace tayi din.

Very interesting,komai na kamfanin a tsare yake cikin wani tsari mai burgewa,banda batajin son aikin cikin ruhinta zata iya cewa company din ya burgeta,kuma kamar tana da gudunmawar da zata iya bayarwa tabbas gurin saitashi. Tsayawa tayi cak da biron dake hannunta bayan ta kammala signing tana duban sunan CEO din dake rubuce cikin ruwan gold daga gefen takardar MUHAMMAD TAUFEEQ. Zame hannunta tayi a hankali daga saman takardar tana kallon sunan,a hankali tunaninta ya koma can baya,sai yanzun ta tuna yaa muhyi ya gaya mata zasuyi aiki ne tare da yaronsa

"Jaffal qalam" ta fada can qasan ranta tana maida file din ta rufe,ta riga ta saka hannu,tabbas data janye,batason a kaita sashen da zatayi aiki tare da kowa,amma ya zatayi?,yaa muhyi ya riga ya daureta da jijiyar jikinta.

A gaggauce ta isa parking lot na gidan sanda yake shirin shiga motarsa,ya dakata ya waiwayo yana dubanta tana dan haki saboda saurin da takeyi,file din ta miqa masa

"Ya akayi?" Ya tambayeta tun kafin ya buda bayan ya karba

"Na cike yaaya" ta fada tana langabe kanta,sosai murmushi ya wadaci fuskarsa,alamun maganar tayi masa dadi sosai,ya fara buda file din ya duba sannan ya dora idonsa a kanta

"Thank you sisi,na gode da baki bani kunya ba baki kuma watsa min qasa a ido ba" yadda yayi appreciating nata saita kasa neman komai daga wajensa,ta saki qaramin murmushi ta gyada kai kawai

"Next week on Monday zaki fara shiga office dinki,komai da kike buqata kiyimin magana baki da matsalarsa in sha Allah,already shi partner din naki ya fara shiga cikin wannan satin" yana maganar yana danne danne a wayarsa. Daga kai yayi

"Na saka miki kudi ko zaki buqaci yin siyayya"

"Oh no yaaya,ina da kudi a account dina fa,sannan last week yaa Saifullahi ya sakamin shima"

"I know,hal jaza'ul ihsani illal ihsan" kai ta jijjiga a hankali,sai taji cikin ranta tana jin dadin abinda tayi masan,tunda shima har qasan zuciya da fuskarsa abun ya faranta masa.

Ciki ta koma ta fara shiryawa don wucewa gida,already dama tana da intention na zuwa yin shopping din,akwai kayayyakin amfaninta da sukayi low.

**********Lafiyayyun motocine qirar range rover baqaqe sidik ke wulwula gudu saman kwalta wata nabin wata har guda hudu a jere. Tun daga inda suka taho wato cikin filin sauka da tashin jiragen saman malam aminu kano wato aminu kano international airport har zuwa cikin rukunin gidajen dake unguwar nasarawa GRA,duk inda suka gifta daukan idanu da kuma hankulan al'umma sukeyi tare da saka kokwanton cikin zukatan al'umma na tunanin mamallakan motocin da babu cikakkiyar number a jiki kamar ta kowanne abun hawa,sai wasu qididdigaggun haruffa da kuma lambobi da sukazo a jere data sauran kowacce mota dake bin 'yaruwarta.
Chapter 10 · 0% Book details