Sashe 50
Tabarmar Kashi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"It seems like anyi disconnecting duk wani details naki daga Account din,to amma kuma ina doubting,saboda indai za'a yi hakan saida saninki da yardarki,anyway,gobe zan shiga bankin,zan duba miki komai in sha Allah" godiya tayi masa ta sauke wayar,duk da cewa wani bangare na zuciyarta cike yake da mamaki,amma wani sashen kuma cikin tantama yake,kanta ya kulle dason gane gaskiya da kuma meye dai dai?,ganin zata batawa kanta lokaci saita ajiye komai,don bata da tabbacin gaskiyar ko rashinta akan duk abinda zuciyarta zata raya mata,taci gaba da cin samosa dinta.
Takai plates din kitchen kenan ta fito taji ana knocking,ta fasa zaman da tayi niyya,ta isa qofar falon ta budeta.
Mamaki ne sosai ya kamata ganin raihanatu,don tsahon aurensu da adam batajin yarinyar tazo gidan yakai sau uku,duk da yadda takeson yarinyar saboda hankali da nutsuwarta,da kuma yadda take girmamata.
*H U G U M A*
*_TABARMAR ƘASHI_*💔
https://arewabooks.com/u/huguma
Page 44
Ta taba yiwa momee din complain akan hakan,tabe baki tayi
"Na rabaki da wannan,wannan me baqin halin,sumumu kasau" murmushi ta danyi kadan,can qasan zuciyarta cike da mamaki,bata taba ganin wani abu na rashin kyautawa raihanatu tayi ba,duk tsahon zuwanta gidan kullum cikin hidima takewa momee,bata tana tsallake umarninta,tausayi da nutsuwarta yake qarawa sãahar qaunarta,wannan ya sanya koda kayan bayarwa zata fitar,raihanan take baiwa,ko yanzu kayan jikinta na sãahar dinne,don ba kasafai momee ke mata dinki ba,takance tana yi mata, yarinyar ce kamar ba mace ba,batason kwalliya bata sawa, sãahar dai bata taba ganinta cikin qazanta ba,ko yaushe fess take da tsaftatattun kaya.
"Shigo ciki mana" sãahar ta fada ganin wani abu me kama da tsoro a fuskar raihana dake tsaye daga bakin qofa,hannunta dauke da ledar dake nuna aikenta momee tayi ta biyo nan,sau biyu tana waigawa tana kallon bayanta kafin ta fado falon.
A qasa ta zauna, sãahar ta tasheta tace ta koma saman kujera
"Ya gida yasu momee?" Ta fara tambayarta ganin har yanzu batace komai ba tana nufar qofar kitchen,hannunta taji an riqo,saita juyo,fuskarta ta sauka akan raihanatu. K'walla ta gani cike fal da idanun nata,yanayinta ya sake sauyawa qwarai,kowanne lokaci zata iya sakin kuka
"Ki zauna anty don Allah,magana nakeson zamuyi,gida nakeson komawa da sauri,kada momee ta fahimci na biya wani gurin" kai ta jinjina,saita dawo da baya ta zauna dab da raihanatu ta zuba mata ido,jikinta yayi wani mugun sanyi da kuma mutuwa,wanda batasan dalilin hakan ba,sai taji gabanta yana faduwa kadan kadan lokacin da taga raihana ta sad da kanta qasa,qwalla tana diga.
Tsahon zamanta da yarinyar bata taba zama irin haka da ita ba,zuciyarta ta shiga fargaba da taraddadi,kafin tace wani abu raihanatu cikin rawar murya ta fara magana
"Kafin rasuwar mamana ta gayamin duniya a yanzu cike take da mutane azzalumai,marasa amana,marasa kuma saka alkhairi da alkhairi,na sake tabbatarwa a yanzu akan yayar mahaifiyata,na kuma sake tabbatarwa a yanzu a zamanki da yaya adam da momee. Bazan taba nutsuwa ba,bazan taba samun kwanciyar hankali ba idan har na bari akayo miki wannan zaluncin,bayan kunnuwa na sunji amma na gagara gaya miki" sai tayi shuru hawayen naci gaba da zuba tana hadiyar zuciya
"Na baro yaya adam a gida yanzu suna shirya yadda zasu qarasa murqushe dukiyarki" ta tsaya da zancan tana kallon sãahar. Ido sosai sãahar din ta zuba mata,maganar tana neman matsugunni a kunnuwanta sannan ta isa ga kwanyarta,tsahon wasu sakanni sannan ta danyi murmushi tace
"Ba murqushewa zaiyi ba ba raihanatu,nina dauka da kaina na bashi,ba bangula guda biyu ba?" Kai ta girgiza alamun a'ah
"Duk wata dukiya dake hannunki da wadda take hannunsa,bama wannan ba anty.....kinsan yaa adam yana da wata matar bayan ke?" Wani irin mugun hautsinawa kanta yayi,mararta kuma ta damqe guri guda kamar curarren alkaki,amai ya taso masa me bala'in zafi tare da tashin hankalin daya daki zuciyarta,saita miqe da mugun gudu ta nufi kitchen wanda shine yafi kusa da ita.
Sosai ta dinga kwarara amai,har sai dan samosa da madarar da tasha babu jimawa suka fice gaba daya,a sannan raihanatu tana tsaye a bayanta tanayi mata sannu cikin tashin hankali,a wahalce sãahar ta gama kuskure bakinta tana maida numfashi ta juyo tana duban raihanatu data gama tsurewa gaba daya,zuciyarta kuma ta fara shiga tsoro da nadamar abinda yasa ta gaya mata wannan babban sirrin
"Kiyi haquri anty,ban gaya miki don na daga hankalinki ba,na gaya miki ne saboda kina da kirki,ke din mutuniyar arziqi ce,barin wasu mutane masu mummunar zuciya su cutar daku babban zunubi ne" hannu ta dora a kafadar raihanatu
"Karki damu raihanatu,jikina yana bani da dukkan gaskiyarki kikayi maganar nan" saita jawo yarinyar jikinta tana jin zuciyarta tana karyewa,duk da a yanzu tana gayawa kanta ba rauni take buqata ba,tana buqatar qarfin hali da dauriya me tarin yawa don ta gano ainihin gaskiyar maganar,duk da wani sashe na zuciyar yana mata tantama,anya adam?,adam da momee?,zasu aikata?.
"Na gode raihanatu" ta fada sannan ta janyeta daga jikinta,hannuwan sãahar duka biyun raihanatu ta kamo ta riqe,abinda bata taba yi ba,cikin rawar murya tace
"Amma don Allah anty kiyimin alqawarin ba wanda zaisan ni na gaya miki maganar nan"
"Komai rintsi komai tsanani raihanatu,na miki wannan alqawarin" tana nan tsaye kamar statue har raihanatu ta fice a gidan. Gaba daya ji tayi kamar an yashe komai daga cikin kanta,ta rasa dukkan wata idea da matakin daya kamata ta fara dauka,babu abinda yake mata amsa kuwwa a kunne sai YAYA ADAM YANA DA WATA MATAR BAYAN KE,ta yaya hakan zata kasance?,ta yaya hakan zata yiwu?,bayan ko yaushe suna tare da dam?,shiba matafiyi ba ba komai ba bare tace yayi amfani da wannan damar yayi auren a wani garin bata sani ba?,sai ta sulale ta zauna a wajen,tasa hannunta guda biyun ta dafe kanta wanda taji yana sara mata,kanta taji yana cushewa,zai buga da kalar tunanin da take takurawa kanta dashi,saita fara karanto sunayen Allah,da haka ta samu taja jikinta ta koma falon ta zube saman kujera.
Tunda ta kwanta bata tashi ba sai da akayi sallar la'asar,kana kallonta zakace bata da lafiya,dab da kiran magariba adam ya shigo,tana daga kwancen ta daga kanta tana kallonsa,fuskarsa cike da walwala da wani irin nishadi wanda batasan daga ina ya samo asali ba,saita samu kanta da qarewa fuskarka kallo da kyau,zuciyarta tana nazartarsa,nazarin da bata taba yinsa a kan adam ba.
Ganinta a kwance yasa ya sauke hannayensa daya ware mata yana jiran ta shigo ya rungumeta,duka sai walwalarsa ta koma,ya tako da sassarfa cikin nuna damuwa me yawa ya iso gareta
"Heart,what happened?" Yayi maganar yana dagota zuwa jikinsa
'banajin dadi" ta bashi amsa a taqaice
"What?,kada dai ace a kwance kika wuni?"kai ta sake gyada masa
"Ya salam,me yasa baki kirani ba?,amma baki kyautamin ba, please please karki qara yimin haka,idan wani abu ya sameki fa?" Yayi maganar kamar zai fashe da kuka,sai ya kwantar da ita,ya ciro waya,saiji tayi yana kiran wani likitansa. Drip yasa aka daura mata,wai tafijin qwarin jikinta,ya kasa zaune ya kasa tsaye,bayan fitar likitan ya shiga kitchen ya dora abincin dare,yayi yayi ta fada me takeson ci tace masa babu komai.
Wanzuwarsa a kitchen din ya bata damar sake zurfafa cikin tunaninta,ta dinga hango mode dinsa tun daga shigowarsa gidan kawo yanzu,tarin qauna kulawa da kuma riritawa ce zallah,sai zuciyarta ta cika da kokwanto,amma kuma ta rasa meye yake bata qwarin gwiwa da tabbaci.
Karin ruwan babu abinda ya qara mata,saboda wata irin narkakkiyar damuwa ce dake kwance qasan a zuciya,a haka suka kwana. Washegari tunda wuri ya hada mata breakfast ya shirya yace mata zai fita,amma azahar ko la'asar zai dawo. Har ya fita saita miqe ta bishi,a qofar dakinsa sukaci karo,yasa hannu ya jawo qofar yana kullewa da dan sauri,yayin da idanunsa ke a kanta yana kasheta da murmushi.
"Akwai wani abu ne?,ko kinaso na taho miki da wani abun?" Kai ta girgiza
"A'ah,zan dan fita strolling ne idan na gaji da kwanciyar"
"Ba damuwa,amma ko nasa momee ta kawo miki raihanatu?"kiran sunan kawai yasa gabanta ya fadi,saboda tuna gagarumin abun da muddin ta samu tabbacin afkuwarsa,zai zama sila ta guntulewar alaqar auratayya tsakaninta da adam,duk yadda take da kai, muddin kai din maha'inci ko maciyin amana ne.....to tana shata layi me girma a tsakaninka da ita.
"Ka barta,na danji dadin jikin ai" ta amsa masa.
Kasa komawa dakinta tayi bayan fitarsa,taja jiki ta zauna saman kujera,kamar kuma wadda aka mintsina saita miqe da sauri,kai tsaye ta doshi dakin adam. Tambayar kanta takeyi me zataje tayi a dakin?,tunda ta tabbatar ya rufe dakin a gabanta,kuma bata da sauran spare key da zai bata damar shiga?,amma duk da wannan tunanin sai ta gaza tsaida kanta daga dosar dakin da takeyi.
Sau daya ta murda dakin bawai don tana tantama ko tana da masaniyar bai rufe ba,amma cikin iko da qudurar ubangiji taji ya bude,mamaki ya cikata,ta tsaya tana duban qofar bayan ta bude,ta leqa sai ta fahimci yana sauri ne bai murza key din da kyau ba,lock din bai gama shiga ba ya zare ya dauka ya shige. Sakin wannan tunanin tayi ta wuce dakin da gaggawa.
Cak ta tsaya tana qarewa dakin kallo,tana nazarin ta ina zata fara binciken da zai bata shaida ko tabbacin abinda take zargi?,shikam adam ma bashi da safe irin nata,saboda yasha gaya mata ya yarda da ita. Wani tunani ya fado mata,a dazu da suka shiga dakin taga yanata kaffa kaffa da wardrobe dinsa,tun bata ankara ba har hankalinta yakai kai,amma bata kawo komai a ranta ba ko kadan,saboda tasan zuwa yanzu ya wanke dukkan wani zarginsa a ranta.
Cike da fargaba ta buda wardrobe din,cikin ranta tana addu'ar Allah yasa komai ya zama hasashe ne,Allah yasa komai ya zama tunani ne,muddin ta samu adam da cin amanarta,batasan ta yadda zuciyarta zata iya dauka ba.
Tsaf ta bincike wardrobe din,saidai bataga komai ba,tasa hannu tana shirin rufewa idanunta ya sauka daga can qasanta,wani abu me kama da jaka ta gani a jingine daga can gefe,saita tsugunna ta jawo,jakace baqa mai cike da zips kala kala,tunda take da adam bata taba ganin jakar ba,wannan ya qara mata qaimi da karsashi,ta fara bude zips din,take kudade masu tarin yawa daure cikin kyauraye da kuma takardu masu yawa suka fado.
*H U G U M A*
*_TABARMAR ƘASHI_*💔
https://arewabooks.com/u/huguma
Page 45
Takai plates din kitchen kenan ta fito taji ana knocking,ta fasa zaman da tayi niyya,ta isa qofar falon ta budeta.
Mamaki ne sosai ya kamata ganin raihanatu,don tsahon aurensu da adam batajin yarinyar tazo gidan yakai sau uku,duk da yadda takeson yarinyar saboda hankali da nutsuwarta,da kuma yadda take girmamata.
*H U G U M A*
*_TABARMAR ƘASHI_*💔
https://arewabooks.com/u/huguma
Page 44
Ta taba yiwa momee din complain akan hakan,tabe baki tayi
"Na rabaki da wannan,wannan me baqin halin,sumumu kasau" murmushi ta danyi kadan,can qasan zuciyarta cike da mamaki,bata taba ganin wani abu na rashin kyautawa raihanatu tayi ba,duk tsahon zuwanta gidan kullum cikin hidima takewa momee,bata tana tsallake umarninta,tausayi da nutsuwarta yake qarawa sãahar qaunarta,wannan ya sanya koda kayan bayarwa zata fitar,raihanan take baiwa,ko yanzu kayan jikinta na sãahar dinne,don ba kasafai momee ke mata dinki ba,takance tana yi mata, yarinyar ce kamar ba mace ba,batason kwalliya bata sawa, sãahar dai bata taba ganinta cikin qazanta ba,ko yaushe fess take da tsaftatattun kaya.
"Shigo ciki mana" sãahar ta fada ganin wani abu me kama da tsoro a fuskar raihana dake tsaye daga bakin qofa,hannunta dauke da ledar dake nuna aikenta momee tayi ta biyo nan,sau biyu tana waigawa tana kallon bayanta kafin ta fado falon.
A qasa ta zauna, sãahar ta tasheta tace ta koma saman kujera
"Ya gida yasu momee?" Ta fara tambayarta ganin har yanzu batace komai ba tana nufar qofar kitchen,hannunta taji an riqo,saita juyo,fuskarta ta sauka akan raihanatu. K'walla ta gani cike fal da idanun nata,yanayinta ya sake sauyawa qwarai,kowanne lokaci zata iya sakin kuka
"Ki zauna anty don Allah,magana nakeson zamuyi,gida nakeson komawa da sauri,kada momee ta fahimci na biya wani gurin" kai ta jinjina,saita dawo da baya ta zauna dab da raihanatu ta zuba mata ido,jikinta yayi wani mugun sanyi da kuma mutuwa,wanda batasan dalilin hakan ba,sai taji gabanta yana faduwa kadan kadan lokacin da taga raihana ta sad da kanta qasa,qwalla tana diga.
Tsahon zamanta da yarinyar bata taba zama irin haka da ita ba,zuciyarta ta shiga fargaba da taraddadi,kafin tace wani abu raihanatu cikin rawar murya ta fara magana
"Kafin rasuwar mamana ta gayamin duniya a yanzu cike take da mutane azzalumai,marasa amana,marasa kuma saka alkhairi da alkhairi,na sake tabbatarwa a yanzu akan yayar mahaifiyata,na kuma sake tabbatarwa a yanzu a zamanki da yaya adam da momee. Bazan taba nutsuwa ba,bazan taba samun kwanciyar hankali ba idan har na bari akayo miki wannan zaluncin,bayan kunnuwa na sunji amma na gagara gaya miki" sai tayi shuru hawayen naci gaba da zuba tana hadiyar zuciya
"Na baro yaya adam a gida yanzu suna shirya yadda zasu qarasa murqushe dukiyarki" ta tsaya da zancan tana kallon sãahar. Ido sosai sãahar din ta zuba mata,maganar tana neman matsugunni a kunnuwanta sannan ta isa ga kwanyarta,tsahon wasu sakanni sannan ta danyi murmushi tace
"Ba murqushewa zaiyi ba ba raihanatu,nina dauka da kaina na bashi,ba bangula guda biyu ba?" Kai ta girgiza alamun a'ah
"Duk wata dukiya dake hannunki da wadda take hannunsa,bama wannan ba anty.....kinsan yaa adam yana da wata matar bayan ke?" Wani irin mugun hautsinawa kanta yayi,mararta kuma ta damqe guri guda kamar curarren alkaki,amai ya taso masa me bala'in zafi tare da tashin hankalin daya daki zuciyarta,saita miqe da mugun gudu ta nufi kitchen wanda shine yafi kusa da ita.
Sosai ta dinga kwarara amai,har sai dan samosa da madarar da tasha babu jimawa suka fice gaba daya,a sannan raihanatu tana tsaye a bayanta tanayi mata sannu cikin tashin hankali,a wahalce sãahar ta gama kuskure bakinta tana maida numfashi ta juyo tana duban raihanatu data gama tsurewa gaba daya,zuciyarta kuma ta fara shiga tsoro da nadamar abinda yasa ta gaya mata wannan babban sirrin
"Kiyi haquri anty,ban gaya miki don na daga hankalinki ba,na gaya miki ne saboda kina da kirki,ke din mutuniyar arziqi ce,barin wasu mutane masu mummunar zuciya su cutar daku babban zunubi ne" hannu ta dora a kafadar raihanatu
"Karki damu raihanatu,jikina yana bani da dukkan gaskiyarki kikayi maganar nan" saita jawo yarinyar jikinta tana jin zuciyarta tana karyewa,duk da a yanzu tana gayawa kanta ba rauni take buqata ba,tana buqatar qarfin hali da dauriya me tarin yawa don ta gano ainihin gaskiyar maganar,duk da wani sashe na zuciyar yana mata tantama,anya adam?,adam da momee?,zasu aikata?.
"Na gode raihanatu" ta fada sannan ta janyeta daga jikinta,hannuwan sãahar duka biyun raihanatu ta kamo ta riqe,abinda bata taba yi ba,cikin rawar murya tace
"Amma don Allah anty kiyimin alqawarin ba wanda zaisan ni na gaya miki maganar nan"
"Komai rintsi komai tsanani raihanatu,na miki wannan alqawarin" tana nan tsaye kamar statue har raihanatu ta fice a gidan. Gaba daya ji tayi kamar an yashe komai daga cikin kanta,ta rasa dukkan wata idea da matakin daya kamata ta fara dauka,babu abinda yake mata amsa kuwwa a kunne sai YAYA ADAM YANA DA WATA MATAR BAYAN KE,ta yaya hakan zata kasance?,ta yaya hakan zata yiwu?,bayan ko yaushe suna tare da dam?,shiba matafiyi ba ba komai ba bare tace yayi amfani da wannan damar yayi auren a wani garin bata sani ba?,sai ta sulale ta zauna a wajen,tasa hannunta guda biyun ta dafe kanta wanda taji yana sara mata,kanta taji yana cushewa,zai buga da kalar tunanin da take takurawa kanta dashi,saita fara karanto sunayen Allah,da haka ta samu taja jikinta ta koma falon ta zube saman kujera.
Tunda ta kwanta bata tashi ba sai da akayi sallar la'asar,kana kallonta zakace bata da lafiya,dab da kiran magariba adam ya shigo,tana daga kwancen ta daga kanta tana kallonsa,fuskarsa cike da walwala da wani irin nishadi wanda batasan daga ina ya samo asali ba,saita samu kanta da qarewa fuskarka kallo da kyau,zuciyarta tana nazartarsa,nazarin da bata taba yinsa a kan adam ba.
Ganinta a kwance yasa ya sauke hannayensa daya ware mata yana jiran ta shigo ya rungumeta,duka sai walwalarsa ta koma,ya tako da sassarfa cikin nuna damuwa me yawa ya iso gareta
"Heart,what happened?" Yayi maganar yana dagota zuwa jikinsa
'banajin dadi" ta bashi amsa a taqaice
"What?,kada dai ace a kwance kika wuni?"kai ta sake gyada masa
"Ya salam,me yasa baki kirani ba?,amma baki kyautamin ba, please please karki qara yimin haka,idan wani abu ya sameki fa?" Yayi maganar kamar zai fashe da kuka,sai ya kwantar da ita,ya ciro waya,saiji tayi yana kiran wani likitansa. Drip yasa aka daura mata,wai tafijin qwarin jikinta,ya kasa zaune ya kasa tsaye,bayan fitar likitan ya shiga kitchen ya dora abincin dare,yayi yayi ta fada me takeson ci tace masa babu komai.
Wanzuwarsa a kitchen din ya bata damar sake zurfafa cikin tunaninta,ta dinga hango mode dinsa tun daga shigowarsa gidan kawo yanzu,tarin qauna kulawa da kuma riritawa ce zallah,sai zuciyarta ta cika da kokwanto,amma kuma ta rasa meye yake bata qwarin gwiwa da tabbaci.
Karin ruwan babu abinda ya qara mata,saboda wata irin narkakkiyar damuwa ce dake kwance qasan a zuciya,a haka suka kwana. Washegari tunda wuri ya hada mata breakfast ya shirya yace mata zai fita,amma azahar ko la'asar zai dawo. Har ya fita saita miqe ta bishi,a qofar dakinsa sukaci karo,yasa hannu ya jawo qofar yana kullewa da dan sauri,yayin da idanunsa ke a kanta yana kasheta da murmushi.
"Akwai wani abu ne?,ko kinaso na taho miki da wani abun?" Kai ta girgiza
"A'ah,zan dan fita strolling ne idan na gaji da kwanciyar"
"Ba damuwa,amma ko nasa momee ta kawo miki raihanatu?"kiran sunan kawai yasa gabanta ya fadi,saboda tuna gagarumin abun da muddin ta samu tabbacin afkuwarsa,zai zama sila ta guntulewar alaqar auratayya tsakaninta da adam,duk yadda take da kai, muddin kai din maha'inci ko maciyin amana ne.....to tana shata layi me girma a tsakaninka da ita.
"Ka barta,na danji dadin jikin ai" ta amsa masa.
Kasa komawa dakinta tayi bayan fitarsa,taja jiki ta zauna saman kujera,kamar kuma wadda aka mintsina saita miqe da sauri,kai tsaye ta doshi dakin adam. Tambayar kanta takeyi me zataje tayi a dakin?,tunda ta tabbatar ya rufe dakin a gabanta,kuma bata da sauran spare key da zai bata damar shiga?,amma duk da wannan tunanin sai ta gaza tsaida kanta daga dosar dakin da takeyi.
Sau daya ta murda dakin bawai don tana tantama ko tana da masaniyar bai rufe ba,amma cikin iko da qudurar ubangiji taji ya bude,mamaki ya cikata,ta tsaya tana duban qofar bayan ta bude,ta leqa sai ta fahimci yana sauri ne bai murza key din da kyau ba,lock din bai gama shiga ba ya zare ya dauka ya shige. Sakin wannan tunanin tayi ta wuce dakin da gaggawa.
Cak ta tsaya tana qarewa dakin kallo,tana nazarin ta ina zata fara binciken da zai bata shaida ko tabbacin abinda take zargi?,shikam adam ma bashi da safe irin nata,saboda yasha gaya mata ya yarda da ita. Wani tunani ya fado mata,a dazu da suka shiga dakin taga yanata kaffa kaffa da wardrobe dinsa,tun bata ankara ba har hankalinta yakai kai,amma bata kawo komai a ranta ba ko kadan,saboda tasan zuwa yanzu ya wanke dukkan wani zarginsa a ranta.
Cike da fargaba ta buda wardrobe din,cikin ranta tana addu'ar Allah yasa komai ya zama hasashe ne,Allah yasa komai ya zama tunani ne,muddin ta samu adam da cin amanarta,batasan ta yadda zuciyarta zata iya dauka ba.
Tsaf ta bincike wardrobe din,saidai bataga komai ba,tasa hannu tana shirin rufewa idanunta ya sauka daga can qasanta,wani abu me kama da jaka ta gani a jingine daga can gefe,saita tsugunna ta jawo,jakace baqa mai cike da zips kala kala,tunda take da adam bata taba ganin jakar ba,wannan ya qara mata qaimi da karsashi,ta fara bude zips din,take kudade masu tarin yawa daure cikin kyauraye da kuma takardu masu yawa suka fado.
*H U G U M A*
*_TABARMAR ƘASHI_*💔
https://arewabooks.com/u/huguma
Page 45