Sashe 150
Tabarmar Kashi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Suna gab da karya kwanar shiga gidan haka kawai gabansa yaji ya fara faduwa. Ya lumshe ido yana kiran sunan Allah, me yake faruwa haka dashi?, Ya tambayi kana. A haka suka garasa cikin gidan shi da jibril ne ya dauki ledojin ya buda motar ya wuce kai tsaye sashensa. Harabar gidan ba kowa kasancewar magariba ta kawo kai.
Qofar a rufe take, sai ya sanya key dinsa ya bude ya tura ya shiga ya fara takawa a hankali zuwa ciki. Parlor din babu kowa shuru kakeji,ya danji mamaki ya kamashi,sai yaci gaba da kutsawa zuwa hanyar da zata sadashi da stairs yana kyautata zaton sun haura sama ne ita da fadeela din.
Wani mahaukacin bugawa zuciyarsa tayi yaji qwaqwalwarsa na neman tsayawa cak daga aiki. Fadeela ce kwance saman saman sassanyan marbles din dake shinfide a gurin, qafafunta na saman stairs na garshe, kanga kuma daya langabe na a qasa,sassalkar sumarsa ta baje sosai a gasa,yayin da kakkauran jini ya soma bata gurin.
Wani irin mummunar rawa jikinsa ya fara yi yanajin kamar numfashinsa zai bar iikinsa sanda va dagata yaga jikinta ya saki gaba daya kamar babu ruhi a tattare da ita. Bakinsa rawa yakeyi yanason kiran sunanta amma ya kasa yanason ya kira ameesha nan ma komai yaqi fitowa daga bakinsa,sai kawai ya saketa ya haura saman da mugun gudu da zummar nemo ameeshan yaji me ya samu diyarsa, saboda komai ya kwance daga kansa tunanin fara zuwa asibiti ma ya fita a kansa,so yake yaji meye ya sameta.
A hankali va janye hannunsa daga marigin gofar dakin sakamakon sautin darivar ameesha da yaji cakude da sautin muryar wani namijin
"Ya isa haka please mana, kai wai baka gajiya ne?"
"Ta yaya zan gaji? bayan har yanzu kawai dandanamin zuma kike a baki, kinqi barina na shiga ainihin inda abin yake?, kina rudani kawai da jikinki, kina barina akan hanya navita fama"
"Au, hakanma baiyi maka ba?,an gaya maka taba jikina din ma abune mai saugi? to ko mijin aurena sai randa nayi ra'ayi naji jima ina cikin yanayi matuqa nake sallama masa, kaima ka godewa Allah daka samu wannan damar,gaka yau har cikin dakin mijina,zaka kwana kana murzata" Dariya ya saki
"In sha Allahu vau sai na cimma gaci" dan tsaki taja
"To watagila idan naii abun yayimin yadda nakeso"
"Kina son muyita wahala ne na baki shawara ki kashe auren nan kawai kizo muyi aure ki huta da debar masa dukiya da kadan da kadan, kizo inda zan bude miki bakin lalitata kivita diba har sai kin gaji" dan shuru tayi sannan tace
"Ba zaka gane ba, kayi suna a rayuwa ma wani abune,yau ace ni matar dan MT JARMA ne ma wani babban alfarma ne, tabbas kana da kudi irin kudin da nakeso, amma matsalar sunanka baiyi fice kamar nasu ba,sannan kuma inason guy din sosai,yana da kyau ya iya soyayya garshe ne"
"Bansan baki da wayo ba sai yau, don ya fini kyau ni mummuna ne a kansa ai ba wani abu bane, kuma da kike maganar so soyayya, da soyayyarsa da dukiya wanne kika fi so?" Ya tambaya seriously
"KUDI malam sune fa gare magana" gyalgyalewa yayi da dariya
"Yauwa,aini na sani, shi kansa da bashi da komai ba zakiii sonsa ba na san halinki fa....ki bani kanki a yau kawai na miki algawarin million goma yanzun nan zakiji alert idan kin yarda"
"Amazing!" Ta fada da matuqar farinciki da zumudi fal muryarta
"Na yard…" Kamar an hankadashi da baya haka
yaji, bai iya tsaiwa yaji ragowar kalmar daga bakinta ba yaji kamar na daka tsawar sunan
"FADEELA!" tsakiyar kwanyarsa. Da wani mugun gudu da sassarfa ya dinga hada matakala bibbiyu uku uku yana sauka,yana isa yasa hannu ya kwashi fadeelan ya fita da gudu. Jibril na hangoshi ya tabbatar babu lafiya, bai bari ya iso ba ya wangle masa gofa,suna shiga ya figi motar da mugun gudu tare da searching na asibitin da zasuje a kansa ba tare da ya tambayi ogan L nasa ba,hankalinsa a mugun tashe sakamakon ganin hawaye saman fuskar mai gidan nasa,mutumin da ya sani sama da shekaru, bai taba ganin karaya ko girgiza saman fuskarsa ba komai girman tashin hankali, lallai abinda ya sameshi ba qarami bane, duk da kowa yasan tsananin qaunar da yakewa fadeela din wanda bata boyuwa.
Har sukaje asibitin aka karbeta tare da qogarin dawo da ita cikin hayyacinta ameeshan batasan abinda akeyi ba. Sai da likitoci suka gama komai suka masa bayanin idan ta farka za'a yi mata X-ray saboda tabbatar da lafiyar qwaqwalwarta akan buguwar da tayi,yana dakin gaban gadon fadeela din a zaune sannan uwar ta iso a birkice tana kuka.
"Me ya sameta?" Ta jefa masa tambayar da sai da yaji kamar ya Sanya wuga ya yanka maqogaronta banda zuciyar musulunci dake qirjinsa, da sunayen Allah daya dinga kira wadanda suka taimaka waien daidaita shi, banda haka ya tabbatar a yadda qirjinsa yayi nauyi shima iwar haka ba shakka yana kwance saman gado ana jinyarsa
"Fita!!" Ya fada a tsawace muryarsa na wani irin sargewa da matsanancin bacin rai,fitar saurin muryarta ba abinda yake tuna masa sai gazantacciyar hirarsu da kwartonta
"Kayi haquri don Allah, ba laifi ko sakacina bane,na gama mata wanka na shiryata kenan,na hau sama nayi wanka nima kafin na shirya na fito na sauko naga babu ita,sai jini wajen stairs, masu aiki suke gayamin ka fita da ita" ta fada cikin gunjin kuka,gabanta kuma yana faduwa da matsanancin toro da firgicin zaiyiwu yaga ANAS ko Kuma wani abu da yayi kama da haka Zaki fita daga nan ko sai na wulaqantaki?, maci amana me tozarta sunnar ma'aiki banason na sake ganin fuskarki daga yau a gaban ido na, muddin kika sake kika qara nunan fuskarki sai nasa bindiga na harbeki,ki tafi na sakeki saki daya" ya furta cikin matugar danne zuciyarsa ya furta saki dayan, amma zuciyarsa tafi amanna da ya qarasa guntule igiyar guda dayan da a yanzu tayi saura a tsakaninsu.
Sosai ta gigice da jin sakin da ya rattabo matan,ta bude baki cikin rawar murya ta fara roqarsa yace
"Ki yiwa kanki suttura ki fita tun ban tattaka ki a nan wajen ba,kije ki auri me kudin da ya fini,ki tara dukiyar da duk kikeson tarawar wannan damuwarki ne, abu daya zan gaya miki,daga yau ki cire a ranki a duniya kin taba haihuwar wata diya fadeela har abada" zata ci gaba da rogonsa yace
"Duk kalma daya idan kika qafa furtamin a bakin aurenki take, get out from here idiot!!!" Dole taja qafafunta ta fice, yasa hannu ya lullube fuskarsa zuciyarsa na bashi yanxun haka akwai janaba a jikinta na wancan kwarton nata.
Bincike akan fadeela ya kammala,ya kuma tabbatar data samu ciwo cikin qwaqwalwarta wanda shine sila na haduwarta da lalurar EPILEPSY. randa ciwon ya fara motsa mata yayi mugun birkicewar da bai taba yi ba,saboda shi dai bai tana ganin ciwon a gaban idanunsa ba daga wajen wani sai yau akan diyarsa mafi soyuwa a wajensa.
Zafafa biyar
"HUGUMA*
•_TABARMAR KASHI_*
Book 02 Page 58
Tun daga ranar bai sake bari ameesha taga
fadeela ba, kamar yadda ameeshan bata sake ganin
fuskarsa ba sai a hoto ko a media. Duk wanda zai tilasta masa yabar ta ta dinga ganin diyarta ya musu rantsuwar da suka tabbatar babu janyewa,duk da bai fito ya furta ainihin abinda ya rabasu ba,dr jarma kawai ya shaidawa saboda gudun kada yace ya maidata dakinta, ko ya bata diyarta,shi kurna ya gayawa hajiya qarama. Hajiya qaraman murmushi ta saki
"Ehe, ka gani ko? ni dama na jima ina ganinta tana
shigowa da maza gidan, to amma idan kayi magana
yanzu za'a ce ka takurawa surukarka shi yasa na
bari, amma kullum ina addu'ar Ubangi ya nuna maka".
"Ince ga yadda na rayu a wadan nan shekarun cikin ciwuka masu zafi guda biyu bata baki ne,ciwon fadeela da kuma mummunan ciwon da ameesha ta dasawa zuciyata,da gyar nima na qwaci kaina daga bugawar zuciya saboda mummunan hawan jini daya kamani wanda da gyar na qwaci kaina daga gareshi Allah ya kawomin waraka don ya dubi zuciyata akan ban zalunci kowa ba.tun daga sannan ta cire kowanne aminci a zuciyata daga kan diya mace, nayi mata uzuri duk da yadda bayyanar halinta na aureta mun zauna nayi haquri da ita mun rabu na tausaya mata na dawo da ita,na sanya qafa na ture duk wani aibunta saboda ganin kamar ta canza,ashe lumbu lumbu tayimin take cin dunduniyata,A DUNIYA AKWAI ABINDA YAFI CIN AMANAR WANDA KA AMINCEWA CIWO DA ZAFI!" ya furta wani irin dumi yana fita daga numfashinsa, alamu suna nuna cikin gololuwar bacin rai yake
"Babu" yaji sãahar ta fada cikin rawar muryar daya tabbatar kuka takeyi.
Hannunsa yakai ya shafi fuskarta,sai ya samu fuskartata jige sharkaf da hawaye,zuciyarsa ra motsa sosai. shi da itan dukkansu an bar musu wani tabo da har su mutu ba zasu daina tunashi ba,ba kuma lallai su fasa jin ciwo idan an taba musu gurin ba,sai ya zameta daga jikinsa cikin nutsuwa,ya sauka daga saman gadon ya kunna fitilar dakin, haske ya gauraye ko ina.
Stool ya jawo gaban gadon,ya zauna sosai yana kallonta da idanunsa da suka canza launi zuwa kalar ruwan goro kamar an disa jini a cikinsu.
"Tashi" ya furta a tausashe yana miga mata hannunsa. A hankali ta yaye duvet din sannan ta sanya tattausan hannunta saman nasa ya migar da ita ta zauna sosai,sai ya koma shima ya zauna sosai din, yayi folding hannayensa a qirjinsa yana dubanta kai tsaye
"Kiyi haquri, na karanta miki diary ba tare da izininki ba" kai ta daga ta kalleshi sai suka hada do,wasu sabbin hawaye suka zarto mata tana jin tausayinsa yana sauka a girjinta,wasu similarities dake cikin labaran su suna dawo mata
"Yayi fama da yawa,shi din bayan yaudara da cin amana harda nakasa ta barwa 'yar cikinta 'yar cikinsa?"
"I hope you forgiven" kai ta gyada masa a hankali.
"Thank you" ya furta yayi shuru na wasu 'yan daqiqu vanason hada abinda zaice da ita, saboda yanzun lokaci ne da zai nema dukkan wata yarda tata du gina kammalalliyar rayuwar da yake buri,iska ya furzar daga bakinsa,sannan ya sake mayar da dubansa a kanta
Qofar a rufe take, sai ya sanya key dinsa ya bude ya tura ya shiga ya fara takawa a hankali zuwa ciki. Parlor din babu kowa shuru kakeji,ya danji mamaki ya kamashi,sai yaci gaba da kutsawa zuwa hanyar da zata sadashi da stairs yana kyautata zaton sun haura sama ne ita da fadeela din.
Wani mahaukacin bugawa zuciyarsa tayi yaji qwaqwalwarsa na neman tsayawa cak daga aiki. Fadeela ce kwance saman saman sassanyan marbles din dake shinfide a gurin, qafafunta na saman stairs na garshe, kanga kuma daya langabe na a qasa,sassalkar sumarsa ta baje sosai a gasa,yayin da kakkauran jini ya soma bata gurin.
Wani irin mummunar rawa jikinsa ya fara yi yanajin kamar numfashinsa zai bar iikinsa sanda va dagata yaga jikinta ya saki gaba daya kamar babu ruhi a tattare da ita. Bakinsa rawa yakeyi yanason kiran sunanta amma ya kasa yanason ya kira ameesha nan ma komai yaqi fitowa daga bakinsa,sai kawai ya saketa ya haura saman da mugun gudu da zummar nemo ameeshan yaji me ya samu diyarsa, saboda komai ya kwance daga kansa tunanin fara zuwa asibiti ma ya fita a kansa,so yake yaji meye ya sameta.
A hankali va janye hannunsa daga marigin gofar dakin sakamakon sautin darivar ameesha da yaji cakude da sautin muryar wani namijin
"Ya isa haka please mana, kai wai baka gajiya ne?"
"Ta yaya zan gaji? bayan har yanzu kawai dandanamin zuma kike a baki, kinqi barina na shiga ainihin inda abin yake?, kina rudani kawai da jikinki, kina barina akan hanya navita fama"
"Au, hakanma baiyi maka ba?,an gaya maka taba jikina din ma abune mai saugi? to ko mijin aurena sai randa nayi ra'ayi naji jima ina cikin yanayi matuqa nake sallama masa, kaima ka godewa Allah daka samu wannan damar,gaka yau har cikin dakin mijina,zaka kwana kana murzata" Dariya ya saki
"In sha Allahu vau sai na cimma gaci" dan tsaki taja
"To watagila idan naii abun yayimin yadda nakeso"
"Kina son muyita wahala ne na baki shawara ki kashe auren nan kawai kizo muyi aure ki huta da debar masa dukiya da kadan da kadan, kizo inda zan bude miki bakin lalitata kivita diba har sai kin gaji" dan shuru tayi sannan tace
"Ba zaka gane ba, kayi suna a rayuwa ma wani abune,yau ace ni matar dan MT JARMA ne ma wani babban alfarma ne, tabbas kana da kudi irin kudin da nakeso, amma matsalar sunanka baiyi fice kamar nasu ba,sannan kuma inason guy din sosai,yana da kyau ya iya soyayya garshe ne"
"Bansan baki da wayo ba sai yau, don ya fini kyau ni mummuna ne a kansa ai ba wani abu bane, kuma da kike maganar so soyayya, da soyayyarsa da dukiya wanne kika fi so?" Ya tambaya seriously
"KUDI malam sune fa gare magana" gyalgyalewa yayi da dariya
"Yauwa,aini na sani, shi kansa da bashi da komai ba zakiii sonsa ba na san halinki fa....ki bani kanki a yau kawai na miki algawarin million goma yanzun nan zakiji alert idan kin yarda"
"Amazing!" Ta fada da matuqar farinciki da zumudi fal muryarta
"Na yard…" Kamar an hankadashi da baya haka
yaji, bai iya tsaiwa yaji ragowar kalmar daga bakinta ba yaji kamar na daka tsawar sunan
"FADEELA!" tsakiyar kwanyarsa. Da wani mugun gudu da sassarfa ya dinga hada matakala bibbiyu uku uku yana sauka,yana isa yasa hannu ya kwashi fadeelan ya fita da gudu. Jibril na hangoshi ya tabbatar babu lafiya, bai bari ya iso ba ya wangle masa gofa,suna shiga ya figi motar da mugun gudu tare da searching na asibitin da zasuje a kansa ba tare da ya tambayi ogan L nasa ba,hankalinsa a mugun tashe sakamakon ganin hawaye saman fuskar mai gidan nasa,mutumin da ya sani sama da shekaru, bai taba ganin karaya ko girgiza saman fuskarsa ba komai girman tashin hankali, lallai abinda ya sameshi ba qarami bane, duk da kowa yasan tsananin qaunar da yakewa fadeela din wanda bata boyuwa.
Har sukaje asibitin aka karbeta tare da qogarin dawo da ita cikin hayyacinta ameeshan batasan abinda akeyi ba. Sai da likitoci suka gama komai suka masa bayanin idan ta farka za'a yi mata X-ray saboda tabbatar da lafiyar qwaqwalwarta akan buguwar da tayi,yana dakin gaban gadon fadeela din a zaune sannan uwar ta iso a birkice tana kuka.
"Me ya sameta?" Ta jefa masa tambayar da sai da yaji kamar ya Sanya wuga ya yanka maqogaronta banda zuciyar musulunci dake qirjinsa, da sunayen Allah daya dinga kira wadanda suka taimaka waien daidaita shi, banda haka ya tabbatar a yadda qirjinsa yayi nauyi shima iwar haka ba shakka yana kwance saman gado ana jinyarsa
"Fita!!" Ya fada a tsawace muryarsa na wani irin sargewa da matsanancin bacin rai,fitar saurin muryarta ba abinda yake tuna masa sai gazantacciyar hirarsu da kwartonta
"Kayi haquri don Allah, ba laifi ko sakacina bane,na gama mata wanka na shiryata kenan,na hau sama nayi wanka nima kafin na shirya na fito na sauko naga babu ita,sai jini wajen stairs, masu aiki suke gayamin ka fita da ita" ta fada cikin gunjin kuka,gabanta kuma yana faduwa da matsanancin toro da firgicin zaiyiwu yaga ANAS ko Kuma wani abu da yayi kama da haka Zaki fita daga nan ko sai na wulaqantaki?, maci amana me tozarta sunnar ma'aiki banason na sake ganin fuskarki daga yau a gaban ido na, muddin kika sake kika qara nunan fuskarki sai nasa bindiga na harbeki,ki tafi na sakeki saki daya" ya furta cikin matugar danne zuciyarsa ya furta saki dayan, amma zuciyarsa tafi amanna da ya qarasa guntule igiyar guda dayan da a yanzu tayi saura a tsakaninsu.
Sosai ta gigice da jin sakin da ya rattabo matan,ta bude baki cikin rawar murya ta fara roqarsa yace
"Ki yiwa kanki suttura ki fita tun ban tattaka ki a nan wajen ba,kije ki auri me kudin da ya fini,ki tara dukiyar da duk kikeson tarawar wannan damuwarki ne, abu daya zan gaya miki,daga yau ki cire a ranki a duniya kin taba haihuwar wata diya fadeela har abada" zata ci gaba da rogonsa yace
"Duk kalma daya idan kika qafa furtamin a bakin aurenki take, get out from here idiot!!!" Dole taja qafafunta ta fice, yasa hannu ya lullube fuskarsa zuciyarsa na bashi yanxun haka akwai janaba a jikinta na wancan kwarton nata.
Bincike akan fadeela ya kammala,ya kuma tabbatar data samu ciwo cikin qwaqwalwarta wanda shine sila na haduwarta da lalurar EPILEPSY. randa ciwon ya fara motsa mata yayi mugun birkicewar da bai taba yi ba,saboda shi dai bai tana ganin ciwon a gaban idanunsa ba daga wajen wani sai yau akan diyarsa mafi soyuwa a wajensa.
Zafafa biyar
"HUGUMA*
•_TABARMAR KASHI_*
Book 02 Page 58
Tun daga ranar bai sake bari ameesha taga
fadeela ba, kamar yadda ameeshan bata sake ganin
fuskarsa ba sai a hoto ko a media. Duk wanda zai tilasta masa yabar ta ta dinga ganin diyarta ya musu rantsuwar da suka tabbatar babu janyewa,duk da bai fito ya furta ainihin abinda ya rabasu ba,dr jarma kawai ya shaidawa saboda gudun kada yace ya maidata dakinta, ko ya bata diyarta,shi kurna ya gayawa hajiya qarama. Hajiya qaraman murmushi ta saki
"Ehe, ka gani ko? ni dama na jima ina ganinta tana
shigowa da maza gidan, to amma idan kayi magana
yanzu za'a ce ka takurawa surukarka shi yasa na
bari, amma kullum ina addu'ar Ubangi ya nuna maka".
"Ince ga yadda na rayu a wadan nan shekarun cikin ciwuka masu zafi guda biyu bata baki ne,ciwon fadeela da kuma mummunan ciwon da ameesha ta dasawa zuciyata,da gyar nima na qwaci kaina daga bugawar zuciya saboda mummunan hawan jini daya kamani wanda da gyar na qwaci kaina daga gareshi Allah ya kawomin waraka don ya dubi zuciyata akan ban zalunci kowa ba.tun daga sannan ta cire kowanne aminci a zuciyata daga kan diya mace, nayi mata uzuri duk da yadda bayyanar halinta na aureta mun zauna nayi haquri da ita mun rabu na tausaya mata na dawo da ita,na sanya qafa na ture duk wani aibunta saboda ganin kamar ta canza,ashe lumbu lumbu tayimin take cin dunduniyata,A DUNIYA AKWAI ABINDA YAFI CIN AMANAR WANDA KA AMINCEWA CIWO DA ZAFI!" ya furta wani irin dumi yana fita daga numfashinsa, alamu suna nuna cikin gololuwar bacin rai yake
"Babu" yaji sãahar ta fada cikin rawar muryar daya tabbatar kuka takeyi.
Hannunsa yakai ya shafi fuskarta,sai ya samu fuskartata jige sharkaf da hawaye,zuciyarsa ra motsa sosai. shi da itan dukkansu an bar musu wani tabo da har su mutu ba zasu daina tunashi ba,ba kuma lallai su fasa jin ciwo idan an taba musu gurin ba,sai ya zameta daga jikinsa cikin nutsuwa,ya sauka daga saman gadon ya kunna fitilar dakin, haske ya gauraye ko ina.
Stool ya jawo gaban gadon,ya zauna sosai yana kallonta da idanunsa da suka canza launi zuwa kalar ruwan goro kamar an disa jini a cikinsu.
"Tashi" ya furta a tausashe yana miga mata hannunsa. A hankali ta yaye duvet din sannan ta sanya tattausan hannunta saman nasa ya migar da ita ta zauna sosai,sai ya koma shima ya zauna sosai din, yayi folding hannayensa a qirjinsa yana dubanta kai tsaye
"Kiyi haquri, na karanta miki diary ba tare da izininki ba" kai ta daga ta kalleshi sai suka hada do,wasu sabbin hawaye suka zarto mata tana jin tausayinsa yana sauka a girjinta,wasu similarities dake cikin labaran su suna dawo mata
"Yayi fama da yawa,shi din bayan yaudara da cin amana harda nakasa ta barwa 'yar cikinta 'yar cikinsa?"
"I hope you forgiven" kai ta gyada masa a hankali.
"Thank you" ya furta yayi shuru na wasu 'yan daqiqu vanason hada abinda zaice da ita, saboda yanzun lokaci ne da zai nema dukkan wata yarda tata du gina kammalalliyar rayuwar da yake buri,iska ya furzar daga bakinsa,sannan ya sake mayar da dubansa a kanta