Sashe 97
Tabarmar Kashi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sanda ya iso ta gama hada komai,hannuwanta na harde a qirjinta ta zubawa na'urar idanu tana jiran ta gama tafasa mata shi ta juye abinta ta wuce ciki.
"Ke" taji ya furta da kakkaurar muryarsa dake cike da wani irin sauti me ratsa kunne da fusgar hankali sanda yake kunna tap din kitchen din ya tara hannayensa yana wankesu.
Bata motsa ba kwata kwata,tamkar babu kowa a wajen har zuwa sanda ya kammala wankewar yasa kitchen towel ya goge farare tas din hannun nasa da babu wata alamar
datti.
A nutse ya zube mata idanunsa,fuskarta sam bata a wajen,amma duk da haka yana iya ganin gefan fuskar tata dake da wani kwantaccen gashi da baya iya kitsuwa,wanda hakan yake masifar qara mata kyau. Sarai yasan fa jishi,wannan halin nata ne kuma abinda yafi tsana kaf rayuwarshi rainin hankali da halin ko in kula
"'Dake nake magana" ya fada a zafafe saidai cikin nutsuwa. Sai a sannan fa sauke hannuwanta ta kuma sanya nata idanun cikin nashi
"Baki iya gaida na gaba dake ba?" Yayi mata tambayar tana sake nutsa idanunsa cikin fararen qwayar idanunta. Second biyar ta dauke dubanta daga kansa,ta karanci izzar da girman kan nasa ne ya motsa da safen nan,bata kuma da ra'ayin kulashi saboda ba zaman da tazo suyi dashi ba kenan,a yanzun jira kawai takeyi gidan ya zama daga shi sai masu shi,bata tunanin ma zai sake ganinta a wanann sashen nasa,zata koma inda tafi wayo ne.
Batasan ya akayi ba,bata kuma san daga ina ba,tana tsaka da juye coffee din nata tajishi dab da ita tamkar zai take yatsunta kwatankwacin abinda ya taba yi mata a company. Wancan karon taji babu dadi qwarai da gaske,don haka a yanzun cikin hanzari taja da baya tana dubansa da razanannun idanunta da suke nuna yadda ta firgita,coffee din data fara juyewa yayi tangal tangal ta fantsama a gasa da jikin machine din.
Wani irin duba yake mata dake nuna fushi cikin idanunsa
"Ko naira biyar na biya a matsayin sadakinki tana da daraia da kima a wajena,saboda
halal dina ce gumina ce,sannan nasan zafin
nemanta.bazan bari a keta alfarmarta ba,don
munyi auren biyan bugatar kawunanmu
hakan ba yana nufin nidin sarakai bane,bazan
dauki rashin kunya ko tsiwa ba,koda zaman
dadiro mukeyi dake,daga yau ya zama dole
ki gaidani kamar yadda kowa cikin gidan nan
yakeyi,kamar yadda nima ya zama dole na
bawa duk wanda vake samana girmansa"
wasu hawaye ne suka fara taruwar mata cikin
idanu,shi kuma irin nashi salon kenan?,tun
daga ranar farko?. Kai ta girgiza,cikin jarumta
da dakiya ta ajjiye cup din hannunta a gefe
"Ai ba haka mukayi da kai ba mr jarma,ba
auren gaishe gaishe mukayi zamuyi da kai
ba,zan kula da fadeela,ni kuma zan rayu
independently" taku biyu ya qaro gaba ya sake
rage kusancin dake a tsakaninsu,sai a sannan
ma ta fuskanci ba dab da ita yake ba,akwai
sauran tazara a tsakaninsu,tsoratar da tayi
yasa taji kaman yayi kusa da ita
"Idan kina tunanin zan nemi wani abu daga gurinki ni ki cire wanann memory din daga kwanyarki ki qoneshi,har abada,saboda nidin tataccen dan iska ne da nake iya samun budurwa kowacce rana nayi disvirgin nata,kinga ko ke kinyimin kadan,abinda nakeso ki fahimta shine,har abada sama nake dake, you must give me a respect, koda ban saka kudina na biya sadakinki ba,ko kece ne kika biya sadakina mrs Khadija?" Ya jefa mata tambayar yana dubanta irin kallon kai tsaye,hannuwansa cikin aljihun wandonsa.
Idanunta dake walainiya da gyallin
hawaye ta daga ta dubeshi,yadda ya kirata kai tsaye da sunan da dukkansu suke sakayawa suke mutuntawa saboda sunan mahaifiya ce ga mahaifinsu ya bata ranta,taci gaba da tsirashi da ido haushinsa da tsanarsa tana kamata,duk yadda tace zata buda baki tayi magana ba shakka hawayen idanunta ne zasu balle,abinda kuma bataso ya sake gani daga gareta
"Maganata itace dai dai,ni dinne kenan na biya,so that's all i need from you ba wani abu can na daban ba" yayi maganar yana dage faffadan kafadunsa guda biyu,sannan ya zare hannunsa daga aljihun ya sake matsowa kadan gaban na'urar dafa coffee din,ya dauki mug din data fara juyewa a ciki ya juye dukka coffee din a nutse ya juya yana barin kitchen din,sai kuma ya tsaya cak ba tare da ya juyo ba
"Ki shirya nan da hour daya zamu shiga cikin gida,maji nason magana dake" sai ya sanya kai yana ci gaba da ficewar,can qasan ransa yana jin wani nishadi da dadin yadda yau ya samu coffee din daya jima yana mararin sha ba tare da ya zubar da kansa ya nema a dafa masa ba.
Wani baqinciki ne yazo mata iya
wuya,ga mari ga tsinka jaka? ta rasa me zatayi masa ta huce,sai kawai tace dashi
"Idan ka shamin coffe ban baka ba,gaisuwa
kuma ni ba auren gaisuwa mukayi da kai ba,so
kayi harkar gabanka kayi abinda ya dameka
nima nayi nawa,idan hakan bazaiyiwu ba ka
fadi nawa ka biya na maida maka abinka kowa
ya kama sabgarshi yaji da damuwarsa" ido
ya lumshe yana sipping coffee din, dadinsa
ya ratsashi,ya sake dakatawa daga tafiyar da
yakeyi ya hadiye sannan ya juyo
"Ki ragewa kanki rashin kunya da tsiwa,if
not kuma zakisha mamaki tare da wahala a
hannuna,zaki rayu ba tare da na shiga harkarki
ba,but dole ki bani respect, you get it?" Yayi
mata tambayar bawai don yana bugatar amsa
ba,sai yasa kansa ya fice.
Yana fita hawayen data riqe yana silmiyo
mata,tabi jikinta da yadan baci da coffee din da kallo sai kawai ta sake sakin hawayen nata
sosai,magoshinta ya cika da wani abu,anya
batayi kuskuren aurensa ba?,anya ba shirya
wannan abun yayi ba?,anya bawai ya shirya
aurenta bane bawai don fadeela kawai ba?,bai shirya hakan bane anya don ya gasata saboda ta samu kubcewa daga kamfaninsu?. Wannan tunanin ya sake daga mata hankali,amma kuma sannu sannu wata murya daga can gasan zuciyarta ke gaya mata
"Kema kina da taki damar karki wani damu da koma meye ya shirya" famfon ta kunna ta tara hannuwanta ta daurayesu ta kuma dauraye jikinta ta baro kitchen din, kamar zuciyarta zata fashe. Da yake zancan jacob ma ita ina ruwanta da wani kukunsa,bashi ya ajeshi ba?, shi yaga zai iya,amma itakam ba zata dauki wannan abubuwan ba sam,don ba wannan auren suka tsara zasuyi shi da ita ba.
*HUGUMA*
* TABARMAR KASHI_*
Book 02 Page 15
Kayan jikinta ta zare kaf ta shiga wanka,tanata qoqarin controlling kanta da fushin da yakeson taso mata a kansa,batason taje wajen maji fuskarta da wani yanayi maras dadi. Cikin miti hamsin ta kammala Shiryawa cikin wata qawatacciyar lallausar atamfar exclusive super me matugar kyau da tsari, dinkin tea boubou akayi mata wanda ya zauna mata a jiki qwarai da gaske, ya kuma fidda sigar kyau da dirin da Allah yayi mata,siririyar sarqar dake wuyanta ta gara fidda tsaho da hasken wuyanta. Medium chantilly vail ta yafa wanda ya dace qwarai da shigarta,ta wadata iikinta da turarukanta masu sanyin qamshi. Har tayi taku biyu gaba qafafunta sanye da wasu plate shoes na kamfanin saint Laurent sai ta dawo ta tsaya gaban mudubin tayi folding hannayenta a qirji,kenan yanzun tare dashi zasu jera zuwa cikin gidan?. Qaramin tsaki taja tana juya abun cikin ranta,ita sam ko hanya batason hadawa dashi,duka yadda ma ta lissafa abubuwan yadda zasu kasance sunata zuwar mata da sabanin hakan,totally ma bata taba kawowa zatayi koda rabin kwana bane a sassansa bare kwana guda cur,saidai ta riga ta tsarama kanta yadda komai zai tafi,bata yarda da wannar tsarin ba.
Duk da tare suke da jibril suna tattaunawa akan ayyukan da ya fara a Australia ya barosu ya taho nan,amma hankalinsa yana kan agogon hannunsa,lokaci lokaci sai ya daga ya duba,ransa yana sake baci. Ya tsani jira, kuma yana tsammanin ya sanar mata zasu shiga maji na son ganinta. Sam baiso ma main ta umarci ganinsu a tare ba,to amma yadda ya fuskanci maji na cikin murna matuga da auren nasa,bayason sam abinda zai tauye wannan farincikin nata.
Mintunan da ya diba mata suna cika ya miqe hannayensa zube a aljihun wandonsa yana yiwa jibril bayanin abinda zai tattara masa ya kuma tura masa duka bayanan ta email,sannan kai tsaye ya fice daga falon zuwa farfajiyar gidan yana takawa majestically kamar yadda ya saba.
Dab da zai isa ainihin sassan gidan nadeeya ta fito dauke da wasu trays. Har zata gota taji husky voice din nan nasa na kiranta. Da sauri kuma cikin murmushi ta sauya akalarta zuwa gareshi,idanunta a kan miskilar fuskar nan da kullum take a dinke tsaf,banda ita,kaf duniya batajin akwai wadda ke iya tunkararsa haka,sau da dama ita dinma yana mata kwarjini,wannan dalilin ne ya sanya ko yaya tayi masa wani laifi take shiga uku,iya idanunsa kadai sun isa sakaka a tara
"Good morning yaa moha"
"Morning" ya amsa mata a taqaice yana duban trays din
"Kayan dasu banaan sukayi breakfast ne na debo,kasan sun wuce"
"Ban tambaya ba.. ki wuce ki taho da
ita, kusameni a nan zamu shiga tare" ya fada cikin basarwar nan tasa. Dadi ne ya Kama nadeeya,dama tun dazun take jiran shigowarsu,don ta matsu taga aunty N din,fadeela kuwa baccin daya debeta da safen shi ya kawo sauqin rigimarta,maji ta hana kowa zuwako kai abinci ma tace a gyalesu tunda akwai cook a sassan. Cikin azama ta qwalawa daya daga cikin masu aikin gidan kira,ta qaraso ta jingina mata trays din tayi gaba
"Idan kuka dade ranki ne zai baci" ta jiyo muryarsa, saita gyada kai tana qara hanzari
kadan.
Muryar nadeeya da taji tana sallama bayan knocking din da take mata ya sanyata miqewa tana murmushi,ta isa bakin qofar ta bude.
Rungume juna kawai sukayi,fuskar nadeeya cike da fara'a kamar wadda ta shekara bata ga sãahar din ba
"Ina faddee na?"
"Tayi baccin gajiya,tun da safe tafarka tana rigimar zuwa gurinki,amma maji tace ba yanzu ba,babu wanda zai tasheku" murmushi säahar ta saki tana in nauyi da kunyar majin tun kafin ma su hadu
"Yaa moha ne yace muje nayi miki jangora,yana jiranki a bakin part dinmu" nadeeya ta fadi tana qarewa sãahar kallo.
"Ke" taji ya furta da kakkaurar muryarsa dake cike da wani irin sauti me ratsa kunne da fusgar hankali sanda yake kunna tap din kitchen din ya tara hannayensa yana wankesu.
Bata motsa ba kwata kwata,tamkar babu kowa a wajen har zuwa sanda ya kammala wankewar yasa kitchen towel ya goge farare tas din hannun nasa da babu wata alamar
datti.
A nutse ya zube mata idanunsa,fuskarta sam bata a wajen,amma duk da haka yana iya ganin gefan fuskar tata dake da wani kwantaccen gashi da baya iya kitsuwa,wanda hakan yake masifar qara mata kyau. Sarai yasan fa jishi,wannan halin nata ne kuma abinda yafi tsana kaf rayuwarshi rainin hankali da halin ko in kula
"'Dake nake magana" ya fada a zafafe saidai cikin nutsuwa. Sai a sannan fa sauke hannuwanta ta kuma sanya nata idanun cikin nashi
"Baki iya gaida na gaba dake ba?" Yayi mata tambayar tana sake nutsa idanunsa cikin fararen qwayar idanunta. Second biyar ta dauke dubanta daga kansa,ta karanci izzar da girman kan nasa ne ya motsa da safen nan,bata kuma da ra'ayin kulashi saboda ba zaman da tazo suyi dashi ba kenan,a yanzun jira kawai takeyi gidan ya zama daga shi sai masu shi,bata tunanin ma zai sake ganinta a wanann sashen nasa,zata koma inda tafi wayo ne.
Batasan ya akayi ba,bata kuma san daga ina ba,tana tsaka da juye coffee din nata tajishi dab da ita tamkar zai take yatsunta kwatankwacin abinda ya taba yi mata a company. Wancan karon taji babu dadi qwarai da gaske,don haka a yanzun cikin hanzari taja da baya tana dubansa da razanannun idanunta da suke nuna yadda ta firgita,coffee din data fara juyewa yayi tangal tangal ta fantsama a gasa da jikin machine din.
Wani irin duba yake mata dake nuna fushi cikin idanunsa
"Ko naira biyar na biya a matsayin sadakinki tana da daraia da kima a wajena,saboda
halal dina ce gumina ce,sannan nasan zafin
nemanta.bazan bari a keta alfarmarta ba,don
munyi auren biyan bugatar kawunanmu
hakan ba yana nufin nidin sarakai bane,bazan
dauki rashin kunya ko tsiwa ba,koda zaman
dadiro mukeyi dake,daga yau ya zama dole
ki gaidani kamar yadda kowa cikin gidan nan
yakeyi,kamar yadda nima ya zama dole na
bawa duk wanda vake samana girmansa"
wasu hawaye ne suka fara taruwar mata cikin
idanu,shi kuma irin nashi salon kenan?,tun
daga ranar farko?. Kai ta girgiza,cikin jarumta
da dakiya ta ajjiye cup din hannunta a gefe
"Ai ba haka mukayi da kai ba mr jarma,ba
auren gaishe gaishe mukayi zamuyi da kai
ba,zan kula da fadeela,ni kuma zan rayu
independently" taku biyu ya qaro gaba ya sake
rage kusancin dake a tsakaninsu,sai a sannan
ma ta fuskanci ba dab da ita yake ba,akwai
sauran tazara a tsakaninsu,tsoratar da tayi
yasa taji kaman yayi kusa da ita
"Idan kina tunanin zan nemi wani abu daga gurinki ni ki cire wanann memory din daga kwanyarki ki qoneshi,har abada,saboda nidin tataccen dan iska ne da nake iya samun budurwa kowacce rana nayi disvirgin nata,kinga ko ke kinyimin kadan,abinda nakeso ki fahimta shine,har abada sama nake dake, you must give me a respect, koda ban saka kudina na biya sadakinki ba,ko kece ne kika biya sadakina mrs Khadija?" Ya jefa mata tambayar yana dubanta irin kallon kai tsaye,hannuwansa cikin aljihun wandonsa.
Idanunta dake walainiya da gyallin
hawaye ta daga ta dubeshi,yadda ya kirata kai tsaye da sunan da dukkansu suke sakayawa suke mutuntawa saboda sunan mahaifiya ce ga mahaifinsu ya bata ranta,taci gaba da tsirashi da ido haushinsa da tsanarsa tana kamata,duk yadda tace zata buda baki tayi magana ba shakka hawayen idanunta ne zasu balle,abinda kuma bataso ya sake gani daga gareta
"Maganata itace dai dai,ni dinne kenan na biya,so that's all i need from you ba wani abu can na daban ba" yayi maganar yana dage faffadan kafadunsa guda biyu,sannan ya zare hannunsa daga aljihun ya sake matsowa kadan gaban na'urar dafa coffee din,ya dauki mug din data fara juyewa a ciki ya juye dukka coffee din a nutse ya juya yana barin kitchen din,sai kuma ya tsaya cak ba tare da ya juyo ba
"Ki shirya nan da hour daya zamu shiga cikin gida,maji nason magana dake" sai ya sanya kai yana ci gaba da ficewar,can qasan ransa yana jin wani nishadi da dadin yadda yau ya samu coffee din daya jima yana mararin sha ba tare da ya zubar da kansa ya nema a dafa masa ba.
Wani baqinciki ne yazo mata iya
wuya,ga mari ga tsinka jaka? ta rasa me zatayi masa ta huce,sai kawai tace dashi
"Idan ka shamin coffe ban baka ba,gaisuwa
kuma ni ba auren gaisuwa mukayi da kai ba,so
kayi harkar gabanka kayi abinda ya dameka
nima nayi nawa,idan hakan bazaiyiwu ba ka
fadi nawa ka biya na maida maka abinka kowa
ya kama sabgarshi yaji da damuwarsa" ido
ya lumshe yana sipping coffee din, dadinsa
ya ratsashi,ya sake dakatawa daga tafiyar da
yakeyi ya hadiye sannan ya juyo
"Ki ragewa kanki rashin kunya da tsiwa,if
not kuma zakisha mamaki tare da wahala a
hannuna,zaki rayu ba tare da na shiga harkarki
ba,but dole ki bani respect, you get it?" Yayi
mata tambayar bawai don yana bugatar amsa
ba,sai yasa kansa ya fice.
Yana fita hawayen data riqe yana silmiyo
mata,tabi jikinta da yadan baci da coffee din da kallo sai kawai ta sake sakin hawayen nata
sosai,magoshinta ya cika da wani abu,anya
batayi kuskuren aurensa ba?,anya ba shirya
wannan abun yayi ba?,anya bawai ya shirya
aurenta bane bawai don fadeela kawai ba?,bai shirya hakan bane anya don ya gasata saboda ta samu kubcewa daga kamfaninsu?. Wannan tunanin ya sake daga mata hankali,amma kuma sannu sannu wata murya daga can gasan zuciyarta ke gaya mata
"Kema kina da taki damar karki wani damu da koma meye ya shirya" famfon ta kunna ta tara hannuwanta ta daurayesu ta kuma dauraye jikinta ta baro kitchen din, kamar zuciyarta zata fashe. Da yake zancan jacob ma ita ina ruwanta da wani kukunsa,bashi ya ajeshi ba?, shi yaga zai iya,amma itakam ba zata dauki wannan abubuwan ba sam,don ba wannan auren suka tsara zasuyi shi da ita ba.
*HUGUMA*
* TABARMAR KASHI_*
Book 02 Page 15
Kayan jikinta ta zare kaf ta shiga wanka,tanata qoqarin controlling kanta da fushin da yakeson taso mata a kansa,batason taje wajen maji fuskarta da wani yanayi maras dadi. Cikin miti hamsin ta kammala Shiryawa cikin wata qawatacciyar lallausar atamfar exclusive super me matugar kyau da tsari, dinkin tea boubou akayi mata wanda ya zauna mata a jiki qwarai da gaske, ya kuma fidda sigar kyau da dirin da Allah yayi mata,siririyar sarqar dake wuyanta ta gara fidda tsaho da hasken wuyanta. Medium chantilly vail ta yafa wanda ya dace qwarai da shigarta,ta wadata iikinta da turarukanta masu sanyin qamshi. Har tayi taku biyu gaba qafafunta sanye da wasu plate shoes na kamfanin saint Laurent sai ta dawo ta tsaya gaban mudubin tayi folding hannayenta a qirji,kenan yanzun tare dashi zasu jera zuwa cikin gidan?. Qaramin tsaki taja tana juya abun cikin ranta,ita sam ko hanya batason hadawa dashi,duka yadda ma ta lissafa abubuwan yadda zasu kasance sunata zuwar mata da sabanin hakan,totally ma bata taba kawowa zatayi koda rabin kwana bane a sassansa bare kwana guda cur,saidai ta riga ta tsarama kanta yadda komai zai tafi,bata yarda da wannar tsarin ba.
Duk da tare suke da jibril suna tattaunawa akan ayyukan da ya fara a Australia ya barosu ya taho nan,amma hankalinsa yana kan agogon hannunsa,lokaci lokaci sai ya daga ya duba,ransa yana sake baci. Ya tsani jira, kuma yana tsammanin ya sanar mata zasu shiga maji na son ganinta. Sam baiso ma main ta umarci ganinsu a tare ba,to amma yadda ya fuskanci maji na cikin murna matuga da auren nasa,bayason sam abinda zai tauye wannan farincikin nata.
Mintunan da ya diba mata suna cika ya miqe hannayensa zube a aljihun wandonsa yana yiwa jibril bayanin abinda zai tattara masa ya kuma tura masa duka bayanan ta email,sannan kai tsaye ya fice daga falon zuwa farfajiyar gidan yana takawa majestically kamar yadda ya saba.
Dab da zai isa ainihin sassan gidan nadeeya ta fito dauke da wasu trays. Har zata gota taji husky voice din nan nasa na kiranta. Da sauri kuma cikin murmushi ta sauya akalarta zuwa gareshi,idanunta a kan miskilar fuskar nan da kullum take a dinke tsaf,banda ita,kaf duniya batajin akwai wadda ke iya tunkararsa haka,sau da dama ita dinma yana mata kwarjini,wannan dalilin ne ya sanya ko yaya tayi masa wani laifi take shiga uku,iya idanunsa kadai sun isa sakaka a tara
"Good morning yaa moha"
"Morning" ya amsa mata a taqaice yana duban trays din
"Kayan dasu banaan sukayi breakfast ne na debo,kasan sun wuce"
"Ban tambaya ba.. ki wuce ki taho da
ita, kusameni a nan zamu shiga tare" ya fada cikin basarwar nan tasa. Dadi ne ya Kama nadeeya,dama tun dazun take jiran shigowarsu,don ta matsu taga aunty N din,fadeela kuwa baccin daya debeta da safen shi ya kawo sauqin rigimarta,maji ta hana kowa zuwako kai abinci ma tace a gyalesu tunda akwai cook a sassan. Cikin azama ta qwalawa daya daga cikin masu aikin gidan kira,ta qaraso ta jingina mata trays din tayi gaba
"Idan kuka dade ranki ne zai baci" ta jiyo muryarsa, saita gyada kai tana qara hanzari
kadan.
Muryar nadeeya da taji tana sallama bayan knocking din da take mata ya sanyata miqewa tana murmushi,ta isa bakin qofar ta bude.
Rungume juna kawai sukayi,fuskar nadeeya cike da fara'a kamar wadda ta shekara bata ga sãahar din ba
"Ina faddee na?"
"Tayi baccin gajiya,tun da safe tafarka tana rigimar zuwa gurinki,amma maji tace ba yanzu ba,babu wanda zai tasheku" murmushi säahar ta saki tana in nauyi da kunyar majin tun kafin ma su hadu
"Yaa moha ne yace muje nayi miki jangora,yana jiranki a bakin part dinmu" nadeeya ta fadi tana qarewa sãahar kallo.