Sashe 27
Tabarmar Kashi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kujera daya taja ta zauna cikin kujeru shiddan dake zagaye da mulmulallen dining table din me wani irin siffa da tsari,a gurguje Noah cook din nasa ya kammala zuba komai bayan ya zube a qasa ya gaidata,ya sauka da sassarfa yana barin parlor din zuwa kitchen don ya tsaftaceshi hadi da kammale komai kamar yadda ya saba a duk sanda ya kammala girkawa uban gidan nasa abinci,daya daga cikin dokokinsa daya kafa masa akan tsafta ne,baya qaunarta sam sam,sai kuma akayi sa'a shima Noah din gwanin tsafta ne dama.
"Kunyi waya da maji kuwa a kwanan nan?" Ta tambayeshi da kulawa,kamar ya dago kansa ya kalleta saboda ambatar sunan da tayi,wanda hakan ya tuna masa da mafarkinta da yayi a daren jiya,sai kuma yaci gaba da diban chips da yakeyi a fork
"Bamuyi ba,bata kirani ba" boyayyar ajiyar zuciya ta sauke,duk da hakan batajin nutsuwa a tattare da ita,shurun maji ta tabbatar bawai yana nufin tabar mata toufeeq bane,hakanan a duk sanda shurunta ya tashi maido da amsa......yana magana ne cikin amo da amsa kuwwa me qarfi,irin qarfin da ita kanta takejin sautin saman jiki da zuciyarta. Ta sani,ba sanin jiya ko yau ba......itadin jarumar macace,wadda bata yarda da faduwa saarewa ko gajiyawa ba,wannan dalilin ne ya sanya har yanzu burinkan mommy qarama ya gaza kaiwa ga gaci,duk da ta cimma nasara da galaba masu yawa a kanta
"Ka qoqarta kayi kiranta" kai kawai ya gyada mata,shuru ya sake ratsa tsakani,tana mamakin yadda har yau bai iya doguwar hira da ita ba,duk da tana data cewa da yawa cikin al'amuran rayuwarsa
"Nace ba" ta sake fada tana fifita masa tea din don ta saisaita zafinsa,qwayoyin idanunsa kawai ya daga ya kalleta ba tare da yace komai ba har zuwa sanda ya janyesu. Janyesun da yayi ne ya qara mata qwarin gwiwa,idanunsa na dabanne,haka kallon dake cikinsu,suna da kwarjini wanda har yau idan ya dubeta tana jin hakan sosai yana tabata
"Yaruwarka HASEENA,nace kuna gaisawa kuwa?" Sosai tambayar tata ta bashi mamaki,ita kanta daya kalleta sai taga tambayar kamar bata hau dai dai ba,tunda tasan kome yake akwai tsakaninsu
"Bani da lokacin biyewa shirmenta" ya amsa a taqaice. Yanason ya bawa hajiya qaraman haske amma kuma shi din bame sanin yadda zaiyi magana me tsaho bane,a ko yaushe yakanyi magana ne a dunqule,indai bamai matuqar muhimmanci ba,shine zai zauna bayani.
Murmushi hajiya qarama ta saki tana tura masa cup din tea din
"Me kakeso na gayawa daddynka?" Ta sake jefa masa tambayar tana dubansa. Bai amsa ba har sai daya kusa cinye abinda ke bakinsa sannan ya miqe alamun ya gama kenan
"Ya kamata ya fahimceni don Allah" shine amsar daya bata,saiya ciri tissue guda daya ya soma sauka,da kallo ta bishi,sannan daga bisani tace
"A dawo lafiya,Allah ya tsare" taci gaba da kallonsa har ya fita daga dining room din. Dubanta ta dawo dashi inda ya tashin,ta jijjiga kai,sai kuma murmushi ya kubce mata,tadan daki table din kadan sannan itama ta miqe ta fice a nutse cikin qasaitaccen takunta.
***********Kamar kowanne lokaci,yau yadan saba lokacin dawowarsa,don bai shigo gidan ba sai bayan sallar magariba,bayan sun tsaya sunyi sallah a masallacin dake gine daga farkon layinsu.
A kullum itace mutum ta farko da yake fara nema idan ya shigo gidan,yau dinma hakanne,sassansu ya wuce kai tsaye,ya samu baaba ramatu tana gyara kayan ruwa lemo da ice cream kala kala da yake zubewa fadeela a fridge din.
"Barka da dawowa yallabai" tafada cikin mutuntawa,cikin girmamawa shima ya amsa mata,tun kafin ya tambaya kuma ta amsa masa
"Tana ciki ita da hajiya qarama" ta nuna hanyar da zata sadashi da bedrooms dinsu,baice komai ba yaci gaba da takawa da 'yar sasaarfa zuwa dakin,yanajin yadda gajiya takebin gabbansa.
A nutse tare kuma da sallama ya tura qofar dakin,hajiya qarama na tsaye goye da hannayenta,fadeela da sabuwar nannynta na daga bakin toilet,nannyn tana tsane mata jiki da towel.
Sallamarsa kadai ta zaburar da ita,ta watsar da towel din ta tako da gudu,sai ya durqusa mata kamar yadda ya saba,ya bude mata hannayensa ta shige tana fadin
"Oyoyo" murmushi hajiya qarama ta saki
"Shikenan,mun huta da complain din daddy yayi late" siririn murmushin da ba kasafai ake ganinsa akan fuskarsa ba ya saki,wani irin sirrintaccen kyansa ya bayyana
"An dawo lafiya?,ina nan ina sake nunawa nannynta yadda zata dinga kula da abubuwa,bana fatan a sake samun matsala daga kanta" hajiya qarama ta fada,sai ya jinjina kai,yana maida hankalinsa ga fadeela data dauko wani kwali ta miqo masa
"Mommy qarama ce ta bani,kai nake jira ka dawo ka hadamin" karban kwalin yayi hannu bibbiyu
"I hope kince mata kin gode?" Kai ta gyada cike da zumudi
"Good,me zai hana ki bawa mommy ta qarasa ladanta?" Kafada ta noqe,kafin tace komai ma mommyn ta daga hannunta sama
"Inaaa,wannan kuma aikinku ne,nidai na gama nawa tunda na cika alqawari" ta fadi tana dariya gami da nufan qofa
"Allah ya bamu alkhairi tunda tsohonki ya dawo ai kuma shikenan" ta fadi tana ficewa daga dakin.
Duk yadda yaso fa barshi yaje yayi wanka yaci abinci sannan a hada qin yarda tayi,abu daya ta bari akayi,ta kira nanny din nata,tazo ta saka mata kaya,tana riqe da kwalin suka fito zuwa sassansa.
Ta harabar gidan suka sake fitowa maimakon yayi Linkin ya bulla ta sassan nasu,tana gaba yana biye da ita,dai dai sanda qaramar motar da aka gama parking dinta yanzu ke budewa.
Labiba ce ke fitowa,sanye da wani skinny jeans da shirt mai gajeran hannu, high heels ne a qafarta me azabar tsini kamar idan ka takashi da kyau zai iya karyewa,yalolon mayafi ne saman wanda baida maraba da mayafin yaran da shekarunsu ba zasu zarta tsakanin uku hudu zuwa biyar ba
"Hi fadeela" abinda ta fada kenan,idanunta a kansa tana jin wani qunci a ranta,duba daya yayi mata,kallon da bata tunanin ya b'ata second uku yana yi mata shi,ya dauke kansa kamar yaga wani abun qyama
"Hi" yarinyar ta maida mata,sannan ta taka da hanzari tabi bayan babanta da yayi gaba tuni tana kiran ya jirata. Tsaye tayi a wajen har suka bace mata,sai a sanann ta samu qwatar kallonta daga kansu,taja wani dogon tsaki
"Yarinyar sai shegen rashin saurin yarda da sabo fal cikinta,ta kwashe halin tsohonta tsaf" tayi maganar cikin salon mita tana maida murfin motar ta rufe,sannan ta saka mata key tana takawa cikin gidan,zuwa yanzu ta fara tuqewa,zuciyarta ta fara gazawa daga yadda ganinsa yake neman fara yi mata wuya,ta jigata sosai da yadda a yanzun ya sake daure mata fiye da baya. A baya koda zai watsar da ita,koda bazai kulata ba,koda bazai kalleta ba amma bazai kyaret ba,bai kuma taba shata mata layin zama inda yake ba,saidai yayi kamar baisan da ita a wajen ba,ita kuma ko babu komai iya hakan ma tasan wata alfarma ce ta samu,wadda dubban matan dake yawo,suke kamar zasu mutu a kanshi basu samu hakan ba,ko babu komai tana samun daman zama ta kalleshi iya son ranta.
Sai daya tsaya ya hada mata komai,ta sake tubure masa sai daya zauna suka fara yi tare sannan ta barshi ya shiga ciki,wanka ya fara yi,ya dawo ya shirya cikin gajerun pajamas.
Yana tsaka da taje kansa wayarsa ta dauki tsuwwa. A nutse ya jawo wayar yana duba me kiran,MAJI shine ya bayyana saman screen din,sai ya ajjiye comb din hannun nasa,ya jawo stool ya zauna akai yana daga kiran.
Sassanyar muryar dattijuwar,dake cike da wani irin amo dake nuna zallar sanyinta koda a yanayi na halitta ma,tayi cikakkiyar sallamar data saka zuciyarsa dokawa,ya lumshe idanunsa yana amsa sallamar tata,tare da qoqarin tuno watannin da ya shafe ba tare daya kirata din ba
"Ka manta dani ko moha?" Ta kirayeshi da sunan da ita kadai ke kiransa dashi,kuma koda a wani guri yaji wannan sautin ya tabbatar ita dince,ko kuma wani dake da alaqa da ita.
Cikin tsananin jin kunya da nauyinta ya motsa labbansa
"Kiyi haquri" ya fada a sanyaye,qaramin murmushi ta saki,ta saba da jin wannan kalmar ta ban haquri daga bakinsa,har batasan iya adadi ba,bada haqurin da kuma ba wai yana nufin ya daina bane,wani abu ne da yake faruwa tsahon shekaru masu yawa,wanda batasan ranar yankewarsa ba,duk da cewa idan har ta bugi qirji ta kuma daga hannuwanta da sunan samun nasara ba shakka batayi laifi ba.
Cikin wani irin rashin sakewa da kuma rashin sabon da baisan daga ina yake taso masa ba a duk inda suke waya ya fara gaisheta,saidai kuma cike da girmamawa ne
"Ina fatan komai yana lafiya?"
"Alhamdulillah"
"Ma sha Allah,kada kayi wasa da addu'a a dukka wani gaba ta rayuwarka,komai yana da lokaci,kuma nan kusa nake fatan samun wani haske da fatahi daga rayuwarmu gaba daya,ina jikata?" Ta tambayi fadeela cike da shauqin son jin muryarta,wata irin qauna me gauraye da tausayi takewa yarinyar. 'Yar halak din kamar tasan ita ake nema kuwa,sai gata ta buda qofar dakin riqe da games dinta tazo kawo qorafi. Kai tsaye ya miqa mata wayar
"Maji ce" ya fada qasa qasa,saita ajjiye kayan hannun nata duka a qasa,ta tako da sassarfa ta karbi wayar.
Gefe ya koma ya harde hannayensa yana kallon yadda suke waya da maji,kamar sun san juna sosai da sosai,duk da batasan maji ba,amma akwai wanda wani irin sabo tsakaninsu qwarai da gaske,tasan maji a baki kamar me. Lokaci kadan tama manta da daddyn nata dake tsaye,hira suke abinsu,kamar ba daga wata qasa maji din ke kira ba,bata jin katinta sam da take yawan qonawa akan fadeela.
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400
Pay at👇
1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim
Sai katura shedar biyanka anan👇
09032345899
Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070
VIP🔥💯
Zafin kai 3k
Furar danko 3k
Tabarmar kashi 3k
Bakon munafuki 3k
*Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din*
+22799643131
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
[8/17, 6:49 PM] +234 806 578 4295: *H U G U M A*
*_TABARMAR ƘASHI_*💔
https://arewabooks.com/u/huguma
Page 24
Lokaci kadan tama manta da daddyn nata dake tsaye,hira suke abinsu,kamar ba daga wata qasa maji din ke kira ba,bata jin katinta sam da take yawan qonawa akan fadeela.
"Kunyi waya da maji kuwa a kwanan nan?" Ta tambayeshi da kulawa,kamar ya dago kansa ya kalleta saboda ambatar sunan da tayi,wanda hakan ya tuna masa da mafarkinta da yayi a daren jiya,sai kuma yaci gaba da diban chips da yakeyi a fork
"Bamuyi ba,bata kirani ba" boyayyar ajiyar zuciya ta sauke,duk da hakan batajin nutsuwa a tattare da ita,shurun maji ta tabbatar bawai yana nufin tabar mata toufeeq bane,hakanan a duk sanda shurunta ya tashi maido da amsa......yana magana ne cikin amo da amsa kuwwa me qarfi,irin qarfin da ita kanta takejin sautin saman jiki da zuciyarta. Ta sani,ba sanin jiya ko yau ba......itadin jarumar macace,wadda bata yarda da faduwa saarewa ko gajiyawa ba,wannan dalilin ne ya sanya har yanzu burinkan mommy qarama ya gaza kaiwa ga gaci,duk da ta cimma nasara da galaba masu yawa a kanta
"Ka qoqarta kayi kiranta" kai kawai ya gyada mata,shuru ya sake ratsa tsakani,tana mamakin yadda har yau bai iya doguwar hira da ita ba,duk da tana data cewa da yawa cikin al'amuran rayuwarsa
"Nace ba" ta sake fada tana fifita masa tea din don ta saisaita zafinsa,qwayoyin idanunsa kawai ya daga ya kalleta ba tare da yace komai ba har zuwa sanda ya janyesu. Janyesun da yayi ne ya qara mata qwarin gwiwa,idanunsa na dabanne,haka kallon dake cikinsu,suna da kwarjini wanda har yau idan ya dubeta tana jin hakan sosai yana tabata
"Yaruwarka HASEENA,nace kuna gaisawa kuwa?" Sosai tambayar tata ta bashi mamaki,ita kanta daya kalleta sai taga tambayar kamar bata hau dai dai ba,tunda tasan kome yake akwai tsakaninsu
"Bani da lokacin biyewa shirmenta" ya amsa a taqaice. Yanason ya bawa hajiya qaraman haske amma kuma shi din bame sanin yadda zaiyi magana me tsaho bane,a ko yaushe yakanyi magana ne a dunqule,indai bamai matuqar muhimmanci ba,shine zai zauna bayani.
Murmushi hajiya qarama ta saki tana tura masa cup din tea din
"Me kakeso na gayawa daddynka?" Ta sake jefa masa tambayar tana dubansa. Bai amsa ba har sai daya kusa cinye abinda ke bakinsa sannan ya miqe alamun ya gama kenan
"Ya kamata ya fahimceni don Allah" shine amsar daya bata,saiya ciri tissue guda daya ya soma sauka,da kallo ta bishi,sannan daga bisani tace
"A dawo lafiya,Allah ya tsare" taci gaba da kallonsa har ya fita daga dining room din. Dubanta ta dawo dashi inda ya tashin,ta jijjiga kai,sai kuma murmushi ya kubce mata,tadan daki table din kadan sannan itama ta miqe ta fice a nutse cikin qasaitaccen takunta.
***********Kamar kowanne lokaci,yau yadan saba lokacin dawowarsa,don bai shigo gidan ba sai bayan sallar magariba,bayan sun tsaya sunyi sallah a masallacin dake gine daga farkon layinsu.
A kullum itace mutum ta farko da yake fara nema idan ya shigo gidan,yau dinma hakanne,sassansu ya wuce kai tsaye,ya samu baaba ramatu tana gyara kayan ruwa lemo da ice cream kala kala da yake zubewa fadeela a fridge din.
"Barka da dawowa yallabai" tafada cikin mutuntawa,cikin girmamawa shima ya amsa mata,tun kafin ya tambaya kuma ta amsa masa
"Tana ciki ita da hajiya qarama" ta nuna hanyar da zata sadashi da bedrooms dinsu,baice komai ba yaci gaba da takawa da 'yar sasaarfa zuwa dakin,yanajin yadda gajiya takebin gabbansa.
A nutse tare kuma da sallama ya tura qofar dakin,hajiya qarama na tsaye goye da hannayenta,fadeela da sabuwar nannynta na daga bakin toilet,nannyn tana tsane mata jiki da towel.
Sallamarsa kadai ta zaburar da ita,ta watsar da towel din ta tako da gudu,sai ya durqusa mata kamar yadda ya saba,ya bude mata hannayensa ta shige tana fadin
"Oyoyo" murmushi hajiya qarama ta saki
"Shikenan,mun huta da complain din daddy yayi late" siririn murmushin da ba kasafai ake ganinsa akan fuskarsa ba ya saki,wani irin sirrintaccen kyansa ya bayyana
"An dawo lafiya?,ina nan ina sake nunawa nannynta yadda zata dinga kula da abubuwa,bana fatan a sake samun matsala daga kanta" hajiya qarama ta fada,sai ya jinjina kai,yana maida hankalinsa ga fadeela data dauko wani kwali ta miqo masa
"Mommy qarama ce ta bani,kai nake jira ka dawo ka hadamin" karban kwalin yayi hannu bibbiyu
"I hope kince mata kin gode?" Kai ta gyada cike da zumudi
"Good,me zai hana ki bawa mommy ta qarasa ladanta?" Kafada ta noqe,kafin tace komai ma mommyn ta daga hannunta sama
"Inaaa,wannan kuma aikinku ne,nidai na gama nawa tunda na cika alqawari" ta fadi tana dariya gami da nufan qofa
"Allah ya bamu alkhairi tunda tsohonki ya dawo ai kuma shikenan" ta fadi tana ficewa daga dakin.
Duk yadda yaso fa barshi yaje yayi wanka yaci abinci sannan a hada qin yarda tayi,abu daya ta bari akayi,ta kira nanny din nata,tazo ta saka mata kaya,tana riqe da kwalin suka fito zuwa sassansa.
Ta harabar gidan suka sake fitowa maimakon yayi Linkin ya bulla ta sassan nasu,tana gaba yana biye da ita,dai dai sanda qaramar motar da aka gama parking dinta yanzu ke budewa.
Labiba ce ke fitowa,sanye da wani skinny jeans da shirt mai gajeran hannu, high heels ne a qafarta me azabar tsini kamar idan ka takashi da kyau zai iya karyewa,yalolon mayafi ne saman wanda baida maraba da mayafin yaran da shekarunsu ba zasu zarta tsakanin uku hudu zuwa biyar ba
"Hi fadeela" abinda ta fada kenan,idanunta a kansa tana jin wani qunci a ranta,duba daya yayi mata,kallon da bata tunanin ya b'ata second uku yana yi mata shi,ya dauke kansa kamar yaga wani abun qyama
"Hi" yarinyar ta maida mata,sannan ta taka da hanzari tabi bayan babanta da yayi gaba tuni tana kiran ya jirata. Tsaye tayi a wajen har suka bace mata,sai a sanann ta samu qwatar kallonta daga kansu,taja wani dogon tsaki
"Yarinyar sai shegen rashin saurin yarda da sabo fal cikinta,ta kwashe halin tsohonta tsaf" tayi maganar cikin salon mita tana maida murfin motar ta rufe,sannan ta saka mata key tana takawa cikin gidan,zuwa yanzu ta fara tuqewa,zuciyarta ta fara gazawa daga yadda ganinsa yake neman fara yi mata wuya,ta jigata sosai da yadda a yanzun ya sake daure mata fiye da baya. A baya koda zai watsar da ita,koda bazai kulata ba,koda bazai kalleta ba amma bazai kyaret ba,bai kuma taba shata mata layin zama inda yake ba,saidai yayi kamar baisan da ita a wajen ba,ita kuma ko babu komai iya hakan ma tasan wata alfarma ce ta samu,wadda dubban matan dake yawo,suke kamar zasu mutu a kanshi basu samu hakan ba,ko babu komai tana samun daman zama ta kalleshi iya son ranta.
Sai daya tsaya ya hada mata komai,ta sake tubure masa sai daya zauna suka fara yi tare sannan ta barshi ya shiga ciki,wanka ya fara yi,ya dawo ya shirya cikin gajerun pajamas.
Yana tsaka da taje kansa wayarsa ta dauki tsuwwa. A nutse ya jawo wayar yana duba me kiran,MAJI shine ya bayyana saman screen din,sai ya ajjiye comb din hannun nasa,ya jawo stool ya zauna akai yana daga kiran.
Sassanyar muryar dattijuwar,dake cike da wani irin amo dake nuna zallar sanyinta koda a yanayi na halitta ma,tayi cikakkiyar sallamar data saka zuciyarsa dokawa,ya lumshe idanunsa yana amsa sallamar tata,tare da qoqarin tuno watannin da ya shafe ba tare daya kirata din ba
"Ka manta dani ko moha?" Ta kirayeshi da sunan da ita kadai ke kiransa dashi,kuma koda a wani guri yaji wannan sautin ya tabbatar ita dince,ko kuma wani dake da alaqa da ita.
Cikin tsananin jin kunya da nauyinta ya motsa labbansa
"Kiyi haquri" ya fada a sanyaye,qaramin murmushi ta saki,ta saba da jin wannan kalmar ta ban haquri daga bakinsa,har batasan iya adadi ba,bada haqurin da kuma ba wai yana nufin ya daina bane,wani abu ne da yake faruwa tsahon shekaru masu yawa,wanda batasan ranar yankewarsa ba,duk da cewa idan har ta bugi qirji ta kuma daga hannuwanta da sunan samun nasara ba shakka batayi laifi ba.
Cikin wani irin rashin sakewa da kuma rashin sabon da baisan daga ina yake taso masa ba a duk inda suke waya ya fara gaisheta,saidai kuma cike da girmamawa ne
"Ina fatan komai yana lafiya?"
"Alhamdulillah"
"Ma sha Allah,kada kayi wasa da addu'a a dukka wani gaba ta rayuwarka,komai yana da lokaci,kuma nan kusa nake fatan samun wani haske da fatahi daga rayuwarmu gaba daya,ina jikata?" Ta tambayi fadeela cike da shauqin son jin muryarta,wata irin qauna me gauraye da tausayi takewa yarinyar. 'Yar halak din kamar tasan ita ake nema kuwa,sai gata ta buda qofar dakin riqe da games dinta tazo kawo qorafi. Kai tsaye ya miqa mata wayar
"Maji ce" ya fada qasa qasa,saita ajjiye kayan hannun nata duka a qasa,ta tako da sassarfa ta karbi wayar.
Gefe ya koma ya harde hannayensa yana kallon yadda suke waya da maji,kamar sun san juna sosai da sosai,duk da batasan maji ba,amma akwai wanda wani irin sabo tsakaninsu qwarai da gaske,tasan maji a baki kamar me. Lokaci kadan tama manta da daddyn nata dake tsaye,hira suke abinsu,kamar ba daga wata qasa maji din ke kira ba,bata jin katinta sam da take yawan qonawa akan fadeela.
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400
Pay at👇
1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim
Sai katura shedar biyanka anan👇
09032345899
Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070
VIP🔥💯
Zafin kai 3k
Furar danko 3k
Tabarmar kashi 3k
Bakon munafuki 3k
*Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din*
+22799643131
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
[8/17, 6:49 PM] +234 806 578 4295: *H U G U M A*
*_TABARMAR ƘASHI_*💔
https://arewabooks.com/u/huguma
Page 24
Lokaci kadan tama manta da daddyn nata dake tsaye,hira suke abinsu,kamar ba daga wata qasa maji din ke kira ba,bata jin katinta sam da take yawan qonawa akan fadeela.