← Book details Tabarmar Kashi Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 111 OF 171

Sashe 111

Tabarmar Kashi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Ki koma dasu gida,bana da enough time da zan iya cin
abinci har haka a office" ya bata amsa yana maida file
din tare sa cirowa sãahar din na gasansa daya tabbatar
shi take nema. Tana karba ta soma takawa zata bar
gurin,lokacin meenal ke maida kwanukanta cikin
kwandon tana jin wani bacin rai ranta kamar zai fashe.
Bata taba zaton zai watsa mata gasa a ido ba yace ta
koma da abincin ba,ta hada komai a gaggauce ta nufi
hanyar fita tana qoqarin danne fushinta da hawayen da
ya cika mata idanu,saboda batason matarsa taga
karayarta. Meenal na fita tabi sahunta,saidai kafin takai
ga fita ya amsa mata zancan dauko fadeela daga
school,har yanzu ransa na susa,tare da jin bacin rai da
mamakin yadda ameesha ta samu number wayar office
dinsa bayan yayi blocking nata a dukka wani layi da
yasan zata iya samunsa.

"Fadeela nada driver,so ba buqatar kije daukota,ki tsaya
kiyi aikinki" waiwayowa tayi ta kalleshi sosai,sai lokacin
taga yadda yanayin fuskarsa ya canza da kyau

"Ba dole bane ace driver kullum shike da alhakin
jigilarta,daga yau shima na soke wannan saidai idan da wani dalili me qwari" barin aikin da yakeyi yayi, ya dauke hannunsa yana soke yatsunsa guri guda, idanunsa a kanta. Cikin ransa yana jin kamar ba wannan aikin ya kamata ta bawa muhimmanci haka ba,yayin da wani sashe na zuciyarsa kuma yake son daga martaba da kimar abinda tayin tare da son gamsar dashi

"Zauna muyi magana" yayi furucin cikin rashin son wasa a fuskarsa. Kai tadan dauke, kamar ba zata zauna ba kuma ta dosana kadan a saman kujerar

"Kome zakiyi kiyi qoqarin kare martabar hajiya,saboda ita din kamar maji take a gurinmu" kai ta girgiza

"Ba maji bace,ba kuma zata taba zama maji ba,am sorry to say ban yarda da kowa ba akan fadeela,saboda nayi experiencing wani abu da yaso tarwatsa rayuwata shigen abinda fadeela ke shirin fuskanta daga gurin mutumin da yafi kowa kusanci dani" ta qarashe maganar muryarta tana rawa. Har cikin jikinsa yaji wani abu ya tsarga masa,ta miqe tana qoqarin boye qwallarta,batason zubda hawaye a gabansa

"¡ have to go" kamar bazai amsa mata ba sai taga ya mige,ya tura kujerarsa baya ya fito a hankali daga gurin ya zauna saman resting chair yana maida takalminsa,ya daura agogonsa sannan ya dauki wayoyinsa da system dinsa sannan yace

"Let's go" sosai tayi mamaki, saboda bata taba kawowa zaice suje din ba. Danne mamakinta tayi tayi gaba yana biye da ita a baya.

A hankali take takawa da irin takunta nan qafafunta akan tsari,wanda sai kayi tsammanin tana sane take shirya takun nata daya bayan daya. A hankali a hankali sai taji kamar gafafunta suna neman hardewa wannan va sanya ta sake rage saurinta sannu a sannu har ya cimmata suka dai daita kafada. Kusan a tare suka daga idanu suka kalli juna,sai kuma kowa ya dauke kansa yaba basarwa, itakam harda qarin matsawa gefe.

Ihun murna kawai fadeela tadinga saki sanda taga sãahar harda abby dinta wai sun biyo daukarta,abinda bata taba samu ba kenan. Yana zaune vana kallonsu ta cikin glass din yana jin wani farinciki na ratsashi saboda walwalar da ya gani saman fuskar fadeelan,wai me ya hanashi yin hakan shi tsahon shekarun da suka shude? ya barwa driver komai da komai na hidimar daukota da kaita?. Ido ya lumshe yana jin wani farinciki.

Duk yadda yaso ga dannewa amma ya kasa sai da ya furta

"Thank you"sanda take maida murfin motar tana rufewa.
Cike da mamaki ta kalleshi sai kuma ta basar

"It's my pleasure" ta amsa masa tana dire school bag din fadeela da tuni ta haye jilkin Abby dinta tana cewa yau itama 'van class dinsu sunga abby dinta da mammanta sunzo daukarta kamar yadda ake daukar kowa.

Sanda suka isa gida ko sassanta bata shiga ba suka wuce sashensu, nadeeya daketa zuba idanun dawowarsu ta tarbesu suka dunguma,shi daya ya wuce ciki, sai daya shiga yaga dining wayam sannan ya tuna Jacob fa bava nan, garamin tsaki yaja ya wuce bedroom dinsa. Duk abubuwan daya aiwatar tun daga wankansa canza kaya da fresh milk da yasha ba hakan bai mantar dashi tunanin dake magale a kwanyarsa ba,meye yasa tace bata yarda da kowa ba? me yasa wani irin rashin jituwa yake gudana tsakaninta da hajiya qaraman cikin dan lokaci kadan?,da wannan tunanin ya gama hutunsa cikin sashen,har aka kirayi magariba yayi alwala suka fita sallah shi da jibril. Bayan ya dawo sallar sashen hajiya qarama ya shiga,don bayan ya fito jibril ya shaida masa sau uku tana aikowa kiransa, ba'a gaya masa bane sabida sunsan dai dai lokacin hutawa yakeyi.

Yaji dadi da bai samu meenal ba a sassan,ya samu guri ya zauna yana gaidata

"Ka kusa fin garfina ai toufeeq" hajiya ta fada tana tara hawaye cikin idonta. Mamaki abun ya bashi qwarai

"Me kuma ya sake faruwa,i thought kun gama magana
da Dr ko akan komai?"

*HUGUMA*

* TABARMAR KASHI *

Book 02Page 27

"Amma toufeeq kamar ni?, meye amfanina a cikin gidan idan ban kula da fadeela ba" ido ya lumshe sannan ya bude,ya gaji gaba daya bayason wani daru

"Karki wani damu, tattaromin magungunan ki bani, ni zan ci gaba da kula da hakan" a bazata maganar tazo mata,har hakan yaso ya rudata amma ta daure

"Haka ma zaka ce dani toufeeq? yayi kyau shikenan, kaje kawai" ya dauka ya kawo qarshen maganar, amma sal ta sake cewa

"ya kuke ciki da meenal?,dazu ta dawo tana kuka,ta bata lokaci tana bada direction na abincin da za'a dafa maka,sai kuma naga da takai maka babu abinda ka taba a ciki,me yake faruwa?" Idanunsa yadan rufe kadan,a yadda ya fuskanci yanayinta ko meye zai fada mata a yanzun zata bata masa lokacine ta qara masa hayaqi akai, saidai duk da haka yana bugatar ya datse dabi'ar daukar abinci takai masa company,alhalin suna da kitchen, sannan kowanne kalar abinci yakeso yana daga office jibril zai iya masa order dinsa

"Mun fita da madam dauko fadeela daga school" idanu tadan bude da kyau tana kallonsa. Tunda suke dashi bata taba jin ranar da ya zarce daga office dauko fadeela makaranta ba sai yau,yau din kenan har hakan ta fara?, har yarinyar taci nasarar juyar masa da hanakali da sauya masa ra'ayi da tsari?,duk kuwa da tarin taurin kansa da kafiyarsa akan tsarinsa?, wanda ko ita ba kasafai takecin nasarar canzashi ba?. Bata gama wannan mamakin ba ta ganshi ya miqe sannan yace

"So please hajiya ki fahimtar da ita basai tayi wahalar kawomin ba,i will be alright, bazan rasa duk abinda nake bugata ba" mamaki ya hanata cewa komai,shi sam baima wani zurfafa dubanta ba bare ya gane ya dora mata

"Zan wuce ciki.da wuri nakeso na kwanta"

"Jacob baya nan,ko a kai maka dinner?" Ta sake garfin halin fada tana ritsashi da ido tare da son tabbatar da zarginta akan säahar . Hannu yasa ya shafi tattausar sumarsa

"No, ba damuwa,i will get something to eat" sai yayi mata sallama yana ficewa. Labiba da haseena, tabbas yana gab da yi musu mummunan warning din da ko sunansa sukaji zasu san nayi,yana musu kara da alkunya ne kawai saboda iyayensa, hajiya qarama da dr jarma,don kwata kwata baya saka mansura a lissafinsa.

Yana shirin fita a sashen adama na isowa, hankalinta yayi gaba sosai don haka bata lura da shi ba har sai da yayi dab da ita, cikin zafin nama ta kauce masa abinda ya sanya ta bugi bango ledar dake hannunta ta. yage,magungunan ciki suka zubo qasa. Cikin tsananin rudewa tare da tuna kakkausan gargadin da hajiyan tayi mata wajen kula da maganin har zuwa sanda zata kawo mata shi,sai ta sulale a gurin tana tattarosu tana zabga salati.

Kansa ya dauke yana ci gaba da tafiya. Har ya gota yá dawo da baya sakamakon wani tunani da ya darsu a ransa. Akwai masu aiki a gidaje kamar haka da suke ta'ammali da kayan maye qwayoyi ba tare da iyayen gidansu sun sani ba,wasu ma idan aka samu tsautsayi har su koyawa yaran gidan

"Ke.. zo nan" kiran da ya sanya hantar cikin adama juyawa,ta dawo da hanzari ta zube a gabansa

"Wadan nan magungunan fa?"

"Eh... na'am" ta fada a rude tana tuna gargadi na biyu data yi mata,kada ta nuna cewa maganin yana da alaqa da ita ko fadeela

"Uhmmnn" ya fadi yana tsuke fuskar nan tasa me sanya shakka da tsoro a zukatansu

"Ko kin fara shaye shayen muggan qwayoyi?" Ya fada kansa tsaye yana tura hannunsa cikin jallabiyyarsa ganin bata ds niyyar amsawa. Fassarar da yayi matan ta razanata matuqa,har batasan sanda ta daga kai da sauri tana rantse rantse ba

"Wallahi A'ah yallabai,magungunan fadeela ne hajiya tace na karbo daga bakin gate"

"Bakin gate kuma?" Ya tambaya cike da mamaki, saboda yasan duka magungunan da fadeela ke sha ba na nan bane, hasalima order dinsu ake mata na kusan million daya,yana damqasu a hannun hajiya qarama har sai sun qare sannan ya sake yi mata order din da kansa (nasan zakuyi mamaki,maganin million daya?,harma fiye da hakan sukan sha,sannan kamar yadda nace wasu da yawa masu gata a cikin masu lalurar EPILEPSY order magungunan nasu akeyi musu,a qalla a shekara sukan sha maganin million daya din, fatanmu Allah ya rabamu da dukkan wasu cututtukan zamani,ya qaremu da lafiya,su kuma ya basu lafiya,wadanda ya zame musu na
har abada ne kuma rabbi yasa ya zamar musu kaffara

"Eh.. .eh" kai ya jinjina,ko sun qare ne tayi order ba tare data sanar masa ba, sai ya samu kansa da lissafa adadin kwanakin da suka rage su qare din.

Har ya daga qafarsa yaci karo da roba,ya
tsugunna yana dubawa sai yaga daya daga cikin robar
maganin da ya gani ne yanzu,ya waiwaya zai kirayeta
amma tuni har ta bace a gurin,ya juyata a
hannunsa,kwata kwata tasha banban da robar
magungunan fadeela,sai kawai ya jefata a aljihun rigarsa ya wuce.
Chapter 111 · 0% Book details