← Book details So Makamin Cuta Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 56 OF 132

Sashe 56

So Makamin Cuta Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ta sunkuyar da kai kasa batace komai ba
Nan mrs rod ta cigaba, tace
Uhm My daugher ena fatan kinsan nan gidan tamkar gida ne ma ashween, kema zanso ace kin sake jikin ki da kowa don tamkar jini muke

Ta nuna zahida tace ga sis din ki nan,
I hope kunyi setling difrncess din ku,? Jasmine Tayi shiru tavrasa me zata ce.

Mrs rod tace c'mon preety jasmine,pls ki zama mai tausayi da yafiya mana, kinga yar uwan naki tana cikin tashin hankali she needs u.
All of us as a family har dake ya kamata mu yafe ma juna ko?

Nan zahida ta ari bakin maganan tace mum, pls..tana kifi kifi da ido alaman taji kunyar karya.

Jasmine bata lura ba kawai tace bakomai mum, ai na yafe mata komai ya wuce.

Nan mrs rod Ta sake wani sarkakken murmushi tace Am so proud of u.Allah ya miki albarka ,as beautifl as ur hrt..
Ta juya ta kalli zahrod "
Oya ke me ki kace mata zahida
Nan ta dube ta badon ranta ya so ba tace " im sorry hun?
Jasmine Ta gyada kai ta danyi murmushin yake.

Gefen su ashween kuwa ba irin lallabi da kamal bai masa ba sam ,ashween yace shi gaskiya sai dai acanza plan don ba zai amince da komawar zahida gidan sa ba har abada, cewar sa " im tired i want to be with my wife kamal.

Kamal yace haba ash , ai dama nasan duk dan jasmine ne kake cewa haka
amma kasan plan din nan zai wargaje da wuri muddin zahida tana zaune da mrs hidayat ko?me akayi kenan.
Shes already poisoning her mind ita take bata duk wani master plan data ke amfani da shi wajen cutar da mutum

Kar garin kare matar namu fa mu jefa ta cikin mummunan hatsari.

Ashween yace kamar ya fa, tana tare da ni wani hatsari kake nufi kamal,tab ashe ko da duniya zai tashi

Kamal Yace look, to kafa fara cin brain , wai ka na tunanin zahida da mrs hidayat baza su gane jasmine matar ka bace in suna tare ku kuna chan?kaifa ka fada min bala"in kishin da suke tafkwa tsakanin su,

mrs rod ai mahaifiyar ku ce, tafi ku nisan tunani duka, in har zaka iya wasa da hankalin zahrod akan jasmine kasa ni u cant fool mrs hidayat.
Nan ma Ya kalle sa yace
And I dont think zaka so abunda zasu ma jazmine
In suka fahimta matar ka ce. Hiding it is the beat way to protect her now

Ash kwata kwata Baiso hakan ba,Amma sai yayi saurin dake wa yace cewa "ya isa haka toh
C'mon why are u scaring me kamal, ba abunda zai taba min ita.. Sannan ya sauke numfashi yace
Toh dai Naji hakan zamuyi bawani changi, lets just go na barta ma tare da su,

Kamal yyi murmushi yace ko kaifa..c'mon just relax,
In don jasmine ne nasan ba matsala cos she loves u alots zata fahimce ka, kuma kaifa kafi kowa sanin yadda zaka shawo kan matar ka su zauna har komai ya kare.

Yace haka ne,ure right, nan suka dunguma suka shige daga ciki

zahida na zaune tare da jasmine a dayan falo suna kallo kamr shiru kamr ba su ba..

Nan su ash Suka kalli juna da kamal alaman hmm yau kuma

Duk da ma ba magana suke yi ba sai yayi kamr babu komai tsakanin su ,
Kamal yayi gyran murya duka suka juyo suka kalle shi,
Yace yan mata ne haka,
Jasmine ne ya soma maganan tace yay kamal, ena wuni
Yace fine yar kwai, kin kyauta da kika zo ai..
Tayi murmushi

baby, haw far?, yace ma zahida da ta dan daure fuska tana masa hararar wasa,nan ya zauna cikin su
Kadan kadan suka taba hira ,

Idon Ashween kuwa nakan matar sa don har ya lura kamsr ta dan sake kadan,
Shidai Baice komai ba sai daga baya yace ma zahida,
Ena maam take,
Ta wani karairaya murya ta dago tace tana sama dama kai take jira,
Bai amsa ta ba
Ya dawo gefen jasmine a hankali yace ena zuwa tare da dan shafa gefen face dinta a dabarance
itakam sai kallon sa kawai take bata amsa ba

Dakin sama suka tafi da kamal enda madam hidyat ke kwance,
Nan suka gaisa da kamal,
Ta zaunar da su

Surutun ta take wanda ta shirya su tsaf cikin hikima da fasaha da daukar hankalin duk maijin ta,
Ta ce ashween bansan ya zan nuna maka yadda anke jinka araina ba, amma bani da wanda nake jin zan jingina kafada ta akansa yanzu in bakai ba,
Son Ka taimake ni ,ka ji kaina tamkar yadda zaka ji kan mahaifiyar ka

Take zahida with you ka koya mata harkokin gona ko zamu samu mu daga 68% na harkokin mu .da suka zube tsakanin jiya da yau.

I know i have no rights, Kayi hakuri gadara da kai ne ya sa na ce kamin hakan ,kuma naga ure one of the best managers na ranch da plantations A kasar nan.i will be honoured en ka taimaka min son pls.
Ta goge hawayen ta cigaba... tace I lost my children kuma kasan duk maza ne suka tafi, badon haka ba da sai mu bi ta wani wajen,to nayi tunani eya tunani bani da lpyar da zan iya harkan papers a yanzu.
Yanzu Gonan ne kawai zai sake dawo damu kan kafarmu akan lokaci ,dama chan shi ya dago mu tun marigayi alhj abdul fatah rod yana nan
Basu ce komai ba suna binta da ido

Kafin su hankara gani su kayi tayi kasa ta tsuguna gaban sa tace pls ,pleasse
Help me son, help me. Ta rike gwiwan sa tana jimami kalar tausayi.

Kamal ne ya kalle sa alaman me kake jira ne wai... mahaifiyar ka ce fa?

Ko ya ji ajikin sa saima kau daknsa gefe dayayi ma dan lokaci
Nan Ya sa hannu ya dago ta yace
Ai Nayi fushi dake maam,
Ashe har sai kin roke ni na taimaka miki?
C'mon wannan ai ba wani abu bane.
Dont worry ok?take yasa fuskan tausaya mata shima kamar ba shi ba yana fooling dinta da calming words
Wanda yasa kamal jinjina masa aransa yace hmmmm

Nan Tayi murmushin jin dadi tana goge hawayen ta tace Allah ya maka albarka har karshen rayuwar ka son,
I truly love you son,ni dama tun dana fara ganin ka nake jiN ka har ajini na ..ta riko hannun sa dam tace
Kaje duk enda da kaje a duniya ba abunda zai sameka sai alkhairi,

Nan Duka suka amsa da ameen..
Haka shima kamal ta dinga praising din sa da kyar dai sukaa rabu,
AKan zata gaya musu komai da komai game da aikin da duk abunda suke bukata kafin a soma aiki akan gidan gonar na su

Dama Allah Allah jasmine take taga fitowar su don tagaji da zaman kurmayen da suke yi da zahida
Yana zuwa kuwa ya sakar mata murmushi a dabarnce itama ta turo mai baki cikin sigar shagwaba

Me yace ma zahidan ne sai Allah dan a hankali sukayi magana tsawon minti 5 kafin ya ce ma jasmine lets go,
Kishin nan nan aranta amma sai ta dan ji saukin sa yau don sosai ta dan tausaya ma yanayin su zahidan musamman mrs rod..
don Bakaramin wasa da tunanin ta sukayi ba dazu a dakin
Don har maganan zahida zatayi aiki a yola sai da sukadan tsakura mata duk da ma basu ce a gidan ashween zata sake dawowa ba.

Cikin motar suna tafiya Kamal ne kawai ya ishe su da surutu don sai da yasata dan dole ta sa baki a hirar tasu ,
ashween kuma yana jan motar yanata dariya kasa kasa don yawanci hirar tsokana ne da shirme,

Nan Har suka ci abinci tare su ukun a wani bukataria,
Kafin sukayi sallama enda kamal ya dada jaddada mata zai samo mata salma nan ba dada dadewa ba.

Da hakan su ma suka tafi gida
Bayan anyi isha'i, sai 8 ya shigo ya same ta alaman ta gama komai tana shirya musu kayan su na tafiyan goben.

Zama yayi gefe tana nadewa yana sa mata a bags
Yana tsokanan ta tana shaqwabewa
Har aka zo kan tsarabar mamy,
Yace bani naga meye ne aciki wato ke kadai aka sani banda ni ko

Ta damke abun ta tace ah' a , yaya me zakayi da shi
Naga dai duk abun Mata ne aciki yaushe kadawo baby girl?

Abun ya bashi dariya yace nidai abani naga abun matan ,ai in ni ba bby girl bace ena da baby girl,

Hararar sa tayi don inya fadi hakan saita rasa da ita yake yi ko da zahida

Haka ta ki fir ta damke abunta ,yace to bakomi, zan rama

Tace eh ,kawai ka rama ai turare ne anan din ba wani abu ba,

Yace ohhhh kin gwammaci na rama akan naga turaren

A dan tsorace tace ehh,
Ai ko rufe baki batayi ba taga yayi wuf ya kashe wutan dakin guri ya lume dum yayi baki, sai karan Ac
Ai sikinini ta ajiye ledan agefe tayi tsit zuciyan ta na neman fara bugu

Shi kuma saiyayi shiru ya dauke numfashin sa yana gefe yana hangen ta .
Tayi lalume tayi laume ba taji kowa ba

Chan Tace yaya ka tafi ne? Taji shiru.
.ta sake cewa, yaya ena kake ne? Still shiru....na ukun ta karkace murya kalar kuka tace wayyo Allah yaya na..wallhy tsoro nake ji

Shiko Yana shiru yana jin
Ta dariya ya riga ya cika masa ciki
Haka ta cigaba da bare baki tana lalume tana kiran sa cikin kukan shagwaba,

Amma shiru,.jin kukan ya soma yin Tsanani ya tashi ya lallaaba ya janyo ta jikin sa a hakan ma saida ta tsorata tana fizgewa
Ba don taji qamshin jikin nasa ba tayi niyyan kurma ihu ne don tsoro.

Haushi ne ya kamata musamman data ga yana mata dariya,tace shine zaka tafi ka barni kalan wani abu ya kamani ko?

Yace me zai kama ki?.naga abunda kike tsoron Ma ya mutu saura me kuma

Ta murguda baki,ta dada lafewa jikin Sa,
Nan ya dago ta suka haura gado
Shiru Sai safiya kuma,
Chapter 56 · 0% Book details