← Book details So Makamin Cuta Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 50 OF 132

Sashe 50

So Makamin Cuta Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Da dai taso ta dada masa bori sosai ta gigi tashi,sai tayi tunanin intayi hakan taci baya,
tuninta ai zahida zata iya lallaba shi tunda su masoya ne ita kuma a barta tutan babu

Take ta sauke wani munafikin hawaye ta riko hannun sa a sanyaye.
Ji take yadda jikin sa yake karkrwa a hankali don tuni ta gane baya cikin hayyacin sa har yanzu.
Baice mata komai ba
Dago ta yayi ya dada gyara mata mazauni a kirjin sa ya kalmaso ta da hannun sa kafin yace meya faru jasmine,waye ya miki wannan abun.?

Sauke ajiyan numfashi tayi ta dada kankame sa nan ta soma rero masa kanun labarai har da gishiri da sugar, tana yi tana goge hawaye kalar tausayi.

Tunda tafara ya lumshe idon sa, don sai da yaji zillon hawaye na kokarin sauka kan fuskan nasa ga kishin bala'i dake kona shi,wai ma arasa abunda zai taba masa jikin princess dinsa sai kare?

wani hali na daban ya tsinci kansa amma yaki ya bari tasan halin da yake ciki sai da yayi shirun kusan minti 3 sannan ya soma bata hakuri cikin sanyin murya da lallabi
Karshe Yace duk wannan abun laifi na ne ki yafe min kinji?

Ta dago ta girgiza masa kai tace uhm.uhm...ni ma enada laifi yaya, na mata rashin kunya ne enaga shiyasa ta min haka.

A ranshi ya ja tsaki yace' Allah dai ya kare ba na nan a gidan nan da yau sai tayi kwanan asibiti jina jina,, i hate her for this, ya dada kamo ta da kyau sai yace kiyi hakuri dai insha Allahu bana barin kowa ya sake taba ki agidan nan kuma duk zasuji ajikin su

tayi karamin murmushi tace nayi,

Duk da hakan yaci gaba da zubo mata kalaman rarrashin dana kwntar da hankali
Itakam Gyada kai kawai takeyi musamman data ji yace
Ita zata fadi kalar hukuncin da zai ma zahida da karime.

A haka har karfe 11 saura ya buga nan ne yace" you wanna go for some ice cream? yau fa akwai rana sosai

Tana manne da shi Da kyar ta kwakalo yes din cikin jin dadi a ranta. yace to zauna nan kijira ni ena zuwa

Nan ta shiga buga game da wayar nasa wanda yawanci shi tafi gani a yannun sa amma ba salin shi din yake using ba
Nan ya koma dakin ta dauko mata kaya masi kyaw tazo tasa sannan shima ya sauya dressing yace ta biyo sa nan su ka fita gari.

Yawon su suka sha ranar don dama ita bata taba zuwa yolan ba,
Nan ya nuna mata wajaje ya kaita shan ice creams kayan cime cime dai kala kala da dik wani abun da yasan zai dauke mata hankali yasa taji sanyi aranta,
Duk da ba wani make up a fuskan ta sosai yake satan kallon cute face dinta suna tafiya.
Ranar gaba daya ya kashe bainkula kowa ba harta wayar sa , sai da ya tabbatar jasmine ta dawo dai dai da dariyar ta da komai don har karfe 8 na dare suna waje sunje club din snooker da table tennis na manyan mutanen gari nan ma suka tsaya yin game abun su.

Gefe guda kuwa Hankalin zahida ko ya gama tashi ,jin shi shiru shiru tun safe ba ashween bare jasmine

Don basu ga shigowar sa ba kuma basu ga fitar su ba.
Sannan aranta ta tabbata shine kawai ya kunce jasmine ya kashe mata sugar
Ita damuwar ta ma kardai ko jasmine Wani abu ya same ta ne ta shiga uku

Gashi ba abokin shawara ko gulma tariga ta bal bale karime da masifa ta kore ta cikin bacin ran da ba gaira ba dalili
don dama ita ba a mata ta dadi

Yanzun Tunanin makomar ta take
Tasan yau dole akwai chakwakiya mai girma.

Tana tsaye a kan stairs tayi tsuru tsuru,chan ta sama ta hango cook nana tana shigowa sa ledojin shoping.

Cikin ta ne ya soma kulu kalar zawo amma sai ta sauke ajiyayyen numfashi ta sauko kasa

Jasmine Tana gaba yana biyo ta kan layi suka shigo palour
Dai dai itama zahida tana karasowa

Wani mugun kallo ya watsa mata jasmine kuwa don munafurci tayi sauri ta koma bayan sa ta lafe alaman ganin zahidan na bata tsoro

Tam ta rike rigar sa ,tana numfashim karya
Nan bugum zuciyan zahida ya dada harbawa

' baice komai ba ganin itama bakin ta na tsoron buduwa sai ya ce ma cook nana dake saukowa ta kira masa kowa da kowa acikin ma'aikatan gidan

Kafin kace minti 10 duk an hallaro kowa ya rusuna
Kafin nan Tsakanin su da zahida kuma ba wanda ya tanka sai mugayen kallo dayake harba mata

Nan ashween ya ZUba wani mummunan doka da jan kunne akan jasmine,
Akan duk wanda ya taba ta ya dauka tamkar shi yake tabawa.itako Tana gefen sa tayi kifi kifi tana kallon uban kowa musamman zahida data gama kulewa don ko ita bai sa doka akan ta kamar jasmine ba,

Hakuri sosai ma'aikata suke bashi duk da basusan dalilin maganan sa ba.don kuwa iya zaman su da shi ba takuri ba ha'inci.

A gefen Karime kuwa da shike tasha jinin jikin ta tayi lagwas a gefe tsaban yadda cikin ta yake kwalalan tsoro zufa ne ke tsatsafo mata duk da acn dake wajen yana busa sanyi

Nan ya salleme su ita ya dakatar da ita.

Kowa ya tafi aka barsu su hudun a falo.
Dama yana zauna tare da jasmine dinsa a gefe

Nan ne ya dubi zahida yace ' wai me yafaru ne a gidan nan yau tsakanin ki da jasmine?

Taso ta juya kan maganan amma gaba daya bata da gaskiya sai ta soma kame kame bata san ta ena zata bullo ba
Itako jasmine tsaban barikanci zahida tana soma maganan itama ta soma matse ido tana ruwan hawaye tana kukkuni ciki ciki
Tamkar ta san dacewa tana Azalzala masa ciwon haushin abun ne a zuciyar sa ,gashi taki sam ta dena sai ma lafewa take ajikin sa tana kananun magan ganu a hankali

Nan zahida ta birkice ,don jasmine ta riga ta maida abun kamar an zalunci ta sosai ita bata da laifin komai

yana shiru yanajin su har zahida ta rufe baki baice uffan ba
A lokacin ma damuwar sa princess dinsa ta dena kuka ne kawai.

Kan karime ya juya , ya mata tas tas sai kuka takeyi tana neman sa gafara,
Sosai jikin zahidan ya dada karaya ganin karime ta sake karyata zancen nata da reactions din ta.
Don sosai ashween ya bude mata ido wuta wuta, ba ita ba har jasmine din saida ta ji abun aranta,

Nan zahidan ta ari maganan tace
Haba ash ,ya zaka tara mu kana mana deban albarka haka ,ai koma meye ne itama tana da laifi zagi na fa tayi

Nan ne ya daka mata wani figitaccen tsawa yace just shut up ko na sassaba miki,
Na baki dama ne kiyi magana tun farko saboda kece babba da su,but you lied to me saboda haka kar na sake jin bakin ki anan wajen

Ai Tuni ta nitsu idonta ya kawo ruwa,ta kau da kai tana diri

Nan yace anyway ,ai bama ni kukayi wa laifin ba

Ya juyo ya kalli jasmine yace zan cika miki alkwarin ki
Yanzun Me kike so na musu?.

Nan zahida ta juyo a haukace tana kallon sa galala tace tab di jam
ta tabe baki tana kada kai.
ko ya kula,
Jasmine dake binsu da wani munafikin kallo nan ta marairaice fuska ta ce korin su zakayi yaya...ni bazan zauna da su ba.

Yace , shikenan.
Kan ya kara wani abun yaji ance
Ashween !!!!! Zahida ta kira sa fa karfi cikin mamaki da kunan rai.

Ido kawai ya ma jasmine akan ta tashi ta shiga ciki don baya cika son yin rashin m a gaban ta musammab in ma zahidan ne.

Jasmine Ba musu ta tashi tana tafiya kallo daya zaka mata kasan hankalin ta ya kwanta

ciki ciki take dariya tana satan kallon zahida
Ai kuwa suna hada ido ta mata kwalo ta murguda mata baki

Zahidan Da gudu ta yo kanta a zuciye ta finciko ta zata wanka mata mari ashween yayi saurin damko ta
Itama sai tas taji saukar wani lafiyayyen mari a fuskan ta sai da ta tsuguna tsaba hajijiyar dake so ya yarda ita kasa
Nan ma yabi ta da tsawa yace mata
A gaba na?

Bata fasa ba Ta budi baki tana shaking zuciyan ta na fat fat tace ashween ni ka mara?ash...we.

Ya daga mata hannu alaman bayason jin komai sannan Ya ce just leave.
Ki fice min a gida na yanzun nan bana son ganin ki ko da na seconds ne

Bata san lokacin da ta fashe masa da kukan takaici ba ta rasa me zatayi awajen

Dadin karawa ma jasmine din ce manne dashi ta rike masa riga gam don tsoro sai kallon su take zUciyan ta fal fuskan ta dauke da munafikin boyayyen murmushi

Nan ma Ya juya yace ma karime and yhu too ki tattara ki bar min gida na yanzu.

Don wallhy Kuka sake na dawo na ganku anan baza kuji da dadi ba.

Zahida Ai koo jira ya gama batayi ba ta wuce sama a haukace tana kuka

Ko ajikin sa ya ja hannun jasmine sukayi site din su

*ayyah beauty is cryng*.😭😂

*surriem*
[23/08, 05:42] ‪+234 806 071 2446‬: *⚜BRILLIANT WRITERS ASSO🖊*

💔

*SO MAKAMIN CUTA*
_'the sword of evil love'_

_Story and written by_
*SURAYYAHMS*🔥

*DEDICATED TO-*@UMMERHERNY NERSALLAH.

*😹😹😹 my people zahida aka beauty tace baku kyauta mata ba gaskiya ba amana*

*Page▶38*

Zahida dake jin kanta kamar zai bude sai abun ya zamo mata kamar hauka komai yazo gabanta jifa takeyi da shi, ta watsar da nan da fasa nan haka tayi kaca kaca da dakin ta tana kuka.

' ranta ne balbal yana ci da wuta bata iya ma tattara komai ba ta dauki jakar ta da wayan ta tayi saurin dialing call airpot ,maza ta fice a gidan rai a bace bata kula kowa ba.

Cikin daren ta bar garin ba ita da samun dawowa abuja ba sai 1.30 na dare
Chapter 50 · 0% Book details