← Book details Buzu Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 76 OF 78

Sashe 76

Buzu Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Har yau jikinta babu ƙwari sosai, bayan fitarsa ta shiga ta gyara abin da za ta gyara, kawai ta nemi guri ta zauna, tana hutawa wani irin bacci ne ya ɗauke ta a gurin.
Ba ta jima da fara baccin ba, sai ga ta a Libraryn Ƙaisar.
Waiwaye ta fara yi taga ta ina za ta gan shi, sai dai ba ta gan shin ba, sai wata guguwa da ta taso, ta watso mata littafin nan da ta ce ba za ta karanta ba. Ta kalli littafin a gabanta amma ba ta motsa ba, ba kuma ta É—auka ba. Kawai littafin ya buÉ—e kansa da kansa, sai mudubin nan ya haska inda ya buÉ—e É—in.
Sayyid ta gani a tsaye a cikin sahara ana ta harbo masa kibiya ta ko ina, Sultan ta ta gani yana ƙoƙarin tare masa, shi ana samun sa da kibiyar. Har ya fara gazawa aka fara samun Sayyid.
Ya na tsaka da tarewar aka janyo shi aka nufi wata wuta da shi, da cin ta yake gwanin ban tsoro. Ba ta iya ganin fuskar wanda yake jan na shi, saboda ya rufe fuskarsa da rawani.
Gaba É—aya Nana ta gigice ta rintse idanunta tana addu'a kar Allah ya ba wa mutumin nasara, can jin shiru sai ta buÉ—e idonta a hankali.
Sai ta daina ganin wancan lamarin, sai wata taguwa da ake ta É—urawa wasu abubuwa.
Sayyid na zuwa ya kama taguwar ya hau, yana hawa ta din ga walagigi da shi, ta nufi kan wani rami da shi. Zumbur Nana ta tashi, tare da miƙewa tsaye a falon. Zuciyarta sai bugawa take yi da sauri.
Waje ta yi da wani irin hanzari, ta nufi inda ake shirya raƙuman da za a yi hawan da su.
Raƙuman duk jajaye ne, an yi musu wani irin ado, ga su ƙosassu.
Gaba É—aya ta ji ba ta yarda da lamarin ba, ta juya ta sake kwasar hanya ta koma sashen su.
Tana zuwa ta ci karo da shi ya fito, sanye da makamanciyar shigar da ya shigo É—akinta bayan auren su.
Takobinsa na soke a gefen ƙugunsa, babbar rigar jikinsa ta sha aiki.
Kallon Nana ya yi, fuskarta ta nuna rama sosai da sosai.
Nana so take ta yi masa magana amma yana tare da Asal da ta sha kwalliya ita ma, sai hura hanci take yi.
Gaba É—aya yanayinta ya nuna masa a rikice take, kuma magana ce a bakinta.

Har za su gifta inda Nana take ya ce "Sayyid excuse me"

Asal ta waiwayo ta kalli Nana jin ta ce masa Sayyid maimakon Imam.

Ya kalli Asal ya kalli Nana, sai kuma ya yi taku biyu ya matsa daf da Nana, ya sunkuyo daidai tsawonta.
Gaba É—aya sauran barorin da suke gurin ma zubo musu ido suka yi.

"Dan Allah kar ka hau Taguwar nan" Ta yi maganar cikin tsoro muryarta har tana rawa.
Ya ɗaga idonsa ya saka a nata, wanda hakan ya rikita ta, tamkar ba ta taɓa saninsa ba.

Bai ce mata komai ba, ya miƙe ya yi gaba. Asal ta bi shi cikin fushi tana tambayarsa "Wai me ta ce maka?"

Ya numfasa ya ce "Da tana son ki ji, ba za ta zaɓi ta gaya mini ba".

"Imam ban gane ba, mene ne abin da ba za ta faÉ—a kowa ya ji ba?"

"Ai kin san duk wanda yake ƙarƙashina, ina ba shi lokacina na saurare shi. Kar ki manta mutumin da yake da Asal doka ba ta ba shi dama a kan wata wadda ba ƙabilarsa ba, mussaman baƙar fata, kin fi kowa sani na, ki daina saka wani abu a ranki dan Allah"

Ya yi maganar daidai lokacin da suka ƙarasa gurin. Daga nesa Nana take hango an ba shi shayi a kofi, ya karɓa ya shanye, an sake zuba masa ya karɓa ya sha.
Aka cika gurin da kaɗe-kaɗe, juyi suka din ga yi tare da sauran 'yan uwansa Imam, su na wasa da takubbansu, gwanin burgewa. Duk da tashin hankalin da Nana take ciki, sai da abin ya ƙayatar da ita.
Aka jero raƙuman nan, suka din ga kama su su na hawa.
Nana gabanta ya tsananta faɗuwa, cike da ƙwarewa ya kama raƙumin nan ya haye.
Idonsa suka sauka a cikin na Nana, fuskarta ɗauke da damuwa, ya lumshe idanunsa ya saita akalar raƙumin nasa, ya wuce gaba sauran suka bi bayansa.

Mutane suka rufa musu baya, suka kama hanyar barin gidan.
Jiki a sanyaye Nana ta koma.
A tsaye ta jingina a gurin girki, tana tunanin abin da ka iya biyo bayan hawan Raƙumar nan da ya yi.
But Asal ta faÉ—o cikin huci, Nana ko motsawa ba ta yi ba sai bin ta da kallo kawai da ta yi.
Har gabanta Asal ta zo tana huci "Uban me ki ka gaya wa Imam, kuma saboda me za ki din ga kiransa da Sayyid? Ban yi miki gargaÉ—i a kan sa ba?"

Nana ta kalle ta, ta ga kar ta yi wani abun da zai sanya ta kore ta a yanzu, dan haka ta sassauta murya ta ce "Haba ya shugabata, Sayyid da Imam duk abu ɗaya ne ai, yana nufin shugaba, mu a Nigeria Sayyid muke cewa, kema idan ki na so sai na kira ki Sayyada. Kuma me Sayyid zai yi da baƙar mace 'yar Nigeria, ai ramin kura sai 'ya'yanta. Kawai ne nemi afuwarsa ne a kan rashin samun gudanar da aikina da na yi, a kwanaki da suka gabata, saboda shi ne ƙa'idar gidan sarauta.
Ki yi haƙuri iya matsayina da aikina nake tsayawa."

Asal ta numfasa tana huci, duk da hankalinta ya É—an kwanta.

"Shikenan na ji, daga yanzu za ki bar É—akin da ki ke, za ki koma É—akin hadimai da ke tsakanin sashen Imam da nawa.
Sannan akwai gurin girki a gurin girki a gurin, yadda za a din ga sauƙaƙa miki, sai dai babu ke babu fitowa a duk lokacin da yake nan, muddin ba abinci ki ka kawo masa ba, kuma ba gyaran sashen za ki yi ba. An dawo da ke sashen nan ne, domin ƙara tabattar da tsaron abincin da Imam zai ci"

Nana ta jinjina kai ta ce "In sha Allah, na gode sosai da sosai"

"Ki hanzarta, ki kwaso kayanki ki mayar can, a yau ba sai gobe ba, ku yi magana da Balaraba ta kai ki"

Nana ta risuna ta yi wa Asal godiya, haka aka yi, a ranar ta kwashe kayanta ta mayar can ɓangaren, barorin gidan na ta ƙara mamakin, yadda a ke ɗaga likkafar Nana baƙuwar haure sama da su.
Nana kuwa murna ta din ga yi, ganin tana ƙara samun kusanci da Imam, ta san addu'a da take yi ce Allah yake taimakonta, kuma tana fatan Allah zai yanke mata wannan wahalar nan kusa.
Fita ta yi da nufin ta kwaso kayan wancan É—akin girkin ta dawo da su nan, ta ga mutane na kaiwa da komowa a sashen.
Wani ta gani a cikin mutanen fuskarsa rufe da rawani, amma ta ga kamar ta san shi ta taɓa ganinsa, kamar ta bi bayan mutumin, sai ta ji ana faɗin Imam ne ya faɗo daga kan Taguwarsa.!

AREWABOOKS

Nana ta rasa wa za ta nufa ta samu cikakken bayanin abin da ya faru. Ta san za a rina, tun da ta ga abin nan kuma ta din ga ji a jikinta, ta san wani abun sai ya faru.

A can É—aki kuma, sannu Asal ta din ga jera masa, ya jinjina mata kai kawai.
Ya lumshe idanunsa yana tuna yadda Nana ta roƙe shi kar ya hau Taguwar.

"Wace ce ke?" Ya furta a hankali.

Asal ta ce "Magana ka ke yi ne?" Ya girgiza mata kai alamar a'a.
Tun da ya hau kan Taguwar nan yake jiri, duk yadda ya ƙwarara jikinsa, da ƙoƙarin sarrafata ya kasa, dan daina gani ya yi gaba ɗaya sai jin sa ya yi ya zamo ƙasa.
Ya yi ajiyar zuciya yana sauke numfashi.

"Imam na saka ta dawo ɗakin Hadaimai kamar yadda ka buƙata, ko za ka ci wani abun a kawo maka?"

Ya girgiza mata kai alamar a'a.

"Ina ne yake yi maka ciwo to?"
Ya yinƙura ya tashi ya ce "Babu ko ina salla zan yi"

Yana tangaÉ—i haka ya shiga ya yi salla, ya sake kwanciya.
Nana na ta kai komo falon babu kowa, tana son ta san halin da yake ciki amma babu wanda za ta tambaya.

Wata tawaga ta ga sun shigo sashen, kallo É—aya ta yi masa ta gane Sultan, tana son fita tana jin tsoron kar ta yi laifi, haka ta tsaya tana hangen abin da yake faruwa.
Asal ta fito cikin hijjabi suka gaisa, ta yi wa Sultan jagora zuwa cikin É—akin.

Da hanzari ya nufe shi yana faÉ—in "Hammad, tashi maza a tafi Asibiti"

Ya buÉ—e idonsa ya kalle shi ya ce "Babu abin da yake damuna Sultan, ba sai na je Asibiti ba"

Cikin damuwa ya ce "Me yasa ka yi hawan bayan ka san ba cikakkiyar Lafiya ce da kai ba? Kuma da ka ji ba za ka iya ba ai sai ka haƙura"

"Lokacin da na yi ba na jin komai a jikina, amma tuba nake ba zan sake ba"

Sultan ya ce "Ka tabattar ba ka jin komai a jikinka ba sai mun je Asibiti ba?"

"Ba na jin komai Abie, ka kwantar da hankalinka"

Ya jinjina kai ya ce "To shikenan, Allah ya tsare gaba ka kwanta ka huta sosai"

Ya jinjina masa kai, suka yi sallama ya tafi.

Duk yadda Nana ta so sanin halin da yake ciki, haka ta haƙura, sai dai bacci mai daɗi ya gagara ɗaukan ta.
Da sassafe ta fita ta hau gyaran sashen, tana jira ko za ta ji motsin Asal, duk yadda za a yi ta tambaye ta, ya jikinsa sai dai ta ji shiru, haka ta ajiye Abincin kari ta koma É—akin da aka ba ta.
Sai wajen sha daya da rabi, ta ji motsi a falon, ta fito ta leƙa.
Shiru ta yi tana kallon mutumin da ya zo, kamar shi ta taɓa gani a gidan cin abincin su Al Hussain. Yana tare da Imam Asad.
Sayyid yana zaune a ƙasan Carfet, shi kuma yana saman kujera.
Chapter 76 · 0% Book details