Sashe 75
Buzu Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Zuba mata ido suka yi, gaba É—aya suka yi shiru daga hirar da suke yi.
Ta ce "Shugabana, ga abincin ko zan jira ku duba idan da abin da bai yi ba?"
Ya girgiza kai ya ce "Za ki iya tafiya"
Sai dai ta kasa tashi, ta ci gaba da rarraba ido.
Ya sake cewa "Za ki iya tafiya"
"Dan Allah ka taimaka mini da ayabar hannunka, yunwa nake ji"
Imam Omar ya ce "Imam Hammad, wai wace ce wannan É—in? Ta san waye kai kuwa abin hannunka za ka ba ta?"
Ya kalli ayabar ya kalle ta, bai kai ga yin magana ba, ta saka hannayenta biyu ta miƙa masa.
Tamkar soko haka ya miƙa mata ayabar, ba tare da musun komai ba.
Ya ce "Ga wata nan ki É—auki yadda za ta ishe ki"
Ta girgiza kai ta ce "Wannan kawai ta ishe ni, na gode sosai da sosai"
Duk su ka bi Nana da ido, wasu cike da takaici, wasu kuma mamakin tsaurin idonta, duk da ba abin mamaki ba ne sosai, tun da ba ta san irin girmansu da matsayinsu ba, kasancewarta bare ba ƙabilarsu ba, kuma ba 'yar ƙasarsu ba.
A hankali ta saci kallon hannayensu, sai ta gan su sanye da zobunan nan irin na hannun Sayyid da ya É—auka ya bata.
A take ta koma gefe ta cinye ayabar, sannan ta yinƙura ta tashi.
Imam Asad ya fara masifar wace mahaukaciyar haka, da za ta zo ta yi musu wannan rashin hankalin, su zuba ido su na kallonta.
Hammad ya ce "Ina mai baku haƙuri, baƙuwa ce a cikin lamarin gidan mulki, ku yi mata afuwa"
Nana tuni ta fice daga É—akin, aikuwa fitarta ke da wuya, jiri ya fara É—ibanta, bango ta dafa tana bi a hankali, sai dai kan ta kai inda take so ta yanke jiki ta faÉ—i.
Faɗan Ƙaisar ne ya sanya ta buɗe ido, a matuƙar galabaice.
"Waye ya ce da ki ka karɓa ki ci? Kin san abin da aka yi a jikin ayabar? Ban da na riga na buɗe miki ido ki na ganin abubuwa, da ba zan sake bari ki ga komai a kansa. Sai kin kashe kan ki a banza a kan mutumin nan, gaba ɗaya kin ƙarar da ƙarfinsa a kan ki, wanda ko tabbacin idan ya tuna ki zai miki irin wannan son ba ki da shi"
Nana dai kasa magana ta yi, saboda yadda jikinta yake a mace, duniyar take juya mata.
Ɗaga bakinta ya yi ya zuba mata wani abu mai kama da turiri, ta yi wani yinƙuri ta hau amai ta hanci da bakinta.
Ba ƙaramin galabaita ta yi ba, jin yadda ƙayoyin da suka tsiro a jikin ayabar su na sukar ƙirjinta gurin yinƙurin aman da ta yi.
Cikin fusata mutumin yake magana, "Wane irin wawanci ne haka da shirme da rashin hankali, ta yaya zamu shirya abu ka je ka bari ya ɓaci?"
Cikin damuwa matashin ya ce "Wallahi Tafawa ba laifina ba ne ba, dan har ya fara ci wata yarinya ce ta hana shi ci, wai ya ba ta yunwa take ji"
"Wace yarinyar ce a kaf faɗin Agadez za ta je tsakiyar ku, har Imam zai ci abu ta ce ya bata? Ɗaya daga cikin mugwayen ɗabi'unsa kenan da ya sanya yake zubar da kimar ku a idon mutane maƙasƙanta, har su samu zarafin raina ku. Ban da raini da wulaƙanci har baiwa ta ga abu a hannun Imam na ƙasar Agadez ta ce za ta ci."
Ya buÉ—e baki zai yi magana ya ce "Ka ga tashi ka bani guri ni kafin na mangare ka" Haka ya ja bakinsa ya tashi ya fice jikinsa a sanyaye.
*****
Alhaji Zailani ne a zaune a falon Hajiya Sa'a, ya je yi mata ta'aziyyar mutuwar Abba.
Ya numfasa ya ce "Wai dama Abban ba shi da lafiya ne?"
Ta girgiza kai ta wassafa masa dukkanin abin da ya faru.
Cikin kaɗuwa yake jin bayanin nata. Ya ce "Ban da ke Hajiya Sa'a, ina ke ina gayyato yarinya da rana tsaka ki janyo ta jikinki, ga shi ta zame miki masifa, haba Sa'a. Ke kin san ba kowa a ke fallasawa sirrin ƙungiya ba, Allah ya kyauta, ya yi mata gaisuwa ya tafi.
*****
Hammad tun bayan tafiyar sauran 'yan uwansa yake tunani daban-daban a ransa.
Tuni aka saita masa wayarsa, ya ci gaba da amfaninsa da ita.
Wayewar gari yana ta jiran Abinci amma shiru, ya gaji da jira saboda yana jin yunwa, ya tafi ya tashi Asal da take ta bacci.
"Imam lafiya kuwa?"
"Ba a kawo mini Abinci ba, ina jin yunwa zan fita"
Kamar ta yi tsaki, saboda ta ji daÉ—in baccin, haushi ya kama ta, tare da tunanin uban abin da ya hana Nana tashi ta yi masa girki ko ta makara haka.
Ga shi duk hadiman sashen ta kore su, dan haka ta tashi da kanta, ta fita.
A zaune ta tarar da Nana ta jingina da bango, idanunta duk sun faÉ—a kamar ta kwana tana amai da gudawa.
"Wani wulaƙancin ne ya sanya ba ki tashi kin yi wa Imam girki ba, har ki ka saka na biyo ki nan?"
Nana ta numfasa ta ce "Ba ni da lafiya ne"
"Ba ki da lafiya kuma Imam ba zai ci abinci ba? Kin san ba kowane Abinci yake ci ba"
Wani malulun takaici ya ƙule Nana, wato lafiyarta ba abin da yake gabanta ba ne, kawai fatanta ta yi wa mijinta girki tun da ga baiwa.
"Magana nake yi miki kin yi mini shiru"
"To me zan ce miki, ba ni da lafiya, ai ban taɓa ƙin yin girki ba. Ko wani abu da ki ka saka ni ba, amma yau ba ni da lafiya babu abin da zan iya yi. Idan ke ba za ki yi mini uzuri ba, ki gaya masa kukunsa babu lafiya na san, shi zai iya yi mini uzuri"
A hasale Asal ta buɗe baki za ta yi magana, Nana ta yi mata wani irin kallo, da a dole ta haɗiye maganganun da ta yi niyyar caɓa wa Nana.
Ta haƙura ta juya ta fita, tana tunanin me ta ji ne ko ta gani, ta kasa yi wa Nana rashin mutunci.
Tana komawa ya kalle ta ya ce "Ina Abincin?"
"Wai ba ta da lafiya"
"Me ya same ta?" Ta girgiza kai jiki a mace ta ce "Nima ban sani ba"
Ya so sake wata tambayar, amma sanin halin Asal ya sanya shi ta shi, zai fita.
Ta ce "To ina za ka je ba ka karya ba?"
"Zan samu abin da zan ci, zan je na ga Mahmoud ne" Daga haka bai kuma cewa komai ba ya fita.
Bakin Imam Hammad fal maganganu kamar yadda bakin Mahmudu yake fal maganganu, amma kowanne ya kasa furta wa kowa.
Hammad ne ya numfasa ya ce "Mahmud ina son na koma kan ayyukana, amma Sultan ya ce mini na dakata, akwai abubuwan da nake son yi da yawa."
Mahmoudu ya ce "To ka yi haƙuri, wataƙila akwai dalilin da ya sanya ya ce ka dakata tukuna"
Ya numfasa ya ce "Haka ne, wai yaushe za ka shigo gida ne?"
Ya girgiza kai ya ce "Ba na son shiga gidan nan naku"
"Saboda me?"
"Kai ma ka sani ai"
Imam ya ce "Ban san komai ba. Jiya Imams sun kawo mini ziyara. Ranar Lahadi za mu yi zagayen raƙuma da shan shayi, ka zo mu je tare"
"Imam, ka na manta waye ni, da ƙoƙarin kai ni matsayin da Allah bai kai ni ba, ni dai dan Allah ka yi haƙuri"
"Mahmoudu, idan ba kai ba wa ka ke so na janyo jikina? Ka san komai fa? Shikenan haka ni zan zauna?" Yayi maganar muryarsa É—auke da rauni.
"Haba jarumin shugabana, ka na fa da wanda ku ka shaƙu, ku ke da kusanci tsakaninku sosai da sosai"
"Waye?" Ya yi maganar yana kallonsa.
"Zan haɗa ku kwanan nan, aure zan ƙara yi maka kwanan nan, ka na son 'yar Nigeria?"
Ƙanƙance idanunsa ya yi yana kallon Mahmoudu. Ya ce "Ga ka nan ga Asal ai"
"Ahh yi haƙuri, kar ka gaya mata sai ta saka a fille mini kai"
Hammad ya yi murmushi yana gyara zamansa.
Sai da Nana ta shafe kwana uku ba ta aikin komai, haka kurum Imam ya ji abin ya tsaye masa ya dame shi, ko ya yi ƙoƙarin mantawa sai ya kasa. Kwanakin nan uku kame-kame kawai yake yi gurin cin abinci, duk abin da zai ci sai ya ga kamar abin zai cutar da shi. Ga uwa uba rashin ɗanɗanon abinci da ba ya ji gaba ɗaya.
Yau da Nana ta lallaɓa ta fito, ta ji ana ta zancen hawan zagayen da za a yi a kan raƙuma.
Har ya yi shirinsa zai fita, ya tarar da Abinci a falo.
Cikin zaƙuwa ya ƙarasa ya buɗe, tabbas ƙamshin girkinta ne. Wani murmushi ya suɓuce masa cike da farin ciki.
Sai dai sam ba su haÉ—u ba.
Ta ce "Shugabana, ga abincin ko zan jira ku duba idan da abin da bai yi ba?"
Ya girgiza kai ya ce "Za ki iya tafiya"
Sai dai ta kasa tashi, ta ci gaba da rarraba ido.
Ya sake cewa "Za ki iya tafiya"
"Dan Allah ka taimaka mini da ayabar hannunka, yunwa nake ji"
Imam Omar ya ce "Imam Hammad, wai wace ce wannan É—in? Ta san waye kai kuwa abin hannunka za ka ba ta?"
Ya kalli ayabar ya kalle ta, bai kai ga yin magana ba, ta saka hannayenta biyu ta miƙa masa.
Tamkar soko haka ya miƙa mata ayabar, ba tare da musun komai ba.
Ya ce "Ga wata nan ki É—auki yadda za ta ishe ki"
Ta girgiza kai ta ce "Wannan kawai ta ishe ni, na gode sosai da sosai"
Duk su ka bi Nana da ido, wasu cike da takaici, wasu kuma mamakin tsaurin idonta, duk da ba abin mamaki ba ne sosai, tun da ba ta san irin girmansu da matsayinsu ba, kasancewarta bare ba ƙabilarsu ba, kuma ba 'yar ƙasarsu ba.
A hankali ta saci kallon hannayensu, sai ta gan su sanye da zobunan nan irin na hannun Sayyid da ya É—auka ya bata.
A take ta koma gefe ta cinye ayabar, sannan ta yinƙura ta tashi.
Imam Asad ya fara masifar wace mahaukaciyar haka, da za ta zo ta yi musu wannan rashin hankalin, su zuba ido su na kallonta.
Hammad ya ce "Ina mai baku haƙuri, baƙuwa ce a cikin lamarin gidan mulki, ku yi mata afuwa"
Nana tuni ta fice daga É—akin, aikuwa fitarta ke da wuya, jiri ya fara É—ibanta, bango ta dafa tana bi a hankali, sai dai kan ta kai inda take so ta yanke jiki ta faÉ—i.
Faɗan Ƙaisar ne ya sanya ta buɗe ido, a matuƙar galabaice.
"Waye ya ce da ki ka karɓa ki ci? Kin san abin da aka yi a jikin ayabar? Ban da na riga na buɗe miki ido ki na ganin abubuwa, da ba zan sake bari ki ga komai a kansa. Sai kin kashe kan ki a banza a kan mutumin nan, gaba ɗaya kin ƙarar da ƙarfinsa a kan ki, wanda ko tabbacin idan ya tuna ki zai miki irin wannan son ba ki da shi"
Nana dai kasa magana ta yi, saboda yadda jikinta yake a mace, duniyar take juya mata.
Ɗaga bakinta ya yi ya zuba mata wani abu mai kama da turiri, ta yi wani yinƙuri ta hau amai ta hanci da bakinta.
Ba ƙaramin galabaita ta yi ba, jin yadda ƙayoyin da suka tsiro a jikin ayabar su na sukar ƙirjinta gurin yinƙurin aman da ta yi.
Cikin fusata mutumin yake magana, "Wane irin wawanci ne haka da shirme da rashin hankali, ta yaya zamu shirya abu ka je ka bari ya ɓaci?"
Cikin damuwa matashin ya ce "Wallahi Tafawa ba laifina ba ne ba, dan har ya fara ci wata yarinya ce ta hana shi ci, wai ya ba ta yunwa take ji"
"Wace yarinyar ce a kaf faɗin Agadez za ta je tsakiyar ku, har Imam zai ci abu ta ce ya bata? Ɗaya daga cikin mugwayen ɗabi'unsa kenan da ya sanya yake zubar da kimar ku a idon mutane maƙasƙanta, har su samu zarafin raina ku. Ban da raini da wulaƙanci har baiwa ta ga abu a hannun Imam na ƙasar Agadez ta ce za ta ci."
Ya buÉ—e baki zai yi magana ya ce "Ka ga tashi ka bani guri ni kafin na mangare ka" Haka ya ja bakinsa ya tashi ya fice jikinsa a sanyaye.
*****
Alhaji Zailani ne a zaune a falon Hajiya Sa'a, ya je yi mata ta'aziyyar mutuwar Abba.
Ya numfasa ya ce "Wai dama Abban ba shi da lafiya ne?"
Ta girgiza kai ta wassafa masa dukkanin abin da ya faru.
Cikin kaɗuwa yake jin bayanin nata. Ya ce "Ban da ke Hajiya Sa'a, ina ke ina gayyato yarinya da rana tsaka ki janyo ta jikinki, ga shi ta zame miki masifa, haba Sa'a. Ke kin san ba kowa a ke fallasawa sirrin ƙungiya ba, Allah ya kyauta, ya yi mata gaisuwa ya tafi.
*****
Hammad tun bayan tafiyar sauran 'yan uwansa yake tunani daban-daban a ransa.
Tuni aka saita masa wayarsa, ya ci gaba da amfaninsa da ita.
Wayewar gari yana ta jiran Abinci amma shiru, ya gaji da jira saboda yana jin yunwa, ya tafi ya tashi Asal da take ta bacci.
"Imam lafiya kuwa?"
"Ba a kawo mini Abinci ba, ina jin yunwa zan fita"
Kamar ta yi tsaki, saboda ta ji daÉ—in baccin, haushi ya kama ta, tare da tunanin uban abin da ya hana Nana tashi ta yi masa girki ko ta makara haka.
Ga shi duk hadiman sashen ta kore su, dan haka ta tashi da kanta, ta fita.
A zaune ta tarar da Nana ta jingina da bango, idanunta duk sun faÉ—a kamar ta kwana tana amai da gudawa.
"Wani wulaƙancin ne ya sanya ba ki tashi kin yi wa Imam girki ba, har ki ka saka na biyo ki nan?"
Nana ta numfasa ta ce "Ba ni da lafiya ne"
"Ba ki da lafiya kuma Imam ba zai ci abinci ba? Kin san ba kowane Abinci yake ci ba"
Wani malulun takaici ya ƙule Nana, wato lafiyarta ba abin da yake gabanta ba ne, kawai fatanta ta yi wa mijinta girki tun da ga baiwa.
"Magana nake yi miki kin yi mini shiru"
"To me zan ce miki, ba ni da lafiya, ai ban taɓa ƙin yin girki ba. Ko wani abu da ki ka saka ni ba, amma yau ba ni da lafiya babu abin da zan iya yi. Idan ke ba za ki yi mini uzuri ba, ki gaya masa kukunsa babu lafiya na san, shi zai iya yi mini uzuri"
A hasale Asal ta buɗe baki za ta yi magana, Nana ta yi mata wani irin kallo, da a dole ta haɗiye maganganun da ta yi niyyar caɓa wa Nana.
Ta haƙura ta juya ta fita, tana tunanin me ta ji ne ko ta gani, ta kasa yi wa Nana rashin mutunci.
Tana komawa ya kalle ta ya ce "Ina Abincin?"
"Wai ba ta da lafiya"
"Me ya same ta?" Ta girgiza kai jiki a mace ta ce "Nima ban sani ba"
Ya so sake wata tambayar, amma sanin halin Asal ya sanya shi ta shi, zai fita.
Ta ce "To ina za ka je ba ka karya ba?"
"Zan samu abin da zan ci, zan je na ga Mahmoud ne" Daga haka bai kuma cewa komai ba ya fita.
Bakin Imam Hammad fal maganganu kamar yadda bakin Mahmudu yake fal maganganu, amma kowanne ya kasa furta wa kowa.
Hammad ne ya numfasa ya ce "Mahmud ina son na koma kan ayyukana, amma Sultan ya ce mini na dakata, akwai abubuwan da nake son yi da yawa."
Mahmoudu ya ce "To ka yi haƙuri, wataƙila akwai dalilin da ya sanya ya ce ka dakata tukuna"
Ya numfasa ya ce "Haka ne, wai yaushe za ka shigo gida ne?"
Ya girgiza kai ya ce "Ba na son shiga gidan nan naku"
"Saboda me?"
"Kai ma ka sani ai"
Imam ya ce "Ban san komai ba. Jiya Imams sun kawo mini ziyara. Ranar Lahadi za mu yi zagayen raƙuma da shan shayi, ka zo mu je tare"
"Imam, ka na manta waye ni, da ƙoƙarin kai ni matsayin da Allah bai kai ni ba, ni dai dan Allah ka yi haƙuri"
"Mahmoudu, idan ba kai ba wa ka ke so na janyo jikina? Ka san komai fa? Shikenan haka ni zan zauna?" Yayi maganar muryarsa É—auke da rauni.
"Haba jarumin shugabana, ka na fa da wanda ku ka shaƙu, ku ke da kusanci tsakaninku sosai da sosai"
"Waye?" Ya yi maganar yana kallonsa.
"Zan haɗa ku kwanan nan, aure zan ƙara yi maka kwanan nan, ka na son 'yar Nigeria?"
Ƙanƙance idanunsa ya yi yana kallon Mahmoudu. Ya ce "Ga ka nan ga Asal ai"
"Ahh yi haƙuri, kar ka gaya mata sai ta saka a fille mini kai"
Hammad ya yi murmushi yana gyara zamansa.
Sai da Nana ta shafe kwana uku ba ta aikin komai, haka kurum Imam ya ji abin ya tsaye masa ya dame shi, ko ya yi ƙoƙarin mantawa sai ya kasa. Kwanakin nan uku kame-kame kawai yake yi gurin cin abinci, duk abin da zai ci sai ya ga kamar abin zai cutar da shi. Ga uwa uba rashin ɗanɗanon abinci da ba ya ji gaba ɗaya.
Yau da Nana ta lallaɓa ta fito, ta ji ana ta zancen hawan zagayen da za a yi a kan raƙuma.
Har ya yi shirinsa zai fita, ya tarar da Abinci a falo.
Cikin zaƙuwa ya ƙarasa ya buɗe, tabbas ƙamshin girkinta ne. Wani murmushi ya suɓuce masa cike da farin ciki.
Sai dai sam ba su haÉ—u ba.