Sashe 52
Buzu Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Hasna ta ce "Saurin me ki ke yi ne?"
"Na gaji ne sosai, bacci nake ji ina son na samu na tashi da wuri"
Ta jinjina kai ta ce "Ya yi je ki" Nana ta fice ta tafi É—akinsu.
Sai dai duk gajiyar da ta yi, bacci ya gagari idanunta.
Tun bayan sallar Asuba, ta tafi kitchen É—in ta fara aikin da Hasna ta saka ta. Sai bayan Azahar ta kammala komai, Hasna ta aiko aka ta É—auki Abincin.
Nana ta fara shirin tafiya ta je ta yi wanka ta huta.
Adama ta ce "Ina za ki je kuma ga ayyukan kitchen fal?"
Nana ta numfasa ta ce "Ki yi haƙuri, Hasna ce ta saka ni aiki, ta ce idan na gama, na je na huta"
"A'a ba zai yiwu ba, ni ce mini a aka yi kawai za ki yi mata aiki, dan hakan idan kin gama ki saka hannu ku ci gaba da aikinmu, wa za ki bar wa wannan aikin?"
"To ki yi haƙuri, na gaji gaskiya ba na jin daɗi" kawai ta fice, tattaunawa suka shiga yi a tsakanin su, yadda za su kawo ƙarshen Nana a gurin baki ɗaya.
A ƙarshe suka yanke shawarar, su ƙara ƙaimi su ɓata ta a gurin Hasna, ganin yadda ita ma ta sako Nana a gaba da tsangwama.
Bayan sallar isha'i, Nana ta daÉ—e a zaune tana tasbihi, tunanin gidansu da 'yan uwanta ya addabi zuciyarta, ga shi abin da ta fito neman har yau babu labari. Ta daÉ—e tana addu'a kafin ta nemi guri ta kwanta.
Washegari ma su na ta aiki tun safe har Yamma, sai ga Hasna ta shigo.
Duk yadda Hasna take da kyau, ita da Al Hussain, wannan da suka shigo ta fita kyau, tamkar balarabiya, jawur da doguwa sai dai siririya ce sosai. Fuskarta ta sha make up, sai zuba ƙamshi take yi.
Ta yafa É—an siririn mayafin abayarta a kanta. Sai kallonsu take É—aya bayan É—aya tana yatsuna fuska su na yare ita da Hasna.
Duk suka gaishe su, Nana kuma ta yi burus.
Hasna ta nuna mata Nana ta ce "Kin ganta nan"
Asal ta yamutsa fuska ta ce "Ya na ganta baƙa ƙirin haka, ina fatan ba na ƙazanta ba ne?" Nana ta yi mamakin jin Hausa raɗau a bakinta.
"Ke ina ruwanki da baƙinta, ba dai Abinci ya yi ba?"
"Eh kin san ba na son ƙazanta ne"
Hasna ta ce "Sauran ma'aikatan namu ma ai akwai baƙaƙe, kuma kema kin san da ba ta da tsafta, ba zan saka ta yi miki girki ba.Ke Nana ba ki ganni da baƙuwa ba ne?" Nana ta ɗaga kai ta kalle su, ta yi shiru tana wasa da wuƙar hannunta, saboda ciwon da maganganun da suke yi ya yi mata, na cin zarafin baƙar fatarta da danganta ta da ƙazanta, duk ba wai duhu ne da ita sosai ba.
Shiru Hasna ta yi ta kamo wata hirar, ganin alamun idan ta matsa Nana za ta yarfa ta ne a gaban baƙuwarta. Ba a taɓa ma'aikacin da ba ya shakkar ta ba sai Nana. Duk abin da ta saka ta na aiki za ta yi, amma ba ta son rainin hankali.
Bayan sun fito Asal ta tsaya ta kalli Hasna ta ce "Hasna"
"Na'am"
"Ina ga yarinyar nan ta yi dai-dai da abin da nake nema"
"Wace yarinyar?"
Asal ta ce "Wannan 'yar Nigeriar, ina buƙatar za ki ba ni ita"
Ayshercool
08081012143
70
Sai da Nene ta tabattar Nana ta É—an nutsu, sannan suka kwanta.
Washegari Nene ta fita, ta bar Nana a gidan tare da Muhsin. Bayan ta dawo daga gurin sama'arta ta cewa Nana, yakamata ta je ta ɗan sai abubuwan da za ta buƙata saboda tafiyar da za ta yi da nisa, kuma ba su san yaya tsarin aikin can ɗin yake ba.
Nana ta ce "Ni babu abin da nake buƙata, ki bani wani abin na riƙe a hannuna, sauran kuɗin kuma ki riƙe saboda kula da Muhsin na s...
"Biyana za ki yi kenan dan na riƙe miki Muhsin?" Nene ta katse ta.
"Allah ya baki haƙuri, ba haka nake nufi na, na ga dole ɗan abubuwan buƙatunsa duk ke ki ke yi masa Nene, tun da ga kuɗi sun"
"Kuɗinki ba su isa su saka na riƙe miki ɗa ba ko?"
Nana ta ce "Na sani, ai shi ya sanya na ce ki yi haƙuri.
Nene ta ce "Ba zan yi haƙurin ba sai na gama, kin iya kunna ni da na fara faɗa ki hau bani haƙuri, wato in ci kaina to sai na idar"
Nana ta yi mata shiru ta yi faÉ—anta ta gama.
Washegari Nene ta saka Nana a gaba suka je kasuwa, ta sata ta yi sayayyar kayan sakawa da na É—an shafe-shafe, ta yi wa Muhsin sayayyar kayan sakawa da pampers. Babu yadda ba ta yi da Nene ba ta É—auki wani abin ta ce ba za ta É—auka na.
Nana ta haɗe rai ta ce "Eh dama ba ki ɗauke ni 'yarki ba, shi ya sanya duk abin da zan yi miki ba kya karɓa"
"Ni za ki yi wa wayo, na ji ban ɗauke ki 'yar ba, ni ga ɗana nan" tayi maganar tana shafo Muhsin da ke bayanta. Da ƙyar sai da suka kai ruwan rana Sannan Nene ta karɓi abin da Nana ta saya mata.
Sai dai kan su bar kasuwar har sun shirya. Nana ta ce "Nene kin ce mini ki na da ɗa, amma ban taɓa ganinsa ya zo ba, ba ya zuwa ya gan ki ne?"
Nene ta ce "Kamar ban damu da shi ba ko?"
"A'a kawai dai tambaya na yi "
"Yana can Nigeria"
"To me yake yi a Nigeria ba ya zuwa inda ki ke?"
"Sana'a yake yi, ai ya zo ki na can gurin aiki"
Duk da Nana ba ta gamsu da amsoshin da Nene ta ba ta ba, amma ta basar ta ce "Allah sarki, Allah bai yi zamu haÉ—u ba".
Haka suka ci gaba da hira suka koma gida, Nana ji take yi tamkar ta É—auke É—anta ta tafi da shi.
Gidansu Ashura Nana ta je, ta samu keke ta É—iÉ—É—inka kayan da ta sayo, ta sake haÉ—a jakarta ta É—auki muhimman abubuwa a kayanta.
Duk da a ɗaki Nene take rufe mata su, ba ta taɓa ganin alamar Nenen tana yi bincike a cikin kayan ba.
*****
Ko da Jamila suka dawo Kano, fakar ido ta yi ta jefar da wannan tarkacen da aka ba ta aka ce da su za ta kai jini.
Gaba ɗaya da ta tuna abin tsigar jikinta take tashi, ta ji ciwon kanta da zazzaɓi ya ƙaru.
Gefe guda kuma hankalinta yana kan yadda ta ji Hajiya Sa'a tana faÉ—in za ta sake bayar da É—an Alhaji Fatuhu. Ta jinjina rashin imaninta mutumin da yake fama da karayar arziki ga ciwo, ya rasa wancan É—an kuma a sake bayar da wannan kamar ba a yi masa adalci ba. Sai dai gaba É—aya ba ta san ta ina za ta fara ba, tana jin a ranta kamar yakamata ta tseratar da yaron.
A gida ta tarar da Gaddafi, ta sha jinin jikinta da irin mugun kallon da ya yi mata, amma bai ce mata uffan ba. Suwaiba ma ƙura mata ido ta yi tana bin ta da kallo.
Ta tsuke fuska ta harsri Suwaiba, sai dai Suwaiba ta tuntsure da dariya, kamar za ta shiÉ—e. Jamila ta yi tsaki ta shige É—akinsu.
Ba ta tarar da Mama a gida ba, haka ma Baba.
*****
Shiru Alhaji Zailani ya yi yana kallon Doctor Sharif yana sauraren shi, har ya gama karanta masa abin da Shukura ta je ta same shi ta yi masa.
Ya ja numfashi ya ce "Shikenan, aikinka ya yi kyau Sharif, na kuma gode sosai da sosai da ka ke sanar da ni wannan abubuwan, Allah ya saka maka da mafificin alkhairi. Ka je za ka ga saƙo" Sharif ya yinƙura ya tashi ya tafi.
Alhaji Zailani ya numfasa a fili ya ce "Duk da kasancewar ki 'ya mafi soyuwa a cikin zuciyata, an zo gaɓar da ki ka ƙetare layin da bai kamata ki ƙetare ba, kina ƙoƙarin tono abin da zai wargaza zaman lafiya da kwanciyar hankali, dan haka ki yi haƙuri da duk matakin da zan ɗauka a kan ki.
*****
Nana ta jingina da jikin gilashin motar, tana kallon tulin yashin saharar da ya mamaye gurin. Fili fetal hagu da dama duk yashi ne. Cikin yanayi mai kama da bacci take ganin abubuwan da ta din ga gani a bacci cikin saharar.
Ko a yanzun ma su na tafe Sayyid kawai take gani a kan raƙumi yana biye da su a cikin saharar.
Kamar an taɓa ta ta ɗan yi firgigit ta kalli gurin, haryanzu a titin da ya ratsa saharar suke tafiya, zuciyarta ta yi wani irin bugu da sai da ta dafe ƙirjinta.
Sanyi ta fara yana ratsa ta har cikin ƙashinta, ta ɗaga ido tana ɗan waige-waige ta ga ta ina za ta gano Ƙaisar ko wata baƙuwar halittar da ba jinsin mutane ba, sai dai ba ta ga komai ba.
Ta sake jingina da jikin motar tana ta karanto duk addu'ar da ta zo bakinta. A haka har suka shigo cikin gari sosai da sosai.
Nana na son karanta Symbols ɗin da take gani, amma ba komai take iya fahimta ba saboda rubutun French. Babbar hanya mai ɗauke da ƙaton gate ta ciki suka wuce.
Ba ƙaramar gajiya Nana ta yi ba, saboda azabar nisan tafiyar da suka shawo ba, ba su ƙarasa ba sai bayan magariba. Kewar ɗan ta ta addabi zuciyarta, tunaninta yadda za ta din ga sintirin tsakanin Agadez da Maraɗi a wannan uwar tafiyar kamar ta ya da shege.
"Na gaji ne sosai, bacci nake ji ina son na samu na tashi da wuri"
Ta jinjina kai ta ce "Ya yi je ki" Nana ta fice ta tafi É—akinsu.
Sai dai duk gajiyar da ta yi, bacci ya gagari idanunta.
Tun bayan sallar Asuba, ta tafi kitchen É—in ta fara aikin da Hasna ta saka ta. Sai bayan Azahar ta kammala komai, Hasna ta aiko aka ta É—auki Abincin.
Nana ta fara shirin tafiya ta je ta yi wanka ta huta.
Adama ta ce "Ina za ki je kuma ga ayyukan kitchen fal?"
Nana ta numfasa ta ce "Ki yi haƙuri, Hasna ce ta saka ni aiki, ta ce idan na gama, na je na huta"
"A'a ba zai yiwu ba, ni ce mini a aka yi kawai za ki yi mata aiki, dan hakan idan kin gama ki saka hannu ku ci gaba da aikinmu, wa za ki bar wa wannan aikin?"
"To ki yi haƙuri, na gaji gaskiya ba na jin daɗi" kawai ta fice, tattaunawa suka shiga yi a tsakanin su, yadda za su kawo ƙarshen Nana a gurin baki ɗaya.
A ƙarshe suka yanke shawarar, su ƙara ƙaimi su ɓata ta a gurin Hasna, ganin yadda ita ma ta sako Nana a gaba da tsangwama.
Bayan sallar isha'i, Nana ta daÉ—e a zaune tana tasbihi, tunanin gidansu da 'yan uwanta ya addabi zuciyarta, ga shi abin da ta fito neman har yau babu labari. Ta daÉ—e tana addu'a kafin ta nemi guri ta kwanta.
Washegari ma su na ta aiki tun safe har Yamma, sai ga Hasna ta shigo.
Duk yadda Hasna take da kyau, ita da Al Hussain, wannan da suka shigo ta fita kyau, tamkar balarabiya, jawur da doguwa sai dai siririya ce sosai. Fuskarta ta sha make up, sai zuba ƙamshi take yi.
Ta yafa É—an siririn mayafin abayarta a kanta. Sai kallonsu take É—aya bayan É—aya tana yatsuna fuska su na yare ita da Hasna.
Duk suka gaishe su, Nana kuma ta yi burus.
Hasna ta nuna mata Nana ta ce "Kin ganta nan"
Asal ta yamutsa fuska ta ce "Ya na ganta baƙa ƙirin haka, ina fatan ba na ƙazanta ba ne?" Nana ta yi mamakin jin Hausa raɗau a bakinta.
"Ke ina ruwanki da baƙinta, ba dai Abinci ya yi ba?"
"Eh kin san ba na son ƙazanta ne"
Hasna ta ce "Sauran ma'aikatan namu ma ai akwai baƙaƙe, kuma kema kin san da ba ta da tsafta, ba zan saka ta yi miki girki ba.Ke Nana ba ki ganni da baƙuwa ba ne?" Nana ta ɗaga kai ta kalle su, ta yi shiru tana wasa da wuƙar hannunta, saboda ciwon da maganganun da suke yi ya yi mata, na cin zarafin baƙar fatarta da danganta ta da ƙazanta, duk ba wai duhu ne da ita sosai ba.
Shiru Hasna ta yi ta kamo wata hirar, ganin alamun idan ta matsa Nana za ta yarfa ta ne a gaban baƙuwarta. Ba a taɓa ma'aikacin da ba ya shakkar ta ba sai Nana. Duk abin da ta saka ta na aiki za ta yi, amma ba ta son rainin hankali.
Bayan sun fito Asal ta tsaya ta kalli Hasna ta ce "Hasna"
"Na'am"
"Ina ga yarinyar nan ta yi dai-dai da abin da nake nema"
"Wace yarinyar?"
Asal ta ce "Wannan 'yar Nigeriar, ina buƙatar za ki ba ni ita"
Ayshercool
08081012143
70
Sai da Nene ta tabattar Nana ta É—an nutsu, sannan suka kwanta.
Washegari Nene ta fita, ta bar Nana a gidan tare da Muhsin. Bayan ta dawo daga gurin sama'arta ta cewa Nana, yakamata ta je ta ɗan sai abubuwan da za ta buƙata saboda tafiyar da za ta yi da nisa, kuma ba su san yaya tsarin aikin can ɗin yake ba.
Nana ta ce "Ni babu abin da nake buƙata, ki bani wani abin na riƙe a hannuna, sauran kuɗin kuma ki riƙe saboda kula da Muhsin na s...
"Biyana za ki yi kenan dan na riƙe miki Muhsin?" Nene ta katse ta.
"Allah ya baki haƙuri, ba haka nake nufi na, na ga dole ɗan abubuwan buƙatunsa duk ke ki ke yi masa Nene, tun da ga kuɗi sun"
"Kuɗinki ba su isa su saka na riƙe miki ɗa ba ko?"
Nana ta ce "Na sani, ai shi ya sanya na ce ki yi haƙuri.
Nene ta ce "Ba zan yi haƙurin ba sai na gama, kin iya kunna ni da na fara faɗa ki hau bani haƙuri, wato in ci kaina to sai na idar"
Nana ta yi mata shiru ta yi faÉ—anta ta gama.
Washegari Nene ta saka Nana a gaba suka je kasuwa, ta sata ta yi sayayyar kayan sakawa da na É—an shafe-shafe, ta yi wa Muhsin sayayyar kayan sakawa da pampers. Babu yadda ba ta yi da Nene ba ta É—auki wani abin ta ce ba za ta É—auka na.
Nana ta haɗe rai ta ce "Eh dama ba ki ɗauke ni 'yarki ba, shi ya sanya duk abin da zan yi miki ba kya karɓa"
"Ni za ki yi wa wayo, na ji ban ɗauke ki 'yar ba, ni ga ɗana nan" tayi maganar tana shafo Muhsin da ke bayanta. Da ƙyar sai da suka kai ruwan rana Sannan Nene ta karɓi abin da Nana ta saya mata.
Sai dai kan su bar kasuwar har sun shirya. Nana ta ce "Nene kin ce mini ki na da ɗa, amma ban taɓa ganinsa ya zo ba, ba ya zuwa ya gan ki ne?"
Nene ta ce "Kamar ban damu da shi ba ko?"
"A'a kawai dai tambaya na yi "
"Yana can Nigeria"
"To me yake yi a Nigeria ba ya zuwa inda ki ke?"
"Sana'a yake yi, ai ya zo ki na can gurin aiki"
Duk da Nana ba ta gamsu da amsoshin da Nene ta ba ta ba, amma ta basar ta ce "Allah sarki, Allah bai yi zamu haÉ—u ba".
Haka suka ci gaba da hira suka koma gida, Nana ji take yi tamkar ta É—auke É—anta ta tafi da shi.
Gidansu Ashura Nana ta je, ta samu keke ta É—iÉ—É—inka kayan da ta sayo, ta sake haÉ—a jakarta ta É—auki muhimman abubuwa a kayanta.
Duk da a ɗaki Nene take rufe mata su, ba ta taɓa ganin alamar Nenen tana yi bincike a cikin kayan ba.
*****
Ko da Jamila suka dawo Kano, fakar ido ta yi ta jefar da wannan tarkacen da aka ba ta aka ce da su za ta kai jini.
Gaba ɗaya da ta tuna abin tsigar jikinta take tashi, ta ji ciwon kanta da zazzaɓi ya ƙaru.
Gefe guda kuma hankalinta yana kan yadda ta ji Hajiya Sa'a tana faÉ—in za ta sake bayar da É—an Alhaji Fatuhu. Ta jinjina rashin imaninta mutumin da yake fama da karayar arziki ga ciwo, ya rasa wancan É—an kuma a sake bayar da wannan kamar ba a yi masa adalci ba. Sai dai gaba É—aya ba ta san ta ina za ta fara ba, tana jin a ranta kamar yakamata ta tseratar da yaron.
A gida ta tarar da Gaddafi, ta sha jinin jikinta da irin mugun kallon da ya yi mata, amma bai ce mata uffan ba. Suwaiba ma ƙura mata ido ta yi tana bin ta da kallo.
Ta tsuke fuska ta harsri Suwaiba, sai dai Suwaiba ta tuntsure da dariya, kamar za ta shiÉ—e. Jamila ta yi tsaki ta shige É—akinsu.
Ba ta tarar da Mama a gida ba, haka ma Baba.
*****
Shiru Alhaji Zailani ya yi yana kallon Doctor Sharif yana sauraren shi, har ya gama karanta masa abin da Shukura ta je ta same shi ta yi masa.
Ya ja numfashi ya ce "Shikenan, aikinka ya yi kyau Sharif, na kuma gode sosai da sosai da ka ke sanar da ni wannan abubuwan, Allah ya saka maka da mafificin alkhairi. Ka je za ka ga saƙo" Sharif ya yinƙura ya tashi ya tafi.
Alhaji Zailani ya numfasa a fili ya ce "Duk da kasancewar ki 'ya mafi soyuwa a cikin zuciyata, an zo gaɓar da ki ka ƙetare layin da bai kamata ki ƙetare ba, kina ƙoƙarin tono abin da zai wargaza zaman lafiya da kwanciyar hankali, dan haka ki yi haƙuri da duk matakin da zan ɗauka a kan ki.
*****
Nana ta jingina da jikin gilashin motar, tana kallon tulin yashin saharar da ya mamaye gurin. Fili fetal hagu da dama duk yashi ne. Cikin yanayi mai kama da bacci take ganin abubuwan da ta din ga gani a bacci cikin saharar.
Ko a yanzun ma su na tafe Sayyid kawai take gani a kan raƙumi yana biye da su a cikin saharar.
Kamar an taɓa ta ta ɗan yi firgigit ta kalli gurin, haryanzu a titin da ya ratsa saharar suke tafiya, zuciyarta ta yi wani irin bugu da sai da ta dafe ƙirjinta.
Sanyi ta fara yana ratsa ta har cikin ƙashinta, ta ɗaga ido tana ɗan waige-waige ta ga ta ina za ta gano Ƙaisar ko wata baƙuwar halittar da ba jinsin mutane ba, sai dai ba ta ga komai ba.
Ta sake jingina da jikin motar tana ta karanto duk addu'ar da ta zo bakinta. A haka har suka shigo cikin gari sosai da sosai.
Nana na son karanta Symbols ɗin da take gani, amma ba komai take iya fahimta ba saboda rubutun French. Babbar hanya mai ɗauke da ƙaton gate ta ciki suka wuce.
Ba ƙaramar gajiya Nana ta yi ba, saboda azabar nisan tafiyar da suka shawo ba, ba su ƙarasa ba sai bayan magariba. Kewar ɗan ta ta addabi zuciyarta, tunaninta yadda za ta din ga sintirin tsakanin Agadez da Maraɗi a wannan uwar tafiyar kamar ta ya da shege.