← Book details Zamba Cikin Aminci Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 8 OF 69

Sashe 8

Zamba Cikin Aminci Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ali na ganin ya zauna ya tashi ya nufi doushe d'in ya murda k'ofar ya jita a kule murmushi d'auke da fuskar sa ya juyo ya kali idan AFREED ke zaune ya nufi ya tako a hankali ya nufi gun sa yace "Haba mutumi na miye abin wani rufe k'ofar toillette d'in ka san fa shiga zanyi," ko kallon inda Ali yake baiyi ba bare ya amsa masa, kara fad'ada' murmushi sa yayi yace "Wai dan na ce bazaka iya fitar dani a d'akin ka ba shine ka rufe doushe d'in, to wlh da wasa nike ka isa ma har kayi yawa yi hakuri ban makulin kaga fah an kusa kira magaribah ka ban nayi na gama na fito ko na shirya kamin ayi kiran sallah, nan ma dai shiru bai ce masa komai ba "Dan Allah fah nace AFREED, sai lokacin ya juyo ya kalesa yace "daba sai ka k'wataba nagani d'an raini hankali, in badan gulma, ba ga d'akin ka can ba amma ba zaka ba dan kawai ka takura man zanyi maganin ka, shi dai Ali yana tsaye bai ce komai ba sai murmushi yake d'auko makulin yayi ya mika masa karb'a Ali yayi tare da juyawa ya bar gun ya nufi doushe d'in yasaka makulin ya bude sannan ya juyo yace "Ba dole yaro ya ban makuli ba ya na gudun kada nayi k'asa k'asa dashi, da sauri ya shige doushe d'in tare da kulo k'ofar.

Wani k'ayattacan murmushi me k'ara masa kyau da kwantar da zuciya AFREED ya saki tare da girgiza kai cikin zuciyar sa yace zaka fito ka same ni.

Shirya wa yayi cikin bakin wondo 3 quart (3 quater) da riga fara mai k'ananun hannu wa ya kali kansa a madubi, nida kaina nasan ina da kyau ne AFREED ya fad'a cikin zuciyar sa yana murmushi d'aukar wayar sa dake saman gado yayi sannan ya kwanta a gadon yana dane dane a wayar. Yayi daidai da fitowar Ali daga toillette yazo ya shirya shima kamar yanda AFREED yayi sedai shi na sa kayan jaune (yelow) da fari ne, sannan yazo ya zauna kusa da AFREED, yace "Wai mutumi na yaushe ne zaka tafi marad'i, naji kana cewa zaka d'auki ko da hutun kwana biyu ne ka je ganin tanti Aicha sabida tana tayi ma k'orafin baka zuwa gun ta."

Maido kalon sa yayi gun Ali "Yace nima ban saniba wanan aikin ne zai bar muntun zumucin, ai hutun sati zan d'auka idan nasamu dama kawai da naje sai na d'an huta."

Ali yace "Gaskiya kam idan kayi mata sati zata daina yawan k'orafin da take, sabida ko jiya sai da ta kira mama ta fad'a mata" sauke ajiyar zuciya yayi yace "Itama dai tanti ta cika k'orafi, ni kamar wata mace za'a dage da sai na wani je idan ma a garin nan take da da sauki" seda ya dan yi shiru na kusan minti 2, kamin yace "Da yake sada zumucin zan je nayi kuma dan ta damu dani ya sa ta ke son gani na, bai komi zanje insha Allah ina fatan Allah ya bani iko" Ali ya d'an tabe baki kanan yace "Da daidai zai fi."

Suna cikin tataunawa a kayi kiran sallah magaribah tashi sukayi don yin alwala AFREED ya shige doushe d'in sa, shima Ali fita yayi tare nufar nasa d'akin da bashi wani banbanci dana AFREED ya fad'a toillette dan d'auro alwala."

AFREED na fitowa ya nufi armoir (wardrobe) d'in sa ya ciro jalabiya (doguwa farar riga ) kusan a tare suka fito suka nufi masalacin da ke lik'e da gidan nasu.

*********

Marad'i...

Har cikin makarantar su AFREEN direba ya shiga da motar daidai inda ake tsaya wa ya ja ya tsaya AFREEN ta bude murfi matar tafita direba ya juya ya bar makarantar AFREEN ta juya da nufin barin gun da direba ya ajiye ta, taji an kira sunnan ta juyawa tayi , hango hasina na nufo ta murmushi ta saki daga cikin nikaf sai wanda ya lura zai gane hakan.

Tsaye tayi tana jiran k'araso war hasina, tana k'arasowa gun AFREEN tace "Abikiya ta ustaziya ko ina nata rufe rufe da shi, dake da shigar ki duk ku na birgeni da nima zan iya da na dinga yin irin shigar ki k'awata, in jin dai kin huce daga fushin da kike dani?"

kamo hannun ta AFREEN tayi tace "K'awata kin fiya surutu gaskiya, mi kika min da zanyi fushi dake in dan abin jiya ne yasa kike cewa hakanan kima daina sabida ni ban d'auke shi abin fushi ba ki barmin wanan zance da na riga na manta."

Hasina tace "Allah ko k'awata?" Kai AFREEN ta d'aga alamar eh, rugumeta hasina tayi tace shiyasa nike son ki k'awata baki fushi baki da rik'o tu est trés simple plus que je le pense, que le bon dieu nous laisse ensemble ma chérie," AFREEN ta amsa "Da ameen ma puce tare cewa ke cika ni mana ki wuce muje classe (class) kada profe de comptabilité ya shiga kinfa san halin sa da ko k'afar sa ya aza bakin classe ba me shiga shikenan sai ka jira fitowar sa" sakin ta hasina tayi ta kamo hannun ta tace "To muje."

Suna shiga ajin kowa ya dawo da kalon sa wajen su 'yan ajin nasu nata ga 'yan biyu nan sun shigo "To indai k'awatawancan ku ya kai yau hasina kisa ta bude fuskar ta mu gani" wata daga cikin 'yan ajin tace "Mi zaku gani ga munmunar fuskar AFREEN sabida munin ta fah ne yasa bata barin a ga fuskar ta sai ta nuna wai ita ustaziya, kar dai muga lega ah to ni na dad'e da gano munafurcin ta."

Kwashe wa da dariya 'yan ajin sukayi, a hasale hasina na ta warce hannun ta daga na AFREEN zata nufi gun wada tayi maganar da sauri AFREEN ta riko hannun ta tace "Haba k'awata na aza karatu kika zo a makarantar nan ba fad'a da cece kuce ba, rabu da ita mu ba muda wanan lokacin abinda ya kawo mu za muyi mu koma gida kinga shiru ma ai magana ce."

Koma wa tayi ta zauna ranta a matukar b'ace tama kasa magana sai huci take AFREEN tace "Haba wai hasina miye abin fushi a ciki kin maganar nan da zaki bar ranki ya bace ai sai taji dad'in cewa taci galabar b'ata miki rai, dan Allah saki raki man nida tayi ma abin ma raina bai b'aci ba se ke sai a sannan hasina ta saki ran ta tare da cewa "Ai ni sai a min abu na hakura idan a ka maki kuma na kasa hakura da bari na ki kayi naje na koya mata hankali wlh ba k'armin haushi ta ban ba."

AFREEN tace "Yi hakuri dai k'awata idan muka biye mata mun taru mun zama d'aya kenan" kwafah hasina tayi tare da hararen wace tayi maganar.

Wada tunda taga hasina tayi kukan kura da nufin ta shak'o ta ta sha jinin jikinta. Daga haka malamin su ya shigo suka fara karatu..............
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
*ZANBA CIKIN AMINCI*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸

ECRITE:

_PAR_

*QUEEN ZEEFAT*

Yar
Mutan
Niger

Wattpad@nazhabibou

💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝

☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

_BISMILAHIR RAHAMANIR RAHIM_

Page 7

K'arfe sha biyu daidai suka fito daga aji dama duk ranar da suke comptabilité ko fitowa récreation (break) basayi sai sunyi awa biyar a cikin classe, dan haka a gajiye suka fito, hasina tace "Wash Allah k'awata wly duk na gaji, ga yanda comptabilité ke caza k'wak'walwa ga kuma gajiyar zaman awa biyar ai dole mutun ya gaji wlh," AFREEN tace "Hakane k'awata akwai gajiya kam amma daga mun k'arasa shekara nan wahala ta k'are insha Allah," Hasina ta girgiza kai tace "Allah sa muna cikin masu sa'a Allah kawo k'arshan wahalar mu" AFREEN ta amsa da "Ameen" daidai lokacin da suka kawo bakin k'ofar makarantar sun tardo direban har yazo d'aukar AFREEN.

Hasina tace "K'awata ke har anzo d'aukar ki ma, kije kawai da yamma mun ha'du amma k'awata ki daina saka nik'af mana dan Allah."

Saida ta juyo ta kalleta tace "Je peux pas kallo na ake sosai wasu ma su ma kamar zasu cinye ni wlh sabida kallon k'urila da suke man, nikam banga abin kallo a tatare dani ba, kyau naga akwai wanda suka fini to miye na wani damuna da ido wlh hakan na takura man sosai ba, ina fad'a maki a nik'af ma ban tsira ba bare na bude fuska na hakan ya fi min kedai, na riga da nasa ba idan nace maki zan iya fita a haka to wlh nayi k'arya kunya ma nake ji."

Hasina tace "Shikenan amma taya kike gani zakiyi saurayi a cikin nik'af."
Hararen ta AFREEN tayi tace "Ni ba su ne a gabana kada ki k'aramin wannan zancen su a dole sai sunga fuskar mutun ne zasu ce suna son su kenan fuskar ce suke so ba mutun ba mtsss ku ne samari su ka dama amma ban dani ba wallahi. Wai haka sis Khairat tace man, bari naje direba na jira na."

D'ariya Hasina tayi tace "Gaskiya k'awata bakida dama to yi hakuri."

murgud'a mata baki tayi sannan tayi gaba abinta tace "k'awata seda yamma in Allah ya kaimu. Murmushi Hasina tayi, kamin AFREEN ta k'arasa tasu motar direban su Hasina yazo a tare suka bar bak'in makarantar.

Direba nayin parcking AFREEN ta fito tare da cewa "Baba direba ka juya ka d'auko Zeinab yanzu sun fito itama," direba yace "Yanzu kam d'iyar albarka" daga nan AFREEN ta nufi cikin gidan, tana shiga falon ta tarar da Maman da Tanti a falon da sauri Tanti ta mike ta tarbo ta tare da cewa "oyoyo d'iyata ya gajiyar makaranta" murmushi ta saki tace "Wlh Tanti akwai gajiya kin san fa yau awa 5 biyar mukeyi a cikin aji muna d'aukar darasi ba hutu."
Chapter 8 · 0% Book details