← Book details Zamba Cikin Aminci Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 32 OF 69

Sashe 32

Zamba Cikin Aminci Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

A gagwace suka fito suka shiga mota ta tayar da motar suka bar gidan, gudu take sosai sabida ganin da tayi lokacin tayar da sallah ya kusa gashi kuma har Zaria ne masallaci yake dan daga anguwar su zuwa anguwar da masallaci yake ya akwai nisa sosai

Tana zuwa bata matsaya lura da inda zata yi parking ba kawai ta nufi idan maza ke parking ta ajiye tata motar sannan suka nufi cikin masallacin basu daɗe da shiga ba aka tayar da sallah.

Ana idar da sallar malamai suka shiga yin ɗaurin aure da ya gabata ana gamawa mutane sukayi ta watsewa sannu sannu, a ƙa'idar AFREEN ne idan aka ida sallah sai mutane sun rage sosai kamin take jawo ƴan ƙananan ta su fito tare da ƙawarta Hasina dan tafiya gida.

Hakama yau ta kasance saida mutane suka rage yayi sauran ƴan tsiraru sannan suka fito, har taje zata nufar parking ɗin da mata ke ajiye motocin su, Zeinab tayi saurin cewa "Ai anty ba ana kika ajiye motar ba wajen parking ɗin maza kika ajiye ta."

Da sauri AFREEN ta juyo tana kallon ta tareda waro idon ta alamun firgici tace "Ya akayi har haka ta faru oh ni AFREEN ina hankali nane yaje har nakai mota can na ajiye ban saniba? kuma ke Zeinab kina gani amma kikaƙi sanar dani."

Zeinab ta ce "Wallahi anty dan naga kina sauri ne kuma an kusa tayar da sallah shiyasa amma naso faɗa maki."

"To wanzu dai ba wannan ba ta yaya zan ɗauko mota a parking ɗin ƴan maza tsakanin da Allah ya zani inshiga yurin nan, gashi yanzu nasan da su Fahad sun riga da sun tafi gida, da ba sai nasa ya fito man da ita ba."

Dariya sosai Hasina tayi sannan tace "Besty miye abin wani ɗaga hankalin ki haka? kamar wada idan taje ɗaukar motar mazan cinye ta zasuyi, ki kwantar da hankalin ki muje na rakaki ki fitar da motar ki da kanki baki ga mutane duk sun watse ba tana iya yiyuwa ma motar takice kaɗai cikin gurin nasan yanzu haka ma kowa ya fitar da tasa sabida kinsan maza da uzuriruka."

Sai a sannan ne AFREEN ta ɗan ji sanhi a zuciyarta sai tace masu "To ku tafi mu tafi."

Suna tafiya suna fira har sun kusa ƙarasawa yurin parking ɗin kamar ance AFREEN ta ɗaga kanta aikuwa sai ta tsinkaye shi tsaye jigine da motar sa kansa duƙe ya na danna wayar sa da alama wani yake jira, a take gaban AFREEN ya wanke ya faɗi, kawai sai taja ta tsaya, da kallo su Hasina suka bita sannan Hasina tace "Malama lafiya kikayi mana tsaye kokin fasa ɗauko motar ne?"

Da hannu AFREEN ta nuna mata AFREED da ke tsaye jigine da motar sa yana dan ne dan ne a wayar sa sannan ta marairaice tare dacewa "Kinga da namiji a wajan abinda nayi gudu kenan fah."

Duka suka juyawa suka dubi gun da AFREEN ke nunawa. Ɗan ƙaramin tsaki tsussss Hasina taja tare dacewa "Dan Allah malama ki wuce muje idan zakije bakiga ko lura damu baiyi ba harakokin gabansa ya ke sannan kuma daga motarsa sai takice cikin wajen, kuma ba wani abu zai mana ba kawai muje muma muyi kamar ba mu ganshi ba ki ɗauko motar mu fito c'est tout."

Ba dan taso ba haka ta bisu har suka ƙarasa gun, yaji shigowar su wajen parking ɗin amma ko ɗagowa baiyi ba ya kalle su bare yasan ko su wanene haka kawai dai yaji gaban sa ya faɗi, bai kawo komai a ransa ba sai ma cewa da yayi *la'ilaha illah anta subhanakah inni kuntun mina zalumin* , ya karanta addu'ar nan ne sadin jin dayayi gabansa ya faɗi sannan yaci gaba da abin da yake.

Bai an kara ba yaji maganar Hasina nacewa ma AFREEN "Besty dan Allah yau idan kika ajiye ni gida ki shiga ku gaisa da ummi dan ranar nan tana tambaya ta ke kuma ma ki daɗe ba ki shiga gidan mu ba sedai ki ajiye nia bakin get kiyi tafiyar ki."

AFREED na cikin tunanin mi ya kayo mace wajan parking ɗin maza ko dai tare da mijinta ne take, bai ƙarasa tunanin da yake ba yaji zazaƙa muyar AFREEN mai sanyi da taushi da ɗaɗin sauraro ta dakin dodan kunnansa shi a lokacin da tace cikin sanyayar ta "Wallahi kinga ban faɗa wa maman da papa ba cewa zanjima ko zan biya yani gun Kinga faɗa déjà yau mun ɓata lokaci ba mu koma gida ba, yanzu haka hankalin su nacan ya tashi zasu ce ko lafiya har yanzu bamu dawo ba, gashi fa ke har anguwar ali dan sofo mai uban nisa nan zan kaiki kinga ko kamin mukai ki mu dawo mun karancin wani lokaci."

Tunda ta fara maganar AFREED ya juwo yana kallon ta sosai ya shagalta da kallon ta kamar yana ganin fuskar ta, kuma kamar mai son gano wani abu a tatare da ita, sabida saida ya bisu duka da kallon kamin yake yarda da cewa wada dai ke cikin niƙaf ɗin dai itace ke maganar, sabida yaga baki kowace a rufe sannan yana hango yanda bakinta ke motsi daga cikin niƙaf ɗin sosai a lokacin yaji wani abu ya cakar masa zuciya ba tareda ya shirya jin hakan ba, riƙe daidai satin da yaji abin yayi yana mai lumshe idonsa, kwata kwata baiji ɗaɗin shurun da yaji tayi ba a lokacin da ta kai ƙarshen zancen ta............

😜😜😜😜😜😜😜😜😜😜😜😜😜😜😜😜😜😜😜
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
*ZAMBA CIKIN AMINCI*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸

Écrit

Par

*QUEEN ZEEFAT*

_Ƴar_
_Mutan_
_Niger_

Wattpad@nazichou

💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝

☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

*_BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHIM_*

*Page* : 29 & 30

Tunda ta fara maganar AFREED ya juwo yana kallon ta sosai ya shagalta da kallon ta kamar yana ganin fuskar ta, kuma kamar mai son gano wani abu a tatare da ita, sabida saida ya bisu duka da kallon kamin yake yarda da cewa wada dai ke cikin niƙaf ɗin dai itace ke maganar, sabida yaga baki kowace a rufe sannan yana hango yanda bakinta ke motsi daga cikin niƙaf ɗin sosai a lokacin yaji wani abu ya cakar masa zuciya ba tareda ya shirya jin hakan ba, riƙe daidai satin da yaji abin yayi yana mai lumshe idonsa, kwata kwata baiji ɗaɗin shurun da yaji tayi ba a lokacin da ta kai ƙarshen zancen ta............

"Bawani nan Besty idan kika kira Maman kika faɗa mata cewa zaki kaini gida daga can zaki shiga ku gaisa da ummi ba abinda zata ce dan haka, ki kira maman yanzu nan ki faɗa mata idan kuwa gidan mune ba zaki ba to shikenan har kaini ɗin bana so ki bari zan je na tari adaidaita sahu ya kaini gida ko ma na kira direba kawai," Hasina ta faɗa tana ƙoƙarin bari gun ranta a ɓace.

Da sauri AFREEN ta kamo hannuta da niyyar tsayar da ita gani ranta ya ɓace sannan tace "Dan Allah Besty kiyi hakuri ba gidanku bane banason zuwa wallahi, amma tunda kin matsa bari na kira maman ɗin sai na faɗa mata, ko kuwa mu yaje na sauke su Zeinab a gida sai na gayawa maman cewa zanje gidan ku na dawo daga nan sai mu wuce."

Wani murmushin farin ciki Hasina ta saki sannan tace "Ko kega ƙawata dan shiyasa nake son ki, kinga maman bazata hanaki zuwa gidan mu, gashi kuma tare zamu tafi, kai ummi sai tayi farin cikin gani ki yau ku tafi mu tafi."

Murmushi AFREEN tayi sannan ta buɗe motar duk suka shiga sannan ta tayar suna ƙoƙarin barin gun Ali ya ƙaraso har lokacin nan AFREED bai daina kallon ta ba har ta shige mota, Ali na ƙarosowa yace "Broh na tsayar dakai ko? yi hakuri nasan bakason jira." Firgigit AFREED yayi tare da saurin juyowa yana kallon Ali

Ɗan hararen sa AFREED yayi sannan yace "Dan Allah muje kawai ka wani je kayi zaman ka, ka wani shanya mutane a nan."

Murmushi Ali yayi kamin yake buɗe motar ya shiga mazaunin direba shi kuwa AFREED ya buɗe wajen mai zaman banza zai shiga sai ya juya idan AFREEN suka ajiye mota da zunmar son ya ƙara ganin ta ko da kuwa ba zai samu ganin fuskar ta ba, ko zaiji idan zata ƙara buɗe baki tace wani abu, amma sai yaga wayam aiko sai ya shiga wage wage ko ƙurar motar bai gani ba bale kuma su na cikin motar, cikin zuciyarsa yace to ina sukayi ko sunyi tafiyar su ne ni ban maji lokacin da ta tayar da motar ba har suka tafi, to wacece ita???

Bai kai ga samun amsar tambaya da yake wa zuciyar sa ba ya tsinci muyar Ali nacewa "Wai AFREED mikake jirane da ba zaka shigo mutafi ba, kodai ka fasa tafiya gidan ne?"

Sai a lokacin AFREED ya dawo daga duniyar tunanin da ya lula, tare da ƙarasa shiga motar cikin nutsuwa da kwanciyar hankali sannan ya rufo murfin motar, lumshe idonsa yayi tare da kwantawa jikin kujerar ya shiga tunani yana jin yanda wani abu ke shigar sz ya na ratsa jinin jikinsa, da ƙarfi gabansa ya daɗi a lokacin da ya ke ma kansa tambayar kadai matar aure ce na zauna ina kallon ta Inna lilahi wa'inna illaihi raji'un ya akayi haka ta faru mima ya kaini kallon ta? Ni komi kyau mace ba isheni kallo ba amma na buge da kallon mai niƙaf ma da yanzu haka ko kyau bata shi, da sauri ya furta astagfirllah a tunanin sa a zuciyarsa ya furta kalmar ta istigfari ashe a fili ne sai Ali ya juwo ya kalle sa yaga idonsa a lumshe suke kamin yake maida duban sa ga tit sannan yace "AFREED magana kake?" shiru baice masa komai ba amma yaji abinda ya faɗa.
Chapter 32 · 0% Book details