Sashe 11
Zamba Cikin Aminci Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Juyawa yayi tare da komawa gidan ya sami yaran sun gewaye uwasu na kuka gaba d'aya hada uwa tasu, duk'awa yayi kusa da su yace "Dan Allah Hajia kiyi hakuri ki yafe man ni wallahi babu ruwana acikin abinda suke niyar yi, ki tatara 'ya'yan ki ku bar musu garin nan idan har zaki iya, indan kin ga zaki tsaya karb'a gadon yaranki toh ni me taimakon ku ne wajan ganin an k'watar maku hakin ku daga garesu, ko dan d'an uwana Asmane kun cancanci abubuwa da dama daga gareni sabida mu bai tab'a mana wani abu ba mara kyau kulun shi Alkairi ya ke fata a gare mu ba sharri ba duk da nuna masa k'iyaya da muke shi bai tab'a k'in mu ba Allah nagani dan haka duk abinda kuka yanke ina tare daku duk rantsi duk wuya, shi kuma da ya rigamu gidan gaskiya Allah ya jikan sa ya masa rahama ya sa ya huta." da ameen suka amsa.
Sannan Hajia zakiya ta share hawayen ta tare da cewa "Nagode alhaji Suley kai ne kad'ai mai hali na gari dama tunda na ganka a cikin su nasan ba da son ran ka hakan ke faruwa ba ni da 'ya'ya na mun yafe maka Allah bar zumuncin kuma ni na riga da na wanke hukuncin barin k'asar nan ta Mali tunda ba mahaifata bace dama sabida shi mijin nawa nike zaune a cikin ta amma tunda wanda yafi mu son sa ya karb'i abinsa ba zan zauna ba, haka yaran nan da abina zan tafi sabida in suna gabana hakalina zai fi kwanta kuma idan Allah ya yada za su diga kawo maku ziyara sabida basuda wanda yafi ku, su kuma da sukeso son cinye masu dukiya suje sunci kad'an watarana sai labari, aka rasama mutum bare daud'a duniya bai komi wallahi su suka sani." daga nan tayi shiru tare da goge hawayen da suka zubo mata sukuwa yaran suna tana kuka.
Sauke ajiyar zuciya Suley yayi yace "Amma naso kiyi zaman ki ko dan makarantar yaranki duk da yanzu a cikin hutun karshan shekara ne." saida ta dan nisa kamin tace "Bai komi idan munje zan canza masu makaranta in Allah ya yada tunda karatun Mali da na Niger kusan d'aya ne ba wani banbanci."
"To shikenan amma ita Fati ki barta ta zauna gu na sabida ita tana shekarar ta karshe a université (university) bai kamata a fitar da ita ba idan ta k'arasa shekarar sai ta koma wajan naki, nima ko zan samu ladar rikon maraya kuma na samu damar sauke hak'in da d'an uwana ya tafi ya barmin ko da kuwa a kan tane kad'e zanyi murna haka, ga kuma soyayar da ke tsakanin su da isma'il d'an waje na, da sabida wata ma nufa tawa da zuga naso hana auren su amma yanzu ina goyan bayan had'in nan d'ari bisa d'ari yanzu ne nasan zafi da mahimmancin d'an uwana da baya nan ina ma zai dawo gare mu dan zan nuna masa matsananciyar k'aunar da nake masa kawai ina dane wane sabida a lokacin gurb'atacan halina ya dane mai kyau d'in mugun abu kad'ai ke cikin zuciya ta......
Bai k'arasa maganar ba sabida kuka da ya ci k'arfin sa.
Suma yaran sake fashewa da kuka sukayi mai ban tausayi, Shima alhaji Suley kukan yake sosai kamar wani k'armin yaro mahaifiyar su ma kukan take mai tsanani sabida mutuwar yanzu take dawo masu sabuwa kamar yanzu ne yarasu, sun zama kalar tausayi gaba d'aya ba mai ba wani hakuri.
Sun k'washi kamar minti sha biyar a haka kamin alhaji Suley ke tsagaita nasa kukan yace "Gaskiya munyi babban rashi Allah dai ya jikan sa da rahama, kuyi hakuri yanzu ne kuke da bukata ta a matsayin mahaifi kuma nine nan zan shige maku gaba insha Allah s'il vous plait pardon moi (please forgive me)."
Hajia Zakiya ta tsagaita nata kukan tare da cewa "Alhaji ni ba zan hanaka Fati ba sabida kaima kana da iko a kansu a matsayin ka na wan mahaifin su, amma da'ita zan tafi idan Allah ya sa hutun nasu ya kare sai ta dawo insha Allah nayi maka wanan alk'awarin idai da rai da lafiya, kuma gobe tunda asuba zamu barin garin nan insha Allah sai in sun dawo ganin ku kuma, ita kuma idan sun daidai ta kansu itada isma'il to sai nafi kowa murnar had'in nan kuma komi na hannun ka na baka wuk'a da nama kawai kayi abinda ya dace a yanzu basu da wani gata sai Allah se kai uba garesu dan haka banida damuwa da hakan kuma mu baka mana komi ba idan ma kayi mun yafe."
"Yanzu tun goben zaku tafiba zaki bari ku kara kwana biyu ba?" tace "A'a tafiyar dai zamu yi insha Allah zafi mana zaman nan d'in, kallon yaran yayi tare da mikewa yace to Allah kaimu goben, bin kan yaran yayi da d'aye d'aye ya na shafawa a sanu ya futar "Allah maku albarka ya jikan mahaifin ku kuma ya baku hakuri da juriya rashin sa tare daku."
Da ameen suka amsa sannan ya kali Hajia yace "To ni zan tafi anje ma zan dawo muyi ban kwana insha Allah." Tace "Ba damuwa saika dawo."
Daga nan ya fita ya bar gidan yana mai tausayin su har cikin rashin, umma ta ci gaban da lalashin 'ya'yata har suka hakura kowa ya tashi ya shiga harakokin gaban shi banda sadissu dake zaune har lokacin ya na tunani, daga bisani ya mike ya nufi k'ofa tare da barin gidan ga baki d'aya.
K'arfe hud'u daidai na dare bus d'in su ta bar cikin k'asar Mali don zuwa Niamey a kasar Niger Allah da ikon tun suna gani duhun asuba har gari ya fara wayewa sannu a hankali ha rana tafito haka har yamma tayi duk inda lokacin sallah yayi haka direban motar zaya tsayar da mota kowa ya fito yayi sallah, har Allah da ikon sa ya kawo su cikin k'asar Niger a garin Niamey suna shiga k'arfe biyar da minti goma yayi, suna saukowa daga cikin bus (car) d'in Hajia zakiya tayi wani k'ayatacan murmushi tare da cewa "Alhamdulilah yau na dawo k'asata da zama Allah nagode ma."
A take suka tatare kayansu da aka fido daga cikin motar tare da nufi gun da masu taxi ke tsaye suka musu magana taxi biyu suka d'auka sabida yawan kayan su duk da sun bar wasu a can.
Wata k'ayataciyar anguwa suka nufa tare da yiwa masu taxin k'watance gidan da zasu sauka bakin wani had'ad'en gidan masu taxi suka ja suka tsaye fitowa suka mahaifiyar tasu ta sake sakin murmushi ta sake furta alhamdulilah ala kuli halin, bud'e jakar ta tayi ta fito da key d'in gidan ta bude sannan ta dawo ta biya masu taxin kud'in su, kamin suka dinga jidar kayan su suna shiga gidan da su masha Allah gidan ba k'aramin kyau gare sa ba suna shiga suka gyara abin gyarawa sannan kowa ya nufi d'akin sa don yin wanka, da suka gama shirin suka dawo falo suna neman abinci sabida yinwar da suka k'waso a hanya.
Da suka buga suka buga basu sami komi a cuisine (kitchen) ba sai a ka tura Adamu nema masu abinci kamin ya dawo akayi kiran sallah magarib haka kowa ya nufi nasa dak'in don gabatar da sallah. Sai banyan sallah isha'i Adamu ya shigo gidan d'auke da abinda ya siyoo masu."
Umma ta dube shi tace "Yanzu Adamu sai yanzu ka dawo duk da kasan muna jin yinwa sosai" saida ya d'an nisa yace "Wallahi umma saida na wahala kamin nasamu abin siyowa."
Suna gama cin abincin kowa ya nufi dakin shi don yin bacin gajiya. Haka safiya na wayewa Fati da Mariama suka tafi kasuwa siyar kayan abinci da abinda ba'a rasaba sunna dawo suka nufi magasin (store) suka shirya komi sannan a ka fara hada hada had'a abincin rana haka suka ci gaba da rayuwa cikin farin ciki da annashuwa, yayiinda Hajia ta bud'e kanfanin siyar da shada da lace da atanta ida ta aikawa alhaji Suley kud'i ya na siyo mata shadodi daga mali yana aiko mata lace da atanfa kuwa haka take zuwa da kanta Nigeria ta saro tazo ta siyar masha Allah sanu a hankali kanfanin nata na ciganba cikin yardar ubangiji.
Konci tashi ba wuya a wajan ubangiji yau ya kama saura kwana hud'u a koma école (school) da marecan ranar alhaji Suley ya kira umma yake tambayata ya butun da wowar Fati makaranta Mali? tace "ka kwantar da hankalin alhaji insha Allahu alk'awarin da nayi maka yana nan ban tada shi ba nan da kwana biyu zata zo in Allah yayada" daga cikin wayar aka amsa "Da Allah ya kaimu."
Da dadare Hajia Zakiya ta tada ma Fati maganar kan cewa jibi zata tafi Mali insha Allah sabida da d'azu alhaji Suley ya kira kan maganar, mayar da kanta k'asa tayi tace "Umma gaskiya ni ban zan koma ba."
"Ko sabida mi kika fad'i haka?" ba tare da ta d'ago ba tace "Kawai ku kuna nan ni ina can ban iya zama ida baki nan gaskiya umma kawai kice wa baba ya yi hakuri."
Sak'e umma tayi tana kalon ta kamin tace "Ki k'wantar da hankalin kin Fati kije kawai ki k'arasa karatun ki can d'in Allah na tare dake kuma baban ku Suley da matar sa za su kula dake kamar yanda zanyi, ga isma'il saurayin ki zai fi kowa kula dake sedai ki rike mutuncin ki, idan baki son zama Mali wa yasaki fara soyaya da d'an uwanki wanda kinsan tôt ou tard tu va retourné laba de que tu sois sa femme (sooner or later you will return to the fact that you are his wife) kiyi hakuri ki tafi tunda mahaifinku na son zuwanki." D'ago da kanta tayi ta kalli mahaifiyar tasu tace "To umma Allah ya kaimu da "Amin" ta amsa sannan ta bar gun.........
Sannan Hajia zakiya ta share hawayen ta tare da cewa "Nagode alhaji Suley kai ne kad'ai mai hali na gari dama tunda na ganka a cikin su nasan ba da son ran ka hakan ke faruwa ba ni da 'ya'ya na mun yafe maka Allah bar zumuncin kuma ni na riga da na wanke hukuncin barin k'asar nan ta Mali tunda ba mahaifata bace dama sabida shi mijin nawa nike zaune a cikin ta amma tunda wanda yafi mu son sa ya karb'i abinsa ba zan zauna ba, haka yaran nan da abina zan tafi sabida in suna gabana hakalina zai fi kwanta kuma idan Allah ya yada za su diga kawo maku ziyara sabida basuda wanda yafi ku, su kuma da sukeso son cinye masu dukiya suje sunci kad'an watarana sai labari, aka rasama mutum bare daud'a duniya bai komi wallahi su suka sani." daga nan tayi shiru tare da goge hawayen da suka zubo mata sukuwa yaran suna tana kuka.
Sauke ajiyar zuciya Suley yayi yace "Amma naso kiyi zaman ki ko dan makarantar yaranki duk da yanzu a cikin hutun karshan shekara ne." saida ta dan nisa kamin tace "Bai komi idan munje zan canza masu makaranta in Allah ya yada tunda karatun Mali da na Niger kusan d'aya ne ba wani banbanci."
"To shikenan amma ita Fati ki barta ta zauna gu na sabida ita tana shekarar ta karshe a université (university) bai kamata a fitar da ita ba idan ta k'arasa shekarar sai ta koma wajan naki, nima ko zan samu ladar rikon maraya kuma na samu damar sauke hak'in da d'an uwana ya tafi ya barmin ko da kuwa a kan tane kad'e zanyi murna haka, ga kuma soyayar da ke tsakanin su da isma'il d'an waje na, da sabida wata ma nufa tawa da zuga naso hana auren su amma yanzu ina goyan bayan had'in nan d'ari bisa d'ari yanzu ne nasan zafi da mahimmancin d'an uwana da baya nan ina ma zai dawo gare mu dan zan nuna masa matsananciyar k'aunar da nake masa kawai ina dane wane sabida a lokacin gurb'atacan halina ya dane mai kyau d'in mugun abu kad'ai ke cikin zuciya ta......
Bai k'arasa maganar ba sabida kuka da ya ci k'arfin sa.
Suma yaran sake fashewa da kuka sukayi mai ban tausayi, Shima alhaji Suley kukan yake sosai kamar wani k'armin yaro mahaifiyar su ma kukan take mai tsanani sabida mutuwar yanzu take dawo masu sabuwa kamar yanzu ne yarasu, sun zama kalar tausayi gaba d'aya ba mai ba wani hakuri.
Sun k'washi kamar minti sha biyar a haka kamin alhaji Suley ke tsagaita nasa kukan yace "Gaskiya munyi babban rashi Allah dai ya jikan sa da rahama, kuyi hakuri yanzu ne kuke da bukata ta a matsayin mahaifi kuma nine nan zan shige maku gaba insha Allah s'il vous plait pardon moi (please forgive me)."
Hajia Zakiya ta tsagaita nata kukan tare da cewa "Alhaji ni ba zan hanaka Fati ba sabida kaima kana da iko a kansu a matsayin ka na wan mahaifin su, amma da'ita zan tafi idan Allah ya sa hutun nasu ya kare sai ta dawo insha Allah nayi maka wanan alk'awarin idai da rai da lafiya, kuma gobe tunda asuba zamu barin garin nan insha Allah sai in sun dawo ganin ku kuma, ita kuma idan sun daidai ta kansu itada isma'il to sai nafi kowa murnar had'in nan kuma komi na hannun ka na baka wuk'a da nama kawai kayi abinda ya dace a yanzu basu da wani gata sai Allah se kai uba garesu dan haka banida damuwa da hakan kuma mu baka mana komi ba idan ma kayi mun yafe."
"Yanzu tun goben zaku tafiba zaki bari ku kara kwana biyu ba?" tace "A'a tafiyar dai zamu yi insha Allah zafi mana zaman nan d'in, kallon yaran yayi tare da mikewa yace to Allah kaimu goben, bin kan yaran yayi da d'aye d'aye ya na shafawa a sanu ya futar "Allah maku albarka ya jikan mahaifin ku kuma ya baku hakuri da juriya rashin sa tare daku."
Da ameen suka amsa sannan ya kali Hajia yace "To ni zan tafi anje ma zan dawo muyi ban kwana insha Allah." Tace "Ba damuwa saika dawo."
Daga nan ya fita ya bar gidan yana mai tausayin su har cikin rashin, umma ta ci gaban da lalashin 'ya'yata har suka hakura kowa ya tashi ya shiga harakokin gaban shi banda sadissu dake zaune har lokacin ya na tunani, daga bisani ya mike ya nufi k'ofa tare da barin gidan ga baki d'aya.
K'arfe hud'u daidai na dare bus d'in su ta bar cikin k'asar Mali don zuwa Niamey a kasar Niger Allah da ikon tun suna gani duhun asuba har gari ya fara wayewa sannu a hankali ha rana tafito haka har yamma tayi duk inda lokacin sallah yayi haka direban motar zaya tsayar da mota kowa ya fito yayi sallah, har Allah da ikon sa ya kawo su cikin k'asar Niger a garin Niamey suna shiga k'arfe biyar da minti goma yayi, suna saukowa daga cikin bus (car) d'in Hajia zakiya tayi wani k'ayatacan murmushi tare da cewa "Alhamdulilah yau na dawo k'asata da zama Allah nagode ma."
A take suka tatare kayansu da aka fido daga cikin motar tare da nufi gun da masu taxi ke tsaye suka musu magana taxi biyu suka d'auka sabida yawan kayan su duk da sun bar wasu a can.
Wata k'ayataciyar anguwa suka nufa tare da yiwa masu taxin k'watance gidan da zasu sauka bakin wani had'ad'en gidan masu taxi suka ja suka tsaye fitowa suka mahaifiyar tasu ta sake sakin murmushi ta sake furta alhamdulilah ala kuli halin, bud'e jakar ta tayi ta fito da key d'in gidan ta bude sannan ta dawo ta biya masu taxin kud'in su, kamin suka dinga jidar kayan su suna shiga gidan da su masha Allah gidan ba k'aramin kyau gare sa ba suna shiga suka gyara abin gyarawa sannan kowa ya nufi d'akin sa don yin wanka, da suka gama shirin suka dawo falo suna neman abinci sabida yinwar da suka k'waso a hanya.
Da suka buga suka buga basu sami komi a cuisine (kitchen) ba sai a ka tura Adamu nema masu abinci kamin ya dawo akayi kiran sallah magarib haka kowa ya nufi nasa dak'in don gabatar da sallah. Sai banyan sallah isha'i Adamu ya shigo gidan d'auke da abinda ya siyoo masu."
Umma ta dube shi tace "Yanzu Adamu sai yanzu ka dawo duk da kasan muna jin yinwa sosai" saida ya d'an nisa yace "Wallahi umma saida na wahala kamin nasamu abin siyowa."
Suna gama cin abincin kowa ya nufi dakin shi don yin bacin gajiya. Haka safiya na wayewa Fati da Mariama suka tafi kasuwa siyar kayan abinci da abinda ba'a rasaba sunna dawo suka nufi magasin (store) suka shirya komi sannan a ka fara hada hada had'a abincin rana haka suka ci gaba da rayuwa cikin farin ciki da annashuwa, yayiinda Hajia ta bud'e kanfanin siyar da shada da lace da atanta ida ta aikawa alhaji Suley kud'i ya na siyo mata shadodi daga mali yana aiko mata lace da atanfa kuwa haka take zuwa da kanta Nigeria ta saro tazo ta siyar masha Allah sanu a hankali kanfanin nata na ciganba cikin yardar ubangiji.
Konci tashi ba wuya a wajan ubangiji yau ya kama saura kwana hud'u a koma école (school) da marecan ranar alhaji Suley ya kira umma yake tambayata ya butun da wowar Fati makaranta Mali? tace "ka kwantar da hankalin alhaji insha Allahu alk'awarin da nayi maka yana nan ban tada shi ba nan da kwana biyu zata zo in Allah yayada" daga cikin wayar aka amsa "Da Allah ya kaimu."
Da dadare Hajia Zakiya ta tada ma Fati maganar kan cewa jibi zata tafi Mali insha Allah sabida da d'azu alhaji Suley ya kira kan maganar, mayar da kanta k'asa tayi tace "Umma gaskiya ni ban zan koma ba."
"Ko sabida mi kika fad'i haka?" ba tare da ta d'ago ba tace "Kawai ku kuna nan ni ina can ban iya zama ida baki nan gaskiya umma kawai kice wa baba ya yi hakuri."
Sak'e umma tayi tana kalon ta kamin tace "Ki k'wantar da hankalin kin Fati kije kawai ki k'arasa karatun ki can d'in Allah na tare dake kuma baban ku Suley da matar sa za su kula dake kamar yanda zanyi, ga isma'il saurayin ki zai fi kowa kula dake sedai ki rike mutuncin ki, idan baki son zama Mali wa yasaki fara soyaya da d'an uwanki wanda kinsan tôt ou tard tu va retourné laba de que tu sois sa femme (sooner or later you will return to the fact that you are his wife) kiyi hakuri ki tafi tunda mahaifinku na son zuwanki." D'ago da kanta tayi ta kalli mahaifiyar tasu tace "To umma Allah ya kaimu da "Amin" ta amsa sannan ta bar gun.........