← Book details Zamba Cikin Aminci Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 10 OF 69

Sashe 10

Zamba Cikin Aminci Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Alhaji Asmane Sanga haifafan kasar Mali ne kuma rik'ak'en dan kasuwa ne, yana da da shaguna uku na sayar da shadodi wanda sukayi fice a k'asar ta Mali sabida bubu kalar shadar da babu a cikin shagu nan sabida idan kaje wani gun baka samu shada ba shi nashi shagon idan kazo zaka samu shiyasa yayi fice kowa yasan da shagu nan sa a k'asar, yana da mata guda mai suna Hajia zakiya wada ita yar kasar Niger ce a jahar Zinder su had'u ne a ta dalin zuwan da ya tab'ayi Niamey bud'e wani katafaren shagon shadodi a garin, ita kuma ta zo yin soutenance kinta ta karshen karatu, to tunda ya ganta ya kwalafa rai a kanta saida Allah yayi har ya aure ta dama iyayen ta ba wasu masu k'arfi ba ne to ko da suka ga mai kud'in danda nan suka amince a ka d'aura aure a kaita Mali, shekarasu guda da aure Allah ya bata haihu ta samu d'iya mace aka samata fati, Fati na da shekara uku aka haifi Mariama, sannan Adamu, da shekara biyar a ka haifi sadissu, to tunda ga kan sadissu haihuwa ta tsaya, yara sun tashi cikin gata da tarbiya ta kowane fanni da karatu islamiya da na boko babu wanda suka bari a baya.

Sadissu na da shekara 12 a duniya Allah yayi wa alhaji Asmane Sanga rasuwa saka makon wata irin rishin lafiya metsanani da ta same shi ta tsawon sati biyu, wani dare juma'a yace ga garin ku mutuwar da ta girgiza matar shi da ya'yan shi amma banda dangin sa, sabida ana yi sadar uku suka zo ma da matar margayi maganar ce wai tatara ta koma garin su ta bar masu yaran su zasu kula dasu da dukiyar tunda suma iyayen su ne ta nuna masu kan bata yarda da abinda suke so ba sudai bata gadon ya'yanta su tatara su bar masu garin, suka nuna mata da ba haka nan ba, to da ta gane dukiyar yaran ce suke son ciyewa, sai tace masu su bar mata yaranta ta tafida su in yaso sai su rike dukiyar can su dinga juya masu, aiko suna jin haka a take suka amince dama su dukiyar ce suke so wani daga cikin su yace to hakama yayi,Tare da miko mata 20000 wai suyi kudin Mota, girgiza kai tayi alamar bazata k'arba haka wanda ya miko mata da kudin ya mayar abinsa cikin aljihu da tak'i amsa tare da cewa "Yaushe zaku tafi."

Tace "Gobe insha Allah", suka amsa da "Allah ya kaimu," tare da juya wa suka bar gidan.

Tun daren ranar Hajia zakiya ta fara had'a kayan ta da na yaranta tare da taimakon babba yarinyar ta Fati, suna cikin gyaran kayan fati tace "Umma lafiya kike ta hada kayan mu" saida umma ta nisa kamin tace "dagin mahaifinku ke son na bar musu kasar sabida dukiyar da d'an uwansu ya bari su ce na barku a hannu ni kuwa nace ban yada ba sabida Allah kadai yasan kalar rayuwar k'uncin da za kuyi a hannun su sabida dama tun mahaifinku na da rai ba kaunar mu suke ba ni daku gaba daya, sabida ni ina 'ya Niger sukuwa 'yan Mali kuma suka so ya auri 'yar uwarsa yaki kuma shima ba kaunar sa suke ba kawai dan yana da arziki ne tunda shi kadai ne shima ga maihaifiyar sa duk sauran 'yan uba ne, amma bai tab'a nuna masu banci ba ko na bar ku nan wahala zaku sha shiyasa zan tafi daku."

"Umma muma bamu yarda ma ki bar mu gunsu k'arfar ki k'afar mu to dukiyar Abba mu fah su zaki bar mawa."
"To dama sabida mi suke so na barku don su rike dukiyar sa ne, ni kuma nace su rik'e d'in su bar min ku don ku fiye man komi a duniyar nan shi ne dalilin amince war su."

To mama ke da ba aikin da kike baki kasuwar komi to dami zaki rike mu yakamata ko wasu 'yan kud'i su baki ko wata kasuwa kiyi."

"Hum yaro yaro ne karki damu Fati Allah na tare damu , kuma bancin haka akwai wata millions 10 da tarkardun wani gida na mahaifin ku dake cikin garin Niamey da ya tab'a bani kamin ya kwanta rishin lafiya yace na ajiye masa kuma kada na fad'awa kowa, to kinga idan Allah yayi masu albarka shikenan a cikin su zan samu na k'arasa biya muku kudin makaranta mu d'anyi abinda ba'a rasa ba shi kuwa gidan muje cikin mu zauna, da yarda Allah ba zamu tagayaraba Allah dai ya ru fa mana asiri duniya da lahira."

Da "ameen" fati amsa wada ta fahimci inda uwar ta dosa.

Da ganan suka ci gaba da gyaran kayan, su na idarwa ta tataro yaranta ta fad'a masu da gobe zasuyi tafiya zuwa kasar Niger kuma ba zasu dawo kasarnan ba har abada amma bata sani ba kosu watarana suji suna son gani dangin mahaifin su to fah baza ta hanasu zuwa sada zumunci ba, ta had'a da cewa nasan kuma kowa nan ku nason yi min tambaya? Ban baku wanan damar ba sabida yanzu banida kyakyawa amsar baku ha bani da wata isha shiyar nutsuwa don haka kowa ya bar tambayar shi har watarana, daga haka kowa yayi gum da baki sa ba damar yin tanbaya.

Washe gari da safe wajan karfe 9 sun gama karyawa..............
,

Muje zuwa.......

Godiya ta musan man a gareku masoya na💞
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
*ZANBA CIKIN AMINCI*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸

ECRITE:

_PAR_

*QUEEN ZEEFAT*

Yar
Mutan
Niger

Wattpad@nazhabibou

💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝

☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

_BISMILAHIR RAHAMANIR RAHIM_

Page 8

Washe gari da safe wajan k'arfe tara sun gama karyawa kenan se ga dagin mahaifin su biyu sun shigo, ko salama babu tare da cewa "Yo zakiya har yanzu baku tafi ba?" juyowa tayi da sauri sabida kamar daga sama taji maganar tunda bata ji shigowar su ba, da ido ta bisu tare da watsa masu wani mugun kallo tace "wai ku mi mu ka tare muku? duka yau kwana biyar da rasuwar bawan Allah nan amma duk kun bi kun takura man, nina ce zan tafi kuma ni nayi niyar tafiya, idan naga dama sai na yi zamana kuma ba yanda za'ayi dani tunda gidan nan na miji na ne da ya'ya na, sai in nayi ra'ayi ne zan tafi ba wai tilasta min zakuyi ba idan naga dama ba ida zani, ku dai kawai ku gode ma Allah inason koma wa k'asata ta haihuwa, da ba dan hakanan ba wly da ba abinda zai sani barin nan d'in wallahi se dai kuyi duk yanda zaku yi Ah to, tunda nawa d'iyan sun girma suma sun isa kula da kansu kuma da dukiyar mahaifin, amma duk da haka na zab'i na tafi da ya'yana sabida a zauna lafiya to kuma sai ku dawo kuna takura man? mun bar muku dukiyar a hannun ku kuma ai kun san hak'i ci zalin marayu ba sai na fad'a maku ba in kun gyara kun sani inbaku gyara ba ma kun sani, sudai sun bar komi nasu hannun ku duk yanda kukeso kuyi daidai ne wallahi kuma kuyi niya ku fita ku bar min gida sabida komi na maku ku kuka ja, idan mun tashi tafiya zan bayar da makulin gidan akai muku sabida ba abinda zanyi da shi ehe."

K'wafa tayi tare da mayar da kallon ta ga abinda take ran ta a matuk'ar b'ace.

Tsaye sukayi sina kallon ta baki bud'e suna tunanin yaushe matar Asmane ta samu baki maida magana, juyawa suka yi suka bar gidan tare da mamaki da tunani iri iri duk jikin su yayi sanyi.

Su na fita k'ofa guda ya kalli guda yace "Anya wanan matar ba so take ta zame mana matsala ba kuwa?" nisa wa wanda aka yiwa tambaya yayi yace "Wallahi ni kuwa tausayi ta bani vraiment elle à besoin d'un peu du temps pour qu'elle puisse se soullager de ce qu'elle resent a cause de la mort de sont mari,sa fait que 5 jours que son mari est decèder, c'est pas bon ce qu'on est entrand de faire, comme maintenant elle a besoin de notre soutient parce qu'elle n'a personne ici que nous et ses enfants (really she needs a little time so that she can relieve herself of what she feels its fact that 5 days that her husband died, it's not good what we are going to do, like now she needs our support because she has no one here but us and her children).

Wani shek'ek'e d'ayan ya kalle sa yace " Ban gane mikake nufi ba, kanaso ka nuna min cewa ka saduda sabida tayi wani w'azin ta can da barazana to Wallahi ahir d'inka mudai bazamu fasa abunda mukayi niya ba Suley sedai kai ka hakura."

Wanda aka kira da Suley yace "To nidai Wallahi na fida hannu na daga cikin wanan rishin gaskiyar na ku na son ku handame dukiyar marayun Allah da basu ji basu gani ba ba ruwana ba hannu na ciki, idan Allah ya tashi k'watar masu hakin su, wallahi naga dai tun uban yaran nan na da rai yake mana abin arziki duk da nuna masa banbanci da muke, muna nuna masa shi d'in uba kad'ai muka had'a da shi, amma shi bai tab'a banbanta mu da kanshi ba, ko ya d'oki wani bare da muhimmanci fiye da mu sabida abinda muke masa amma bai tab'a nunawa ba dan haka ni ba ruwana ku kuje kuyi Allah bada sa'a."
Chapter 10 · 0% Book details