← Book details Zamba Cikin Aminci Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 30 OF 69

Sashe 30

Zamba Cikin Aminci Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ƙarasawa tayi kusa dashi ta zauna a kasan kapet daidai ƙafafun sa, sannan tace "Yaya ina yuni ya hanya da fatan kunzo lafiya?"

"Lafiya lau mukazo Khadija mun sameku lafiya?"

Saida taƙara sune kanta sannan tace "Lafiya lau yaya ya kuka baro su Momy?"

"Lafiyar su lau kidaina jin kunyata kinji ƙanwata ki saki jikinki muyi fira."

Murmushi kawai tayi ta ƙara duke kanta seda ta daci kallon Ali kamin tace "Yaya ina yuni anzo lafiya?"

Wani haɗaɗen murmushi ya sakar mata wanda shi kanshi baisan yayi mata shi ba ita kuwa anan take wata soyayyar ta ƙara shigar ta ai da sauri ta kauda idonta daga gareshi. Ali ya amsa da "Lafiya lau Khadija ai ni yau ina fushi dake ne sabida kwata kwata yau baki ganina sai AFREED?"

Kara sunkuyar da kan nata tayi tana jin soyayyar sa na ƙara shigar ta sabida duk wani harafi da zai faɗa a maganarsa tsikar jikinta tashi take, tace "A'a yaya ba haka bane?"

Ali yace "Yane idan bahaka bane ba gashi gunsa kikaje kika zauna ba, to idan dai ba haka bane ki taso ki dawo kusana muyi hira."

Kasa tashi tayi daga inda take sabida ita kaɗai tasan halin da zata shiga idan har ta koma kusa dashi anan ɗin ma da take zaune ya ta ƙara bare ta koma kusa dashi."

Murmushi AFREED yayi yace Khadija tashi ki koma kusan sa shi nikam Ummi ta isheni abukiyar hira shi kuwa ai tunda surutu ya masa yawa ai ko mutum goma zai iya haɗawa yayi caca baki dasu."

Tayi niyar tashi sai ga su Fariya sun fito daga ɗaki, suna ƙarasowa nan cikin falon su shayo kwalliya masha Allah sai zuba kamshi suke.

Suna ƙarasowa suka nemi guri suka zauna tare da cewa "Tanti ina yaya Umar ne yazo ya kai yawo."

Tanti dake ta sauraran ɗiyan nata tun ɗazu tana murmushi tace "Yanan saman hanya tessaoua yaje tunda safe wajan wani aiki yanzu kunga ya shigo to wai da kukayi shirin fita abinci fah?"

Ali yace "Gaskiya dan ni yinwa nakeji kusan ni bana jimirin yunwa ko."

Tanti tace "Shikenan ku tashi muje kuci man ko kuwa a kawo abincin nan?"

Ali yace "Tanti akayo nan kawai sai ci a saman kapet."

Haka kuwa akayi suka nemi guri Fariya Farisa da Khadija sukaje su ɗauko kulolin daga kan dinning su ka kawo su nan cikin falon Khadija duƙa tayi servir ɗin su ta zubawa kowa sannan suka gewaya gaba ɗaya suka faracin abincin cikin farin ciki...........
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
ZAMBA CIKIN AMINCI
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸

Écrit

Par

*QUEEN ZEEFAT*

_Ƴar_
_Mutan_
_Niger_

*_Wattpad@nazichou*_

💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝

☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003

*_BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHIM_*

*Page* : 27 & 28

Suna cikin cin abincin Umar babban ɗan Tanti ya shigo falon da sallama ɗauke da bakinshi, gaba ɗaya suka ɗago tare suna masu amsa sallamar da murmushi ɗauke da fuskokinsu, da gudu ummi tashi daga kan ƙafafuwan AFREED taje ta rungume ɗan uwan nata, dariya yayi tare da ɗaukar ta sannan ya ƙarasa inda suke.

Mahaifiyarsa ya gaida ta masa da murmushi ɗauke a fuskar tana masa ya hanya, juyawa ya gun su AFREED yana dariya yace "Wata sabon gani broh yau kaine da kanka zaune cikin garin Maraɗi a cikin falon mama, yaude kam mama zata kwana farin ciki sabida kullum bakinta ya dauke da sunanka Ita dai AFREED, broh da ace lokacin damina ne yau da Allah sai yayi ruwa bansa wace addu'a bace mama tayi har Allah ya kaɗo mata kai yau garin nan."

Dariya sosai Ali yayi sannan yace "Kai AFREED kowa yasan baka son fita daga garin Niamey kowa nason ganin ka amma kaje ka zauna gu ɗaya."

Murmushi AFREED yayi yace "Umar irin wannan shari haka kamar dai ban taɓa zuwa Maraɗi nan ba to ni na dawo nan da zama bakiɗaya ma ta man shari sai ta ƙare, kai kuwa Ali ɗan sa ido duk abinku baku isa ku haɗa Ni da tanti ta ba."

Umar yace "Ba wani shari an san halinka ne ni yanda ma akayi ka zauna anata hira da kai haka ko ka iya ɗumine yanzu? dan nasan magana wahala take maka AFREED."

Ali yace "Ashe kaima ka gano haka tunɗa zu yake ban mamakin maganar nan da yake da har yanzu banji yace ya gaji ba."

Murmushi AFREED yayi baice komai ba sannan cema Umar "Yanzu dai zauna kaci abincin nasan ka kwaso yunwa idan ka gama sai ka ƙarasa min iskancin ai naga kaima ba zuwa garin namu kake ba."

Umar yace "Aidai nafika tunda ni ko wata uku bayin ba da naje garin naku ba."

AFREED yace "To anji zauna dai ka cika cikin ka tukun na."

Zama Umar yayi sannan ya kalli su Farisa yace "ƴan biyun Momy ashe daku akazo da fatan kunzo lafiya wannan gumkin ɗan uwan nawa injin dai bai ta kura ku ba a hanya."

Murmushi su kayi tare sannan sukace "Yaya ina yuni lafiya lau muka zo kuma babu abinda yaya yayi muna a tare suke maganar babu mai wuce ɗan uwan sa kamar ɗaya tasan abinda ɗayar zata ce.

Umar yace "Allah ya mashi sa'a da ace ya taɓa min ku ai dan yanzu na rama maku."

Murmushi AFREED yayi baice komai ba sabida ya fah gaji da maganar nan dan ba ƙaramin ƙoƙari yayi ba yau na magana mai tsayi da yayi har haka."

Umar ya dubi Ali yace "Gaskiya Ali kana fama ban masan ya kake zama da wannan ɗan uwan naka ba?"

Ali yace "To ya zanyi haka nan dai nike ɗan hakuri da shi kamin ya ɓata min rai na bigeshi ai matar sace ke da aiki nan gaba."

Gaba ɗaya suka kwashe da dariya har da tanti, AFREED ya kalli su Farisa ya game fuska kamar bai taɓa dariya ba yace "Kun wani zauna kuna yiwa mutan dariya dan samun yuri to maza ku bar nan tun kan raina ya ɓace nayi maganin ku." sumi sumi suka tashi su duka harda ummi suka bar gun dama su daɗe da gama cin abincin har sun gyara gun da suka gama.

Tanti da farin ciki ya cika mata zuciya ta kalli AFREED tace "Ji AFREED ka korar min yara ba sai ka bari ayi ta duramar nan da suba suma su rage dare tunda basu sami zuwa yawon ba."

AFREED yace "Tanti kawai sai su zauna suna jin hirar mutane kawai su rai namu."

Tanti tace Hum AFREED uwayan son girma."

Hira sukaci gaba dayi har dare ya soma yi sannan sukayi wa Tanti sallama suka koma ɓangaren su, suna shiga Umar yayi nasa ɗakin tare da ce masu ya shiga yayi wanka dan cewa yayi tunda su AFREED sunzo to yadawo ɓangaren su da zama ya baro nasa sai kuma idan sun koma tunda ɓangaren da su AFREED suka sauka yana ɗauke da ɗakuna huɗu ne.

Umar na shiga ɗaƙin shi Ali ya dubi AFREED yace "Broh yana ga yau kanta hira sosai ka saki jiki ana kwasa hira dakai don gaskiya kaban mamaki ko dai ka fara koyon yawan magana ne bansani ba?"

Kallon shi AFREED yayi sannan yace "Wallahi broh daurewa kawai nake sabida tanti tana farin cikin zuwana bai kamata nayi gum da baki naba dan gudun kar farin cikin nata ya koma ciki sabida rashin magana ta duk da itama tasan ban wani cika yawan magana nayi ba, amma bancin haka wallahi nan duk nagaji da maganar da nayi yau."

Ali yace "To haka da kayi yayi daidai yanzu sai kaje ka kwanta dan bakin naka ya huta tunda ma kaga dare yayi."

AFREED yace "Hakane bari naje na ɗan watsa ruwa sai na kwanta."

Daga nan kowa ya nufi ɗakin sa domin samun bacci da hutu mai kyau,sedai muce asuba ta gari su AFREED.

**** **** ****

AFREEN suna fita daga gida direct wajan shopping suka nufa suna ida shopping sukayi gida anty Fauziya, sosai tayi farin cikin ganin su haka su ka wuni gidan, a nan ne Firdaoussi ke yi Hasina maganar KAMAL, Hasina najin zancen tayi farin ciki sosai, ta ƙara bawa AFREEN kwarin gwiwar kula shi haka dai suka tasa ta a gaba suna nuna mata mahimmanci fara soyayya sukace dan Allah ta bashi dama.

Sai bayan magariba suka bar gidan anty Fauziya sabida saida suka mata girki, don sunce tunda sun zo ta huta gata da tsohon ciki na wata shida kuma mai mata aiki ta tafi garin su sabida rasuwa da kakar tayi shine taje gaisuwa, da zasu tafi anti Fauziya ta haɗa kowace daga cikinsu da leda ɗoke da kayan kwalliya da turaruka masu ɗadin kamshi, ita kuwa AFREEN turaruka kaɗai ta saka mata sabida tasan ita ba ma'abuciyar kwalliya bace.

Suna fita daga gidan anty Fauziya suka nufi anguwar su Hasina suka ajiye ta a ƙofar gidansu sannan suka nufi gida a bakin ƙofar gidan su Firdaoussi AFREEN taja ta tsaya sannan itama Firdaoussi ta sauka tana masu saida safe, idan masu karatu basu manta ba ai nace muku gida biyu ne a haɗe waje guda wato gidan Alhaji Sadisu mahaifin su AFREEN da na yayan shi Alhaji Adamu wanda shi Alhaji Sadisu ne ya gina wa ɗan uwan nasa dan haka suke makwabtan juna katanga ce kawai ta rabasu to Firdaoussi ɗiyar Alhaji Adamu ce kuma itace suke ƴan wari guda da AFREEN.

AFREEN na shiga cikin gidansu tayi parking ɗin motar ta wajan da suke ajiye motoci sannan suka fito ita da Zeinab suka nufi ɓangaren Hajiya Zakiya wato kaka su wada ta haifi mahaifin su, suna shiga suka tardo ta saman darduma da alama sallah ta ƙare, zama sukayi saman kujerun dake cikin folon sannan suka ce Mamy (Kaka) ina wuni ya yunin gida?"

Da murmushi take kallon su sannan tace "Lafiya ƴan albarka jikoki na sai yanzu kuka dawo daga gidan Fauziyar? ɗazu Sadisu ya shigo nan nake tambayar sa AFREEN dan naga duk yau baki shigo nan ba, sai yace ai kuna gidan Fauziya."

Murmushi AFREEN tayi tace "Eh Mamy wallahi sai yanzu muka dawo mun kama mata aiki ne kinsan tayi nauhi sosai cikin jikin tane ɗan wata shida amma saika kace yau ko gobe zata haihu da tsananin girman sa."
Chapter 30 · 0% Book details