Sashe 12
Zamba Cikin Aminci Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ranar da Fati zata tafi ta had'a mata shatara ta arziki don ta kaiwa 'yan k'asar Mali, har gidan bus (car) suka rakata tana ta kuka su ne basu dawo gida ba har saida suka ga tafiyar motar su tana kuka tana d'aga masu hannu har suka ba'ce mata itama umma saida ta saki 'yan k'walla.
**************
BAYAN SHEKARA HUDU
Abubuwa da yawa sun faru wanda cikin shekaru hud'un nan hada auren Fati da Isma'il wanda suke zaune a k'asar Mali cikin so da k'auna tare da kwonciyar hankali da nutsuwa da yaron su guda Abdallah hada tsohon ciki a jikin itama Mariama tayi aure a Zinder inda take d'auke da tsohon ciki, shi kuwa Adamu ya kamala karatun shi yana kulla da kanfanin mahaifiyar su da matar sa guda wada umma ce ta had'a auren su tare da d'iyar 'yar uwar ta dake garin Maradi, yana zaune yuri guda mahaifiyar sa da matar sa, shi kuwa sadissu yana université (university) ta garin Agadez yana shekara karshe ta doctorat.
Arzikin mahaifiyar su hab'aka yake masha Allah komi na rayuwa sunada shi sai abinda ba'a rasa saba sabida Hajia Zakiya tayi arziki sosai ba wanda bai santa ba a cikin garin Niamey, yanzu ba abinda zasu ce sai suce alhamdulilah Allah ya gama masu komi a rayuwa.
Watarana sadissu ya fito daga cikin makaranta zai d'an zaga gari a lokacin yana da 28 ans masha Allah kyakyawan saurayi dashi mai jini ajika kamanin sa na Malienne sun fito sak kamar mahaifi sa dogo dashi abin birgeewa da ko wace mace 'yan mata bouzaye na ta haukan shi amma shi ko ta kansu bai bi duk da kusan yanda bouzaye keda kyau da har idan ka kalleso bakason ka d'auke ido, amma shi ko akansa, a yanda ya tsara ma kansa baida ma lokacin soyaya a yanzu sai ya kamala karatu, kwatsame yana fito daga université ya d'an yi nisa da makarantar tasu ya kai bakin titi har zai tsalaka hanya yaji kuka kamar na mace a kusa dashi.
Juyawa yayi da k'arfi gefan da yake jin kukan, wata matashiyar budurwa ya gani duk'e ta had'a kai da gwiwa tana kuka kamar ranta zai fita............
Na Queen Zeefat
Kuyi comments masoyan zanba cikin aminci hakan zai sa nayi wani page💓💖❤️
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
*ZANBA CIKIN AMINCI*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
ECRITE:
_PAR_
*QUEEN ZEEFAT*
Yar
Mutan
Niger
Wattpad@nazhabibou
_BISMILAHIR RAHAMANIR RAHIM_
Page 9
Juyawa yayi da k'arfi gefan da yake jiyo kukan, wata matashiyar budurwa ya gani duk'e ta had'e kai da gwiwa tana kuka kamar ran ta zai fita, d'auke kan shi yayi daga kallon ta da niyar ya bar gun, kawai sai ya tsintsi kansa da kasa barin wurin sake juyowa yayi ya kalle ta take ya ji wani matsanacin tausayin ta ya shige sa.
D'aga k'afafun sa yayi ya k'arasa kusa da ita ya tsuguna yace "Asalama aleikum baiwar Allah lafiya mi yasa meki kike zaune bakin hanya kina kuka."
Firgigite tayi ta d'ago da sauri lokaci d'aya ta mike tsaye yarinyar buzuwa ce mai massifar kyau duk da hawaye da suka cika fuskar ta da idanun ta duk sunyi ja haka duk illahirin fuskar yayi ja abinka ka farin mutum, hakan bazai hana ka hango tsananin kyau da Allah ya mata ba sabida ko a cikin buzaye samun mai kyau irin nata sai an tona kuma sai ansha wuya gun neman koda za'asamu mai kyau irin nata sabida kyakyawa ce ta gasken gaske.
Zuba mashi manyan idanun ta tayi cikin na shi.
Take yaji wani abu ya tsirga mashi cikin zuciya da sauri ya k'auda idon sa yana kallon wani gefe yace "Baiwar Allah magana nake maki ko kurma ce ke ban sani ba."
Har yanzu idon ta na kanshi amma ta kasa magana, kusan minti biyu da yaji shiru ya juwo dan yaga ko ta tafi ne, sai yaga tana tsaye, har lokacin shi take kallon hawaye na k'ara bulbulowa ga fuskar, kuma tak'i magana, ganin haka yasa ya k'auda idonsa sabida bai jurar kallon cikin k'wayar idanun ta don da sun had'a ido wani abu yake ji yana masa zirrrrrrrrr tun daga saman kanshi har cikin tafin k'afar sa.
Da yaga bata da niyar yin magana sai ya juya da niyar barin gun da sauri ta rik'o hannu shi ta k'ara fashewa da wani matsanancin kuka mai tab'a zuciya.
Juyowa yayi da k'arfi yana fuskantar ta yace "Dan Allah baiwar Allah ki daina kukan nan wallahi har cikin rai nake jin wanan kukan naki."
Har yanzu dai kallon sa take hannuta rike da na shi kuma tak'i cewa komai, amma ta bar kukan sai hawaye dake anbaliya a fuskar ta kamar ruwan teku.
K'ara kallon fuskar yayi da tagama yin ja yace "Ki daina kukan nan kada kisama kanki ciwon kai, kuma ni ki sakeni na tafiya ta tunda baza kiyi magana sabida na lura ke ba kurma bace kina jin duk abinda nake fad'a." ya fad'i haka tare da fizge hannu sa daga nata.
K'ara sauri riko hannu tayi cikin wata siririyar muyar ta bud'e baki da kyar cikin kuka tace "Dan Allah ka taimaka min aike na akayi da 2000f shine yanzu ina shirin tsaleke titi wasu maza biyu suka zo suka sabce suka gudu gashi yanzu idan naje gida nace an sabce min wallahi dukan mutuwa za'a man ka taimaka min dan kashe ni zatayi, tun d'azu nake nan ba wanda ya min magana bar inyi tunanin za'a taimaka min se kai duk wanda na tsayar nace dan Allah ya taimaka min sai ya fara min wata maganar banza ni kam ba halina bane."
Tunda ta fara maganar ya k'urawa d'an k'aramin bakin ta ido yana kallon yanda take magana sannu sannu cikin nutsuwa da kuma yanda bakin ke motsawa. Jin shiru baice komai ba yasa ta d'ago da kanta ta ga ita yake kallo ko k'yabtawa baiyi da sauri ta saki hannu nasa tana ja da baya d'aga mata hannu yayi alamar ta tsaya sabida bakinsa ya masa nauhi, ja tayi ta tsaya d'an nesa dashi jikin ta na rawa sabida gani take shima d'aya yake da sauran mutanen da tayi ta tsayar wa, wanda a farin ganin shi da tayi bata mishi wannan kallon ba amma yanzu da taga ya tsura mata ido yana kallon ta kawai sai take ganin shima d'aya yake da sauran.
Cikin sark'ewar murya yace "Baiwar Allah dakata ba cutar dake zanyi ba tambayar ki kawai zanyi."
"To.... i...na jin...ka," ta fad'a cikin in ina hawaye na koma zubowa a fukar ta.
Shiru yayi na kusan sakan 5 sannan yace "Miyasa za'a yi miki fad'a idan kince sabce kud'in akayi? Su a gidan basu san.........." Bai k'arasa maganar ba sakamakon katse sa datayi.
Tace "Oh mon dieu (oh my god) idan fad'a ne kawai za'a min da sauki da bazan zauna anan ina asarar hawaye na ba kuma ina neman taimakon jama'a ba, kawai idan zaka taimaka min toh inko ba zaka taimaka min ba? na kama gabana tare da k'ara matso k'walla a idanun ta.
Wata irin ajiyar zuciya ya sauke tare da saka hannun sa cikin aljihun wanda sa ya ciro da kud'in sannan ya k'arasa kusa da ita yace karb'i kije ki siyo abinda aka aike ki siyowa sai ki koma gida, amma dan Allah ki daina tsayawa a hanya kina kuka kina min asarar tsadadin hawayen ki wanan ba girman ki bane kin ga ke ba wata karamar yarinya ba kuma ki daina fitowa ba hijab gaskiya kina barin kowa na kallon surarar jikin ki bazan lamun ta da hakan ban kuma shine yasa duk wanda kika tsayar yake gayami ki magana banza.
Sororo tayi tana kalonshi kamar taga wata sabuwar halita, sake waro ido tayi lokacin da idonta ya sauka kan kud'in dake hanun sa tace "Dan Allah ka rufa man asiri ni fa 2000 nace maka an sabce min ba wai 5000 ba taya zaka d'auki har 5000 ka bani ya zanyi da ita, kuma dakake cewa kan na daina maka asarar hawaye na na za'a kaima cewa kayi hawaye na to taya zan maka asarar su? da kace kada na sake fita ba hijab sabida ba zaka yarda ba to ni shine ban gane ba bawan Allah? Amma zan daina.
Wani irin had'ad'en murmushi ya saki yace "Nima bansan na fad'i hakan ba, amma tunda kince zaki daina ai shikenan kuma yanzu bazaki gane da cewa wanan kukan da kike nine kikewa asarar hawayen ki ba sai nan gaba insha Allah zaki gane, karb'i kud'in ni na wuce.
Saida ta nisa kamin tace "Dan Allah ka rufaman asiri ya zanyi da'ita sedai ka tafi mu tafi na sami canji sai na baka cikon."
D'aga k'afafun sa yayi ya fara tafiya tare da cewa "To mu tafi."
Jerawa sukayi suna tafiya kamar saurayi da budurwa masha Allah couple in su yayi suyi matuk'ar kyau duk idan suka gifta sai an kallesu shi kuwa da ya ga haka sai yai tunanin kowa itace ya ke kallo, tsayawa yayi cak ya daina tafiyar, juyowa tayi tana kollon sa da alama tambaya a bakinta amma kamin tace wani abun shi ya rigata.
Fido da rigar sanyin sa yayi tare da cewa "Karb'i wanan kisa naga kamar kina jin sanyi kuma mutane sai kallon ki suke" dayake lokacin sanyi ne.
Ba musu ta karb'i rigar ta saka ta soma tafiya bin bayan ta yayi da kalo tareda sauke wata kyakyawa ajiyar zuciya sannan ya fara tafiya.
Sun k'washi kusa da rabin awa a hanya suna neman canjin 5000 basu samu ba ja yayi ya tsaya yace kinga ni gaskiya nagaji dayawa kawai kije ni bar miki 5000 d'in juwo tayi ta kalleshi idonta ya shiga sosai cikin nasa wani irin fa'duwar kaba taji tayi sauri k'auda idonta ta tunanin miyasa gaban ta fad'uwa yanzu tayi alhalin tun dazu da take kallon cikin idonshi bata ji hakan ba sai yanzu.
Katse mata tunanin yayi yace "Lafiya kika yi shiru."
**************
BAYAN SHEKARA HUDU
Abubuwa da yawa sun faru wanda cikin shekaru hud'un nan hada auren Fati da Isma'il wanda suke zaune a k'asar Mali cikin so da k'auna tare da kwonciyar hankali da nutsuwa da yaron su guda Abdallah hada tsohon ciki a jikin itama Mariama tayi aure a Zinder inda take d'auke da tsohon ciki, shi kuwa Adamu ya kamala karatun shi yana kulla da kanfanin mahaifiyar su da matar sa guda wada umma ce ta had'a auren su tare da d'iyar 'yar uwar ta dake garin Maradi, yana zaune yuri guda mahaifiyar sa da matar sa, shi kuwa sadissu yana université (university) ta garin Agadez yana shekara karshe ta doctorat.
Arzikin mahaifiyar su hab'aka yake masha Allah komi na rayuwa sunada shi sai abinda ba'a rasa saba sabida Hajia Zakiya tayi arziki sosai ba wanda bai santa ba a cikin garin Niamey, yanzu ba abinda zasu ce sai suce alhamdulilah Allah ya gama masu komi a rayuwa.
Watarana sadissu ya fito daga cikin makaranta zai d'an zaga gari a lokacin yana da 28 ans masha Allah kyakyawan saurayi dashi mai jini ajika kamanin sa na Malienne sun fito sak kamar mahaifi sa dogo dashi abin birgeewa da ko wace mace 'yan mata bouzaye na ta haukan shi amma shi ko ta kansu bai bi duk da kusan yanda bouzaye keda kyau da har idan ka kalleso bakason ka d'auke ido, amma shi ko akansa, a yanda ya tsara ma kansa baida ma lokacin soyaya a yanzu sai ya kamala karatu, kwatsame yana fito daga université ya d'an yi nisa da makarantar tasu ya kai bakin titi har zai tsalaka hanya yaji kuka kamar na mace a kusa dashi.
Juyawa yayi da k'arfi gefan da yake jin kukan, wata matashiyar budurwa ya gani duk'e ta had'a kai da gwiwa tana kuka kamar ranta zai fita............
Na Queen Zeefat
Kuyi comments masoyan zanba cikin aminci hakan zai sa nayi wani page💓💖❤️
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
*ZANBA CIKIN AMINCI*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
ECRITE:
_PAR_
*QUEEN ZEEFAT*
Yar
Mutan
Niger
Wattpad@nazhabibou
_BISMILAHIR RAHAMANIR RAHIM_
Page 9
Juyawa yayi da k'arfi gefan da yake jiyo kukan, wata matashiyar budurwa ya gani duk'e ta had'e kai da gwiwa tana kuka kamar ran ta zai fita, d'auke kan shi yayi daga kallon ta da niyar ya bar gun, kawai sai ya tsintsi kansa da kasa barin wurin sake juyowa yayi ya kalle ta take ya ji wani matsanacin tausayin ta ya shige sa.
D'aga k'afafun sa yayi ya k'arasa kusa da ita ya tsuguna yace "Asalama aleikum baiwar Allah lafiya mi yasa meki kike zaune bakin hanya kina kuka."
Firgigite tayi ta d'ago da sauri lokaci d'aya ta mike tsaye yarinyar buzuwa ce mai massifar kyau duk da hawaye da suka cika fuskar ta da idanun ta duk sunyi ja haka duk illahirin fuskar yayi ja abinka ka farin mutum, hakan bazai hana ka hango tsananin kyau da Allah ya mata ba sabida ko a cikin buzaye samun mai kyau irin nata sai an tona kuma sai ansha wuya gun neman koda za'asamu mai kyau irin nata sabida kyakyawa ce ta gasken gaske.
Zuba mashi manyan idanun ta tayi cikin na shi.
Take yaji wani abu ya tsirga mashi cikin zuciya da sauri ya k'auda idon sa yana kallon wani gefe yace "Baiwar Allah magana nake maki ko kurma ce ke ban sani ba."
Har yanzu idon ta na kanshi amma ta kasa magana, kusan minti biyu da yaji shiru ya juwo dan yaga ko ta tafi ne, sai yaga tana tsaye, har lokacin shi take kallon hawaye na k'ara bulbulowa ga fuskar, kuma tak'i magana, ganin haka yasa ya k'auda idonsa sabida bai jurar kallon cikin k'wayar idanun ta don da sun had'a ido wani abu yake ji yana masa zirrrrrrrrr tun daga saman kanshi har cikin tafin k'afar sa.
Da yaga bata da niyar yin magana sai ya juya da niyar barin gun da sauri ta rik'o hannu shi ta k'ara fashewa da wani matsanancin kuka mai tab'a zuciya.
Juyowa yayi da k'arfi yana fuskantar ta yace "Dan Allah baiwar Allah ki daina kukan nan wallahi har cikin rai nake jin wanan kukan naki."
Har yanzu dai kallon sa take hannuta rike da na shi kuma tak'i cewa komai, amma ta bar kukan sai hawaye dake anbaliya a fuskar ta kamar ruwan teku.
K'ara kallon fuskar yayi da tagama yin ja yace "Ki daina kukan nan kada kisama kanki ciwon kai, kuma ni ki sakeni na tafiya ta tunda baza kiyi magana sabida na lura ke ba kurma bace kina jin duk abinda nake fad'a." ya fad'i haka tare da fizge hannu sa daga nata.
K'ara sauri riko hannu tayi cikin wata siririyar muyar ta bud'e baki da kyar cikin kuka tace "Dan Allah ka taimaka min aike na akayi da 2000f shine yanzu ina shirin tsaleke titi wasu maza biyu suka zo suka sabce suka gudu gashi yanzu idan naje gida nace an sabce min wallahi dukan mutuwa za'a man ka taimaka min dan kashe ni zatayi, tun d'azu nake nan ba wanda ya min magana bar inyi tunanin za'a taimaka min se kai duk wanda na tsayar nace dan Allah ya taimaka min sai ya fara min wata maganar banza ni kam ba halina bane."
Tunda ta fara maganar ya k'urawa d'an k'aramin bakin ta ido yana kallon yanda take magana sannu sannu cikin nutsuwa da kuma yanda bakin ke motsawa. Jin shiru baice komai ba yasa ta d'ago da kanta ta ga ita yake kallo ko k'yabtawa baiyi da sauri ta saki hannu nasa tana ja da baya d'aga mata hannu yayi alamar ta tsaya sabida bakinsa ya masa nauhi, ja tayi ta tsaya d'an nesa dashi jikin ta na rawa sabida gani take shima d'aya yake da sauran mutanen da tayi ta tsayar wa, wanda a farin ganin shi da tayi bata mishi wannan kallon ba amma yanzu da taga ya tsura mata ido yana kallon ta kawai sai take ganin shima d'aya yake da sauran.
Cikin sark'ewar murya yace "Baiwar Allah dakata ba cutar dake zanyi ba tambayar ki kawai zanyi."
"To.... i...na jin...ka," ta fad'a cikin in ina hawaye na koma zubowa a fukar ta.
Shiru yayi na kusan sakan 5 sannan yace "Miyasa za'a yi miki fad'a idan kince sabce kud'in akayi? Su a gidan basu san.........." Bai k'arasa maganar ba sakamakon katse sa datayi.
Tace "Oh mon dieu (oh my god) idan fad'a ne kawai za'a min da sauki da bazan zauna anan ina asarar hawaye na ba kuma ina neman taimakon jama'a ba, kawai idan zaka taimaka min toh inko ba zaka taimaka min ba? na kama gabana tare da k'ara matso k'walla a idanun ta.
Wata irin ajiyar zuciya ya sauke tare da saka hannun sa cikin aljihun wanda sa ya ciro da kud'in sannan ya k'arasa kusa da ita yace karb'i kije ki siyo abinda aka aike ki siyowa sai ki koma gida, amma dan Allah ki daina tsayawa a hanya kina kuka kina min asarar tsadadin hawayen ki wanan ba girman ki bane kin ga ke ba wata karamar yarinya ba kuma ki daina fitowa ba hijab gaskiya kina barin kowa na kallon surarar jikin ki bazan lamun ta da hakan ban kuma shine yasa duk wanda kika tsayar yake gayami ki magana banza.
Sororo tayi tana kalonshi kamar taga wata sabuwar halita, sake waro ido tayi lokacin da idonta ya sauka kan kud'in dake hanun sa tace "Dan Allah ka rufa man asiri ni fa 2000 nace maka an sabce min ba wai 5000 ba taya zaka d'auki har 5000 ka bani ya zanyi da ita, kuma dakake cewa kan na daina maka asarar hawaye na na za'a kaima cewa kayi hawaye na to taya zan maka asarar su? da kace kada na sake fita ba hijab sabida ba zaka yarda ba to ni shine ban gane ba bawan Allah? Amma zan daina.
Wani irin had'ad'en murmushi ya saki yace "Nima bansan na fad'i hakan ba, amma tunda kince zaki daina ai shikenan kuma yanzu bazaki gane da cewa wanan kukan da kike nine kikewa asarar hawayen ki ba sai nan gaba insha Allah zaki gane, karb'i kud'in ni na wuce.
Saida ta nisa kamin tace "Dan Allah ka rufaman asiri ya zanyi da'ita sedai ka tafi mu tafi na sami canji sai na baka cikon."
D'aga k'afafun sa yayi ya fara tafiya tare da cewa "To mu tafi."
Jerawa sukayi suna tafiya kamar saurayi da budurwa masha Allah couple in su yayi suyi matuk'ar kyau duk idan suka gifta sai an kallesu shi kuwa da ya ga haka sai yai tunanin kowa itace ya ke kallo, tsayawa yayi cak ya daina tafiyar, juyowa tayi tana kollon sa da alama tambaya a bakinta amma kamin tace wani abun shi ya rigata.
Fido da rigar sanyin sa yayi tare da cewa "Karb'i wanan kisa naga kamar kina jin sanyi kuma mutane sai kallon ki suke" dayake lokacin sanyi ne.
Ba musu ta karb'i rigar ta saka ta soma tafiya bin bayan ta yayi da kalo tareda sauke wata kyakyawa ajiyar zuciya sannan ya fara tafiya.
Sun k'washi kusa da rabin awa a hanya suna neman canjin 5000 basu samu ba ja yayi ya tsaya yace kinga ni gaskiya nagaji dayawa kawai kije ni bar miki 5000 d'in juwo tayi ta kalleshi idonta ya shiga sosai cikin nasa wani irin fa'duwar kaba taji tayi sauri k'auda idonta ta tunanin miyasa gaban ta fad'uwa yanzu tayi alhalin tun dazu da take kallon cikin idonshi bata ji hakan ba sai yanzu.
Katse mata tunanin yayi yace "Lafiya kika yi shiru."