Sashe 55
Zamba Cikin Aminci Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Lafiya lau wallahi, ya su momy da yaya AFREED dan yan biyu kuma?"
Yace "Kowa lafiya, ya karatu?"
Tace "Alhamdulilah."
Ali ya ɗan nisa sannan yace "To madala Allah ya taimaka, kina jina Khadijah wani ɗan aiki ne zan sakaki dan Allah in babu damuwa?"
"Lah Hubby dan zaka sakani aiki har sai kace dan Allah mi zaka sakani na ƙasa yi in dai ba saɓon Allah ba ne, ai ko babu komai a tsakanin mu kai ɗin yaya na ne kana da ikon sakani ko wane irin aiki ne kuma nayi ko inaso ko ba naso."
"Hakane hubby amma duk da haka ya kamata na fara tambayar ko kina da dama ko ai sa c'est normal?"
"Hakane kuma to ina jinka miye aikin da zan yi ɗin?"
Saida Ali ya ƙara gyara zaman wayar a kunanan sa sannan yace "Number wata ƴar islamiyyar ku nake so ki samo min a na cema ta AFREEN wata ƴar fara doguwa farin nata dai ba sosai ba wada ta fara karatun a ranar saukar ku."
Fuskar Khadijah da ke ɗauke da murmushi ta koma kamar bata taɓa dariya ba cike da game fuska tace "banga ne taba kuma miye zakayi da number ta, sannan karasa wanda zaka saka wannan aikin sai dan baka ɗauke ni da mahimmanci ba."
Murmushi Ali yayi yana jin daɗi wai saboda shi ne Khadijah ke ta wannan shan maganin alhamdulilah shima an fara kishin sa, daga bisani sai yace "Kwantar da hankali hubby ki yarda dani babu abinda zanyi da number ta ina da ke kuma mi zai kaini kula wata kawai inada buƙatar number ne daga baya zan sanar maki dalilin neman number nata kawai ki taimaka ki nema man idan kikayi hankan kamar kin ceto rayuwa ne."
"To shikenan hubby na gane ta ai dama da gangan nace ban gane ta ba zan nemo number ta insha Allahu sabida ƙanwata ƙawata tace."
"Masha Allah kinga abin ya zo da sauƙi, to sai naji ki gaida su tanti."
"Za su ji insha Allah." Daga nan Ali ya kashe kiran sannan Khadijah ta ajiye wayar ta na murmushi ta nufi wardrobe dan fitar da kayan da zata saka."
Bayan kwana biyun da Ali ya yi kiran Khadijah don ta nema masa number AFREEN, sai gata ran cikon kwana na uku ta kira shi ringing biyu ya ɗaga tare da sallama yace "Hubby barka ki da warhaka da kin yuni lafiya?"
Tace "Lafiya lau ina yuni?"
Yace "alhamdulilah ya gida?"
"Gida lafiyar sa lau."
"To madala ina aikin da na saka ki komai ya daidaita ko kuwa?"
Tace "Komai normal hubby aiki na ƙarasa kiran dana maka kenan na baka résultat ɗin aikin."
Ali ya waro ido kamar tana ganin shi sannan yace "Da sauri haka hubby injin dai baki ce wani ke buƙatar number ba."
Tace "Haba hubby kamar banda hankali, kamar kuma ba mace ba, kawai sai na fito fili na tunawa kai na asiri, to da nayi haka ai da yanzu ban samo lamba ba dan ita da kanta Zeinab ƙanwar ta ɗin bata san na ɗauko number a wayar ta ba."
Ali yace "To ya akayi ki ɗauke ta ba tare da ta saniba."
Murmushi Khadijah tayi sannan tace "Ƙarɓa wayar ta nayi nace ƙawata bari naka sunan da kika saka min a matsayin na ƙawar ki wace baki da kamar ta a islamiyyar nan, sai Zeinab ɗin tace to shikenan bari na baki ƙawata a tunanin ki mi zan saka, kawai sai ta miƙon man wayar na shiga nayi ta duba numbobin mutane banga inda ta saka sunan AFREEN ba, amma sanin yanda ta ke ƙaunar AFREEN ɗin yasa wani suna da nagani ta saka ma deuxième mère (my second Mom) ya ɗaukar man da hankali sosai sai natsa akan sa na tambayeta nace wacce kuma wada kike ji sosai ki ka saka ma wannan sunan, tana murmushi tace man anty AFREEN ce daga nan nayi hamdala sannan nace a lallai yanzu nayar kuna jin juna sosai, tace sosai kuwa ban san ya zan kwatanta yanda nake son ta ba wallahi ni banda kamar ta duk cikin yaye na, ba tare da ta lura ba na hardace number a kaina, sai nayi mata sai anjima nayi tafiya ta harda tambayar naga sunan da ta sakamin ɗin nace mata eh, ina gusawa daga gun ta na saka number a phone ɗin na na saving ɗin ya dan kar na manta."
Ali ya saki murmushi yace "Woow very nice shiyasa nake alfahari dake hubby gaskiya kinyi taimako, ban zan tamɓa mantawa da wannan ba yanzu ki turoman number ta whatsapp yanzu yanzu ina jiranki nagode sosai hubby." Ba tare da ya jiran jin abinda zata ce ba ya katse kiran.
Ba musu Khadijah ta tura masa number daidai ya kuna data saƙon number ya shigo, buɗe saƙon yayi tare yi mata reply kamar haka "Nagode sosai Allah saka da alkairi kinyi ƙoƙarin sosai." sai ya tura sannan ya sake tura mata sticker da aka rubuta i love you sai kawai ya kashe data ya nufi toillet danyin wanka saida ya ɗauki kusan min ashirin kamin yake fito ya shirya cikin wasu haɗaɗun ƙananun kaya masu mugun kyau kuma su ka zauna a jikin sa tsaf kamar dan shi a kayi kayan, sannan ya feshe jikin da daɗaɗan turaruka masu mugun kamshi a take ya fara zuba uban kamshi kamar yayi wanka da tekun turare sannan ya fito daga nashi ɗakin yana ta sakin wani haɗaɗen murmushi kamar wanda akayiwa albishirin shiga aljanna, don yau jin sa yake a cikin wani irin farin cikin mara musultuwa, saboda gani yake ya samo maganin ciwon ɗan uwansa zai warke har abada.
Ɗakin AFREED Ali ya nufa kai tsaye ya buɗe ƙofa ya shiga tare da yin wata ƴar siririyar sallama AFREED dake zaune saman wata haɗaɗiyar kujera dake ɗakin kansa a duƙe da ya dafe a hannuwan sa ya rasa abinda ke masa ɗadi saboda tunanin AFREEN ya amsa masa sallamar ba tare da ya ɗago ba.
Kusan minti biyu Ali ya yi a tsaye ya nazarin ɗan uwan na sa da bisani sai ya ƙarasa kusa AFREED ɗin ya zauna tare da dafa shi, sai a lokacin ya ɗago kansa ya sauke idonsa da suka yi ja kamar gauta cikin na Ali, da sauri Ali ya janye hannunsa da ke saman kafaɗar AFREED tare da ɗan gusawa kaɗan daga kusa dashi a ɗan tsora ce yace "Broh lafiyar ka mi ya sami idon ka kuma komi yake damun ka yanzun, ku ma dan Allah faɗa man kada kasa hankali na tashi."
Ɗan riƙo hannun sa AFREED ya yi sannan ya koma kallon sa yace "Wallahi broh ina cikin matsala nakasa jure rashin yarinya nan, yanda nake ji a cikin zuciyata da yanda son ta ke bin duk sasan jikina yana ratsa jinin jiki na da ilahirin jikina baki ɗaya ya hanani sukuni, gani nake inda banje Maraɗi na nemo ta ba na faɗa mata abinda ke raina zan iya rasa rai na wallahi." kawai sai ga hawaye na gudu a saman fuskar AFREED.
Da mugun mamaki Ali ke kallon AFREED da wani irin tausayin sa da ya ɗarsu a zuciyarsa wai yau AFREED ne ke zubar da kwala sabida wata ɗiya mace, macen wacce bata masan yanayi ba, shida yasan da ko kallon mace baiyi bare har yace yana son ta har soyayyar ta ta kaishi ga haka Allah kenan mai yanda yaso bai taɓa tunanin haka ga AFREED ba.
Bai ƙarasa mamakin saba yaji AFREED na cewa "Ka taimaka min ɗan uwa dan gaskiya nakasa jurewa har ma na yanke shawara zuwa Maraɗi gobe Insha Allahu dan nemo farin cikin rai na."
Da sauri Ali yace "Ai ba se takai ga haka ba ka kwantar da hankalin ka insha Allahu AFREEN taka ce, kai ko yanzu kake so masa zaka iya jin muryar ta dan kuwa har na riga da na nemo maka number ta, saboda ni ma ba jure ganin ka a cikin wannan halin wallahi yanzu komai zai daidaita Insha Allahu."
Wani irin farin cikin ne ya mamaye zuciyar AFREED da har bai san lokacin da ya kama Ali ya rungume ba, ya sakin murmushi tare da hawayen farin ciki yace "ba nida kamar ka ɗan uwa ba zani taɓa samun farin ciki mai ɗaurewa ba in babu kai, ni ban masan wane irin godiya zan maka ba, mi ka keso nayi maka da zai sanya ka farin ciki ka gama min komai a rayuwa Allah ya biyaka da mafificin alkairi ya sada ka da aljannar fidaoussi.
Ali yace "Ni sakeni dan Allah miye na wani yi min godiya ne, ka nagani ina iya farin ciki ne idan kai baka tare da shi, ni kawai ka ɗauki number ta na baka ka samu ka kirata tun kan lokaci ya ƙure maka, ka san ƴan mata ba su zama babu saurayi to idan ka bari wani ya riga ka shiga zuciyata, to fa sunan ka sorry, abinda zaka min naji daɗi kuwa shine kayi gaggawar saka ma yarinyar nan soyayyar ka mai tsananin kamar yanda itama ta yi ƙoƙarin wajen saka tata a zuciyarka, koda kuwa ta nada wanda take so inason kayi ƙoƙarin mayar da soyayyar ta sa a kanka har kazo ka ci nasarar aurenta, idan kayi to ni ka gama yi man komai wallah."
"To shikenan Ali naji saka man number a nan," AFREED ya faɗa ya na mai miƙa masa waya sa cike da farin ciki.
Karɓa Ali yayi ya saka number sannan ya tashi ya fice ya na mai cewa nan da kwana biyu inji dadaɗan labari."
Ali na fita AFREED ya saki wani haɗaɗen murmushi tare da mai da gaba gabas ya yiwa Ubangiji sujada ta nuna godiyar sa a garesa, sannan ya miƙe ya nufi toillet yana farin ciki kamar ba shine ya gama hawaye yanzu ba."
Yace "Kowa lafiya, ya karatu?"
Tace "Alhamdulilah."
Ali ya ɗan nisa sannan yace "To madala Allah ya taimaka, kina jina Khadijah wani ɗan aiki ne zan sakaki dan Allah in babu damuwa?"
"Lah Hubby dan zaka sakani aiki har sai kace dan Allah mi zaka sakani na ƙasa yi in dai ba saɓon Allah ba ne, ai ko babu komai a tsakanin mu kai ɗin yaya na ne kana da ikon sakani ko wane irin aiki ne kuma nayi ko inaso ko ba naso."
"Hakane hubby amma duk da haka ya kamata na fara tambayar ko kina da dama ko ai sa c'est normal?"
"Hakane kuma to ina jinka miye aikin da zan yi ɗin?"
Saida Ali ya ƙara gyara zaman wayar a kunanan sa sannan yace "Number wata ƴar islamiyyar ku nake so ki samo min a na cema ta AFREEN wata ƴar fara doguwa farin nata dai ba sosai ba wada ta fara karatun a ranar saukar ku."
Fuskar Khadijah da ke ɗauke da murmushi ta koma kamar bata taɓa dariya ba cike da game fuska tace "banga ne taba kuma miye zakayi da number ta, sannan karasa wanda zaka saka wannan aikin sai dan baka ɗauke ni da mahimmanci ba."
Murmushi Ali yayi yana jin daɗi wai saboda shi ne Khadijah ke ta wannan shan maganin alhamdulilah shima an fara kishin sa, daga bisani sai yace "Kwantar da hankali hubby ki yarda dani babu abinda zanyi da number ta ina da ke kuma mi zai kaini kula wata kawai inada buƙatar number ne daga baya zan sanar maki dalilin neman number nata kawai ki taimaka ki nema man idan kikayi hankan kamar kin ceto rayuwa ne."
"To shikenan hubby na gane ta ai dama da gangan nace ban gane ta ba zan nemo number ta insha Allahu sabida ƙanwata ƙawata tace."
"Masha Allah kinga abin ya zo da sauƙi, to sai naji ki gaida su tanti."
"Za su ji insha Allah." Daga nan Ali ya kashe kiran sannan Khadijah ta ajiye wayar ta na murmushi ta nufi wardrobe dan fitar da kayan da zata saka."
Bayan kwana biyun da Ali ya yi kiran Khadijah don ta nema masa number AFREEN, sai gata ran cikon kwana na uku ta kira shi ringing biyu ya ɗaga tare da sallama yace "Hubby barka ki da warhaka da kin yuni lafiya?"
Tace "Lafiya lau ina yuni?"
Yace "alhamdulilah ya gida?"
"Gida lafiyar sa lau."
"To madala ina aikin da na saka ki komai ya daidaita ko kuwa?"
Tace "Komai normal hubby aiki na ƙarasa kiran dana maka kenan na baka résultat ɗin aikin."
Ali ya waro ido kamar tana ganin shi sannan yace "Da sauri haka hubby injin dai baki ce wani ke buƙatar number ba."
Tace "Haba hubby kamar banda hankali, kamar kuma ba mace ba, kawai sai na fito fili na tunawa kai na asiri, to da nayi haka ai da yanzu ban samo lamba ba dan ita da kanta Zeinab ƙanwar ta ɗin bata san na ɗauko number a wayar ta ba."
Ali yace "To ya akayi ki ɗauke ta ba tare da ta saniba."
Murmushi Khadijah tayi sannan tace "Ƙarɓa wayar ta nayi nace ƙawata bari naka sunan da kika saka min a matsayin na ƙawar ki wace baki da kamar ta a islamiyyar nan, sai Zeinab ɗin tace to shikenan bari na baki ƙawata a tunanin ki mi zan saka, kawai sai ta miƙon man wayar na shiga nayi ta duba numbobin mutane banga inda ta saka sunan AFREEN ba, amma sanin yanda ta ke ƙaunar AFREEN ɗin yasa wani suna da nagani ta saka ma deuxième mère (my second Mom) ya ɗaukar man da hankali sosai sai natsa akan sa na tambayeta nace wacce kuma wada kike ji sosai ki ka saka ma wannan sunan, tana murmushi tace man anty AFREEN ce daga nan nayi hamdala sannan nace a lallai yanzu nayar kuna jin juna sosai, tace sosai kuwa ban san ya zan kwatanta yanda nake son ta ba wallahi ni banda kamar ta duk cikin yaye na, ba tare da ta lura ba na hardace number a kaina, sai nayi mata sai anjima nayi tafiya ta harda tambayar naga sunan da ta sakamin ɗin nace mata eh, ina gusawa daga gun ta na saka number a phone ɗin na na saving ɗin ya dan kar na manta."
Ali ya saki murmushi yace "Woow very nice shiyasa nake alfahari dake hubby gaskiya kinyi taimako, ban zan tamɓa mantawa da wannan ba yanzu ki turoman number ta whatsapp yanzu yanzu ina jiranki nagode sosai hubby." Ba tare da ya jiran jin abinda zata ce ba ya katse kiran.
Ba musu Khadijah ta tura masa number daidai ya kuna data saƙon number ya shigo, buɗe saƙon yayi tare yi mata reply kamar haka "Nagode sosai Allah saka da alkairi kinyi ƙoƙarin sosai." sai ya tura sannan ya sake tura mata sticker da aka rubuta i love you sai kawai ya kashe data ya nufi toillet danyin wanka saida ya ɗauki kusan min ashirin kamin yake fito ya shirya cikin wasu haɗaɗun ƙananun kaya masu mugun kyau kuma su ka zauna a jikin sa tsaf kamar dan shi a kayi kayan, sannan ya feshe jikin da daɗaɗan turaruka masu mugun kamshi a take ya fara zuba uban kamshi kamar yayi wanka da tekun turare sannan ya fito daga nashi ɗakin yana ta sakin wani haɗaɗen murmushi kamar wanda akayiwa albishirin shiga aljanna, don yau jin sa yake a cikin wani irin farin cikin mara musultuwa, saboda gani yake ya samo maganin ciwon ɗan uwansa zai warke har abada.
Ɗakin AFREED Ali ya nufa kai tsaye ya buɗe ƙofa ya shiga tare da yin wata ƴar siririyar sallama AFREED dake zaune saman wata haɗaɗiyar kujera dake ɗakin kansa a duƙe da ya dafe a hannuwan sa ya rasa abinda ke masa ɗadi saboda tunanin AFREEN ya amsa masa sallamar ba tare da ya ɗago ba.
Kusan minti biyu Ali ya yi a tsaye ya nazarin ɗan uwan na sa da bisani sai ya ƙarasa kusa AFREED ɗin ya zauna tare da dafa shi, sai a lokacin ya ɗago kansa ya sauke idonsa da suka yi ja kamar gauta cikin na Ali, da sauri Ali ya janye hannunsa da ke saman kafaɗar AFREED tare da ɗan gusawa kaɗan daga kusa dashi a ɗan tsora ce yace "Broh lafiyar ka mi ya sami idon ka kuma komi yake damun ka yanzun, ku ma dan Allah faɗa man kada kasa hankali na tashi."
Ɗan riƙo hannun sa AFREED ya yi sannan ya koma kallon sa yace "Wallahi broh ina cikin matsala nakasa jure rashin yarinya nan, yanda nake ji a cikin zuciyata da yanda son ta ke bin duk sasan jikina yana ratsa jinin jiki na da ilahirin jikina baki ɗaya ya hanani sukuni, gani nake inda banje Maraɗi na nemo ta ba na faɗa mata abinda ke raina zan iya rasa rai na wallahi." kawai sai ga hawaye na gudu a saman fuskar AFREED.
Da mugun mamaki Ali ke kallon AFREED da wani irin tausayin sa da ya ɗarsu a zuciyarsa wai yau AFREED ne ke zubar da kwala sabida wata ɗiya mace, macen wacce bata masan yanayi ba, shida yasan da ko kallon mace baiyi bare har yace yana son ta har soyayyar ta ta kaishi ga haka Allah kenan mai yanda yaso bai taɓa tunanin haka ga AFREED ba.
Bai ƙarasa mamakin saba yaji AFREED na cewa "Ka taimaka min ɗan uwa dan gaskiya nakasa jurewa har ma na yanke shawara zuwa Maraɗi gobe Insha Allahu dan nemo farin cikin rai na."
Da sauri Ali yace "Ai ba se takai ga haka ba ka kwantar da hankalin ka insha Allahu AFREEN taka ce, kai ko yanzu kake so masa zaka iya jin muryar ta dan kuwa har na riga da na nemo maka number ta, saboda ni ma ba jure ganin ka a cikin wannan halin wallahi yanzu komai zai daidaita Insha Allahu."
Wani irin farin cikin ne ya mamaye zuciyar AFREED da har bai san lokacin da ya kama Ali ya rungume ba, ya sakin murmushi tare da hawayen farin ciki yace "ba nida kamar ka ɗan uwa ba zani taɓa samun farin ciki mai ɗaurewa ba in babu kai, ni ban masan wane irin godiya zan maka ba, mi ka keso nayi maka da zai sanya ka farin ciki ka gama min komai a rayuwa Allah ya biyaka da mafificin alkairi ya sada ka da aljannar fidaoussi.
Ali yace "Ni sakeni dan Allah miye na wani yi min godiya ne, ka nagani ina iya farin ciki ne idan kai baka tare da shi, ni kawai ka ɗauki number ta na baka ka samu ka kirata tun kan lokaci ya ƙure maka, ka san ƴan mata ba su zama babu saurayi to idan ka bari wani ya riga ka shiga zuciyata, to fa sunan ka sorry, abinda zaka min naji daɗi kuwa shine kayi gaggawar saka ma yarinyar nan soyayyar ka mai tsananin kamar yanda itama ta yi ƙoƙarin wajen saka tata a zuciyarka, koda kuwa ta nada wanda take so inason kayi ƙoƙarin mayar da soyayyar ta sa a kanka har kazo ka ci nasarar aurenta, idan kayi to ni ka gama yi man komai wallah."
"To shikenan Ali naji saka man number a nan," AFREED ya faɗa ya na mai miƙa masa waya sa cike da farin ciki.
Karɓa Ali yayi ya saka number sannan ya tashi ya fice ya na mai cewa nan da kwana biyu inji dadaɗan labari."
Ali na fita AFREED ya saki wani haɗaɗen murmushi tare da mai da gaba gabas ya yiwa Ubangiji sujada ta nuna godiyar sa a garesa, sannan ya miƙe ya nufi toillet yana farin ciki kamar ba shine ya gama hawaye yanzu ba."