Sashe 23
Zamba Cikin Aminci Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da amin ya amsa sannan ya tashi ya fice daga falon ya nufi ɓangaren su, yana shiga direct ɗakin AFREED ya wuce, tardo sa yayi kwace idonsa a lumshe kamar mai bacci, juyawa yayi ya kalli abincin da aka kawo masa wanda ko kallon sa baiyi ba bare ma ace ya ci sa, da sannu sannu ya nufi bakin gadon ya zauna sannan yace "Ɗan uwana AFREED tashi kaci abincin mana ya za'a kawo maka abincin tun ɗazu kaƙi ci tashi dan Allah."
Shiru kakeji AFREED bai ko motsa ba bare ya nuna ya jisa har ayi maganar zai amsa masa, Ali ya koma cewa "AFREED ka tashi man kada abincin yayi sanhi kuma ka kasa ci," nan ma shiru AFREED bai motsa ba, "Haba ɗan uwana mi yayi zafi haka?" Har yanzu AFREED bai motsa ba bare ayi tunanin zai tashi daga kwanciyar dayake.
Shiru Ali yayi na tsawon minti biyu yana kallon AFREED sannan ya kuma cewa "Nifa nasan ba bacci kake ba, amma tunda kaƙi tashi bari na kira momy na faɗa mata baka ci komai ba dama tana can cikin damuwa sabida ka taso ka ta howarka baka tsaya kaci abincin ba shine ta aikoni nazo nagani idan baka ci ba naje na faɗa mata."
AFREED najin haka yayi sauri ya tashi zaune tare da ƙoƙarin saukowa daka saman gadon Ali yayi saurin riƙo sa yace "Ina kuma zakaje?"
Wani mugun kallo AFREED yayiwa Ali sannan yace "Kai dan Allah cikani ina fah zanje da ya wuce gun momy naga halin data ke ciki."
Mtsss Ali yaja wani ɗan ƙaramin tsaki sannan yace "Dan Allah dakata malam ka damu da halin da zata shiga ne ka kama hanya kayi tafiyar ka kamin taje ɗakin su Fariya ta dawo sannan kuma kaje gunta da alamu damuwa a fuskar idan baka don sata cikin damuwa miyasa ka aikata haka, abu guda ne zaka yi idan kana son kaga damuwar ta ta gushe shine ka karɓi abincin nan ka ciye shi sannan kasamu kayi sallah idan ka gama sai kaje gunta cikin sakin fuska a take za kaga farin cikin ta mara musultuwa amma ba ka wani tashi da sauri haka ba wai kai ga meson gani halin da take ciki, idan kaje haka ba sedai ka ƙara mata damuwar ba ɗan raini hankali kawai."
Saƙe AFREED yayi na wajan second 3 yana kallon Ali daga bisani dai ya sauke ajiyar zuciya mai nauyi ba tare da yace wani abu ba ya karɓi abincin daga hannun Ali ya fara ci har sai da yaci fiye da rabin assiette (plet) sannan ya ajiye, yana ƙoƙarin tashi daga bisa gadon Ali ya riƙo sa yace "Yo ina kuma zaka kaida baka ƙarasa cin abincin ba?"
Da sauri AFREED ya fizge hannun sa yana cewa wallahi Ali ka fita haraka kazo ka sakani cin abincin nan naci ba dan maso sannan kuma so kake sai na cinye wannan uban abincin to wane irin ciki ne dani da zan iya cinye sa? kuma wallahi baka isaba don na tabata ko kai dake cin abincin sosai ba iya cinye wannan abincin zaka yi ba amma ni kake son kaga na cinye shi a cikin wane cikin kake son gani na saka shi? to wallahi duk fitinar ka yau sai ka barni," mtsss yaja tsaki tare da shigewa douche da sauri ya banko ƙofar toilette ɗin da ƙarfi.
Murmushi Ali ya saki tare da cewa "Ɗan uwana, abokina, kuma uban gidan AFREED Allah tsare min kai ya baka mata ta gari wada zata iya jure wannan halin naka sannan kuma ta zama sillar gyara maka wannan bahagon halin naka amin tunda dai kaci abincin ai shikenan dama da gaganne nace sai ka cinye shi."
Daga na shi ma ya tashi ya fita daga ɗakin AFREED ya nufi nasa ɗakin.
Shikuwa AFREED dake cikin douche yana jin fitar Ali ya fito a cikin zuciyarsa yana cewa anyi mutum sai shegin surutu da fitina da son takurawa jama'a, mtsss yaja ɗan ƙaramin tsaki tare da shimfiɗa darduma ya tada sallah.
*WANENE AFREED*
AFREED Sumana Gissa shine cikakken sunan AFREED wato ɗan ga Alhaji Sumana Gissa wanda yake cikakken bazabarme ne ɗan asalin garin Dosso kuma ingénieur (injiniya) ne aiki ne ya maido sa Niamey da zama, sai mahaifiyar AFREED Hajiya Falmata Ita kuwa cikakkiyar babarbara ce gaba da baya ƴar asalin garin Diffa, su biyu iyayen su suka haifa ita ƙanwarta Kaltum sun haɗu da Alhaji Sumana ne wajan walimar taron buɗe wata ma'aikata gina-gine a garin diffa ita kuwa tatafi wucewa ta gaban ma'aikatar ta dawo Ga aikin da aka mata yana ganinta ya ruɗe sabida Allah yayi mata kyau ga wani uban kamshi dake tashi a jikin ta, kun san barebari game da kamshi babu kamar su sedai kuma ba fara ce sosai ba haka dai har ya samu ya tsayar da ita ta yi masa kwatancan gidan su ida yaje ya sami mahaifin ta da maganar, da mahaifin nata yayi bincike a kansa ya samu kyakyawa shaida a tatare da shi, ya bashi auren Falmata cikin ƙanƙanan lokacin akayi komi da komi haka a ɗaura auren Falmata da Alhaji Sumana Gissa cikin aminci, suka tare a babban gidansu dake cikin garin Niamey wata uku da auren Falmata akayi na ƙanwarta Kaltum wani bafilatani mai rufi asiri a garin Tillaberi amma ba ɗan asalin garin bane neman kuɗi ya kawo sa Niger shi ɗin ɗan asalin garin Senegal ne.
Bayan shekara guda da auren Falmata da Alhaji Sumana Allah ya basu ƙaruwar ɗan namiji murna wajan wannan famille (family) ba'a magana kowa ka gani cikin farin ciki yake yaro mulmulmul dashi kyakkyawan gaske sai farin jini kowa ya gansa sai yaji kamar a basa shi kuma duk wanda ya ɗauka ba yason ya ajiye har saida jikinsa yayi ciwo kamin suna, ranar suna yaro yaci sunan AFREED, bikin sunan ya ƙawatu dan anci ansha sai dai son barka.
AFREED na da wata shida da haihuwa Kaltum ƙanwar Hajiya Falmata Ita ma ta haihi ɗan ta fari kal mai mugun kama da AFREED tunda yazo duniya mahaifinsa yayi masa huɗuba da Ali wato sunan mahaifinsa su Hajiya Falmata sedai tunda Kaltum ta haihu jini yaƙi tsayawa, likitoci suyi iya bakin ƙoƙarin su wajan ganin sun shawo kan matsalar amma abin ya ci tura, kwana biyu da haihuwar tace ga garinku aikuwa tashi hankali gun Hajiya Falmata ba'a magana taci kuka taci kuka har ta godewa Allah har yakai kukan baya fitowa saida ayita jin tana sauke ajiyar zuciya, sosai takasa hakura da rasuwar ƙanwarta ta kullum cikin kuka take ganin haka yasa Alhaji Sumana ya roƙi mahaifin Ali da ya taimaka ya bawa matarsa yaron sai taci gaba da shayar dashi tunda ita cikin jegon take, kuma ganin ɗan ƴar uwatata zaisa ya dinga ɗebe bata kewa haka kuwa akayi Mahaifin Ali yace ya bata shi halak malak tasa ma kanta cewa itace ta haifesa sannan ya ƙara da cewa shi yanzu ƙasar su zai komawa dama sabida Kaltum yake zaune a Niger amma yanzu komawa zai yi tunda ya gama abinda yake a Niger abinda ya samu Allah sa masa albarka, kuma yace su taimaka idan Ali ya girma su bashi labarin shin duk dacewa zai dinga zuwa ganisa lokacin zuwa lokaci amma daya ke bai san halin rayuwa ba ko yanada rai zai girma kokuwa Allah dai masani.
Ai kuwa kuka sai ya koma dariya gun Hajiya Falmata don ba ƙaramin farin ciki tayi ba daji an bata Ali har abada, ba ma ta iya musulta farin cikin da take cikin don ji take kamar ƴar uwata in ce gaba-ɗaya take raino, haka dai Hajiya Falmata ta haɗa ɗiyanta biyu gaba ɗaya ta na shayar dasu cikin tsantsan so da gata dan ba ƙaramin ji dasu take ba shima Alhaji Sumana ba'a barsa a baya ba sabida idai yana gari to a kowa ne lokacin suna tare dashi babu wani banbanci da iyayen AFREED ke nunawa ga Ali duk ɗaya suka ɗokesu, har ma sufi yiwa Ali Abu basu ma AFREED ba, Ali dai kam baida maraicin uwa da uba don Hajiya Falmata da Alhaji Sumana ba ƙaramin sonsa suke ba.
Shikuwa mahaifin Ali ya riga da da ya koma ƙasar su ya bar amanar Ali a hannun iyayen AFREED.
AFREED da Ali na da shekara uku uku aka saka su école coranique (islamiyya) da jardin d'enfants (nursery school) Mai tsadan gaske Masha Allah duk da yarinta su haka bai hana su rike abinda ake koyar dasu ba kuma idan sun zo gida Hajiya Falmata ta ƙara koyawar dasu su, AFREED sun tashi cikin gata sosai amma hakan bai hana iyayensu basu tarbiyya ba Hajiya Falmata da Alhaji Sumana suna iya ƙoƙarin su wajan ganin sun basu cikakkiyar tarbiyya, AFREED ya tashi miskili mara son magana bai ƙaunar zama inda ake hayaniya da yawan surutu sedai halinsa yasha banban da na Ali wanda shi kuwa ma'abucin surutu ne da barkwanci duk da wannan halin na surutu na Ali da AFREED bai so amma ba ƙaramin ƙaunar junansu suke ba ko kaɗan basa son ganin junansu cikin damuwa a tare suke komai nasu, ko Hajiya Falmata da Alhaji Sumana basu san tsakanin su ba.
Kwanci tashi babu wuya a wajan Ubangiji su AFREED har sunyi shekara bakwai bakwai sosai sukayi wayo masha Allah idan ka gansu zakayi tunanin sufi shekarun dake garesu sabida tsananin wayo da Allah ya masu. Ita kuwa Hajiya Falmata tunda ta haifi AFREED Ko ɓatan wata bata taɓa yi ba bare ayi batun samun cikin shiru shiru kakeji har saida su AFREED su kayi shekara goma sannan Allah ya ƙara bata haihuwa wanda har sun fida rai da samun ta idan ta haifi ƴan biyu duka mata ranar suna yara aka raɗa masu sunan Fariya da Farisa murna gun AFREED da Ali ba'a magana kullum suna tare dasu an samu ƙanai duk in sun taso daga makaranta suna tare da su bacci kaɗai ke rabasu da ƙannansu.
Shiru kakeji AFREED bai ko motsa ba bare ya nuna ya jisa har ayi maganar zai amsa masa, Ali ya koma cewa "AFREED ka tashi man kada abincin yayi sanhi kuma ka kasa ci," nan ma shiru AFREED bai motsa ba, "Haba ɗan uwana mi yayi zafi haka?" Har yanzu AFREED bai motsa ba bare ayi tunanin zai tashi daga kwanciyar dayake.
Shiru Ali yayi na tsawon minti biyu yana kallon AFREED sannan ya kuma cewa "Nifa nasan ba bacci kake ba, amma tunda kaƙi tashi bari na kira momy na faɗa mata baka ci komai ba dama tana can cikin damuwa sabida ka taso ka ta howarka baka tsaya kaci abincin ba shine ta aikoni nazo nagani idan baka ci ba naje na faɗa mata."
AFREED najin haka yayi sauri ya tashi zaune tare da ƙoƙarin saukowa daka saman gadon Ali yayi saurin riƙo sa yace "Ina kuma zakaje?"
Wani mugun kallo AFREED yayiwa Ali sannan yace "Kai dan Allah cikani ina fah zanje da ya wuce gun momy naga halin data ke ciki."
Mtsss Ali yaja wani ɗan ƙaramin tsaki sannan yace "Dan Allah dakata malam ka damu da halin da zata shiga ne ka kama hanya kayi tafiyar ka kamin taje ɗakin su Fariya ta dawo sannan kuma kaje gunta da alamu damuwa a fuskar idan baka don sata cikin damuwa miyasa ka aikata haka, abu guda ne zaka yi idan kana son kaga damuwar ta ta gushe shine ka karɓi abincin nan ka ciye shi sannan kasamu kayi sallah idan ka gama sai kaje gunta cikin sakin fuska a take za kaga farin cikin ta mara musultuwa amma ba ka wani tashi da sauri haka ba wai kai ga meson gani halin da take ciki, idan kaje haka ba sedai ka ƙara mata damuwar ba ɗan raini hankali kawai."
Saƙe AFREED yayi na wajan second 3 yana kallon Ali daga bisani dai ya sauke ajiyar zuciya mai nauyi ba tare da yace wani abu ba ya karɓi abincin daga hannun Ali ya fara ci har sai da yaci fiye da rabin assiette (plet) sannan ya ajiye, yana ƙoƙarin tashi daga bisa gadon Ali ya riƙo sa yace "Yo ina kuma zaka kaida baka ƙarasa cin abincin ba?"
Da sauri AFREED ya fizge hannun sa yana cewa wallahi Ali ka fita haraka kazo ka sakani cin abincin nan naci ba dan maso sannan kuma so kake sai na cinye wannan uban abincin to wane irin ciki ne dani da zan iya cinye sa? kuma wallahi baka isaba don na tabata ko kai dake cin abincin sosai ba iya cinye wannan abincin zaka yi ba amma ni kake son kaga na cinye shi a cikin wane cikin kake son gani na saka shi? to wallahi duk fitinar ka yau sai ka barni," mtsss yaja tsaki tare da shigewa douche da sauri ya banko ƙofar toilette ɗin da ƙarfi.
Murmushi Ali ya saki tare da cewa "Ɗan uwana, abokina, kuma uban gidan AFREED Allah tsare min kai ya baka mata ta gari wada zata iya jure wannan halin naka sannan kuma ta zama sillar gyara maka wannan bahagon halin naka amin tunda dai kaci abincin ai shikenan dama da gaganne nace sai ka cinye shi."
Daga na shi ma ya tashi ya fita daga ɗakin AFREED ya nufi nasa ɗakin.
Shikuwa AFREED dake cikin douche yana jin fitar Ali ya fito a cikin zuciyarsa yana cewa anyi mutum sai shegin surutu da fitina da son takurawa jama'a, mtsss yaja ɗan ƙaramin tsaki tare da shimfiɗa darduma ya tada sallah.
*WANENE AFREED*
AFREED Sumana Gissa shine cikakken sunan AFREED wato ɗan ga Alhaji Sumana Gissa wanda yake cikakken bazabarme ne ɗan asalin garin Dosso kuma ingénieur (injiniya) ne aiki ne ya maido sa Niamey da zama, sai mahaifiyar AFREED Hajiya Falmata Ita kuwa cikakkiyar babarbara ce gaba da baya ƴar asalin garin Diffa, su biyu iyayen su suka haifa ita ƙanwarta Kaltum sun haɗu da Alhaji Sumana ne wajan walimar taron buɗe wata ma'aikata gina-gine a garin diffa ita kuwa tatafi wucewa ta gaban ma'aikatar ta dawo Ga aikin da aka mata yana ganinta ya ruɗe sabida Allah yayi mata kyau ga wani uban kamshi dake tashi a jikin ta, kun san barebari game da kamshi babu kamar su sedai kuma ba fara ce sosai ba haka dai har ya samu ya tsayar da ita ta yi masa kwatancan gidan su ida yaje ya sami mahaifin ta da maganar, da mahaifin nata yayi bincike a kansa ya samu kyakyawa shaida a tatare da shi, ya bashi auren Falmata cikin ƙanƙanan lokacin akayi komi da komi haka a ɗaura auren Falmata da Alhaji Sumana Gissa cikin aminci, suka tare a babban gidansu dake cikin garin Niamey wata uku da auren Falmata akayi na ƙanwarta Kaltum wani bafilatani mai rufi asiri a garin Tillaberi amma ba ɗan asalin garin bane neman kuɗi ya kawo sa Niger shi ɗin ɗan asalin garin Senegal ne.
Bayan shekara guda da auren Falmata da Alhaji Sumana Allah ya basu ƙaruwar ɗan namiji murna wajan wannan famille (family) ba'a magana kowa ka gani cikin farin ciki yake yaro mulmulmul dashi kyakkyawan gaske sai farin jini kowa ya gansa sai yaji kamar a basa shi kuma duk wanda ya ɗauka ba yason ya ajiye har saida jikinsa yayi ciwo kamin suna, ranar suna yaro yaci sunan AFREED, bikin sunan ya ƙawatu dan anci ansha sai dai son barka.
AFREED na da wata shida da haihuwa Kaltum ƙanwar Hajiya Falmata Ita ma ta haihi ɗan ta fari kal mai mugun kama da AFREED tunda yazo duniya mahaifinsa yayi masa huɗuba da Ali wato sunan mahaifinsa su Hajiya Falmata sedai tunda Kaltum ta haihu jini yaƙi tsayawa, likitoci suyi iya bakin ƙoƙarin su wajan ganin sun shawo kan matsalar amma abin ya ci tura, kwana biyu da haihuwar tace ga garinku aikuwa tashi hankali gun Hajiya Falmata ba'a magana taci kuka taci kuka har ta godewa Allah har yakai kukan baya fitowa saida ayita jin tana sauke ajiyar zuciya, sosai takasa hakura da rasuwar ƙanwarta ta kullum cikin kuka take ganin haka yasa Alhaji Sumana ya roƙi mahaifin Ali da ya taimaka ya bawa matarsa yaron sai taci gaba da shayar dashi tunda ita cikin jegon take, kuma ganin ɗan ƴar uwatata zaisa ya dinga ɗebe bata kewa haka kuwa akayi Mahaifin Ali yace ya bata shi halak malak tasa ma kanta cewa itace ta haifesa sannan ya ƙara da cewa shi yanzu ƙasar su zai komawa dama sabida Kaltum yake zaune a Niger amma yanzu komawa zai yi tunda ya gama abinda yake a Niger abinda ya samu Allah sa masa albarka, kuma yace su taimaka idan Ali ya girma su bashi labarin shin duk dacewa zai dinga zuwa ganisa lokacin zuwa lokaci amma daya ke bai san halin rayuwa ba ko yanada rai zai girma kokuwa Allah dai masani.
Ai kuwa kuka sai ya koma dariya gun Hajiya Falmata don ba ƙaramin farin ciki tayi ba daji an bata Ali har abada, ba ma ta iya musulta farin cikin da take cikin don ji take kamar ƴar uwata in ce gaba-ɗaya take raino, haka dai Hajiya Falmata ta haɗa ɗiyanta biyu gaba ɗaya ta na shayar dasu cikin tsantsan so da gata dan ba ƙaramin ji dasu take ba shima Alhaji Sumana ba'a barsa a baya ba sabida idai yana gari to a kowa ne lokacin suna tare dashi babu wani banbanci da iyayen AFREED ke nunawa ga Ali duk ɗaya suka ɗokesu, har ma sufi yiwa Ali Abu basu ma AFREED ba, Ali dai kam baida maraicin uwa da uba don Hajiya Falmata da Alhaji Sumana ba ƙaramin sonsa suke ba.
Shikuwa mahaifin Ali ya riga da da ya koma ƙasar su ya bar amanar Ali a hannun iyayen AFREED.
AFREED da Ali na da shekara uku uku aka saka su école coranique (islamiyya) da jardin d'enfants (nursery school) Mai tsadan gaske Masha Allah duk da yarinta su haka bai hana su rike abinda ake koyar dasu ba kuma idan sun zo gida Hajiya Falmata ta ƙara koyawar dasu su, AFREED sun tashi cikin gata sosai amma hakan bai hana iyayensu basu tarbiyya ba Hajiya Falmata da Alhaji Sumana suna iya ƙoƙarin su wajan ganin sun basu cikakkiyar tarbiyya, AFREED ya tashi miskili mara son magana bai ƙaunar zama inda ake hayaniya da yawan surutu sedai halinsa yasha banban da na Ali wanda shi kuwa ma'abucin surutu ne da barkwanci duk da wannan halin na surutu na Ali da AFREED bai so amma ba ƙaramin ƙaunar junansu suke ba ko kaɗan basa son ganin junansu cikin damuwa a tare suke komai nasu, ko Hajiya Falmata da Alhaji Sumana basu san tsakanin su ba.
Kwanci tashi babu wuya a wajan Ubangiji su AFREED har sunyi shekara bakwai bakwai sosai sukayi wayo masha Allah idan ka gansu zakayi tunanin sufi shekarun dake garesu sabida tsananin wayo da Allah ya masu. Ita kuwa Hajiya Falmata tunda ta haifi AFREED Ko ɓatan wata bata taɓa yi ba bare ayi batun samun cikin shiru shiru kakeji har saida su AFREED su kayi shekara goma sannan Allah ya ƙara bata haihuwa wanda har sun fida rai da samun ta idan ta haifi ƴan biyu duka mata ranar suna yara aka raɗa masu sunan Fariya da Farisa murna gun AFREED da Ali ba'a magana kullum suna tare dasu an samu ƙanai duk in sun taso daga makaranta suna tare da su bacci kaɗai ke rabasu da ƙannansu.