Sashe 56
Zamba Cikin Aminci Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yana fitowa daga wanka ya tsantsara shiri wanda rabon da da yin sa har ya manta kai kace gun AFREEN ɗin zai je zance ya gama feshe jikin da daɗaɗan turaruka ya fito daga ɓangaren na su gaba ɗaya ya nufi garden inda iskan sanyin maraice ke bugawa, yana ida shiga garden ɗin ya zauna a ɗaya daga cikin kujerun dake gun, tareda fido wayar sa don kiran AFREEN har ya tura kiran kuma da sauri kamin kiran ya shiga sai ya katse kiran, yana tunanin to idan ya kirata mi zai ce mata shi da ba soyayya ya ɓayi ba, hasali ko mace bai taɓa yiwa magana inba secretary ɗin sa in ka fida iyayen sa mata da kuma ƙananan sa, ya na cikin kuma wannan tunanin, saikuma gabansa ya faɗi dalilin tuna cewa ya taɓa ganin AFREED da saurayin ta wajen saukar da su kayi kada a ce ma tayi aure ko da yake da Ali ya samo man labari inda tayi sai kuma yace "Zanyi ko ƙoƙarin saka soyayyata a zuciyarta koda kuwa ta nada wani ai ita allura ce cikin ruwa mai rabo kan samu, kuma in Allah ya yarda malaki na ce shiyasa ma par coïncidence sunayan mu suke shigin na junan mu.
Can AFREED yayi tunanin bari ya fara mata magana ta whatsapp idan tana yi, ai ko take yanke ya shiga whatsapp ɗin sa ya shiga neman sunan da ya sakan mata mai taken ma femme insha Allah (my wife) yana dubawa kam yaga sunanta ya fito a whatsapp kawai ba tare da ɓata lokaci ba ya ɗaga mata hannu tare da rubuta mata salut (hello) sai ya tura cikin sa'a kuma sai a ka yi katarin tana en ligne (online).
*Kashi nayi kokarin wajen ganin na faranta maku har nayi page uku ki da jina kuma sai bayan sallah in da rai da lafiya insha Allahu* 😘😘😘
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
*ZAMBA CIKIN AMINCI*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
Écrit
Par
*QUEEN ZEEFAT*
_Ƴar_
_Mutan_
_Niger_
*Wattpad@nazichou*
💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝
☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️
https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/
*_BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHIM_*
*Page* : 51 & 52
Can AFREED yayi tunanin bari ya fara mata magana ta whatsapp idan tana yi, ai ko take yanke ya shiga whatsapp ɗin sa ya shiga neman sunan da ya sakan mata mai taken ma femme insha Allah (my wife) yana dubawa kam yaga sunanta ya fito a whatsapp kawai ba tare da ɓata lokaci ba ya ɗaga mata hannu tare da rubuta mata salut (hello) sai ya tura cikin sa'a kuma sai a ka yi katarin tana en ligne (online).
AFREEN na cikin chatting da kawayenta a cikin wani group ɗin su da suke tura abubuwan ƙaruwa na Musulunci sai kawai taga alamun saƙo ya shigo da wata bakuwar number da bata sani ba, sai ta fita daga group ɗin ta ƙurawa number ido na kusan minti 3, sai ta sauke ajiyar zuciya tare de cewa can cikin ƙansan zuciyarta "Waye keda wannan number kadai KAMAL ne Idan kuwa shine mi zai ce man kai ba ma shi bane don ba number sa bace, to waye?" AFREEN ta tambayi kanta.
Da har zata huce kuma sai ta buɗe saƙon ta karanta yafi sau uku sannan tayi ta tunanin tashare ko wanene ko kuwa ta mayar danjin ko waye, kawai sai ta yanke shawarar mayar masa da sakon sai ta rubuta masa cewa "salut Xava?"
AFREED nagani ta maido sefa yaji wani farin ciki ya sabko masa a zuciya, bata tare da ɓata lokaci ba ya mayar mata da amsa ta gaisuwa nan dai suka gaisa sannan AFREEN tace "A qui j'ai l'honneur (dawa nake magana)."
Ba tare da wani noke noke ba AFREED ya sanar mata ko shi wanene da kuma inda yasanta sai dai bai faɗa mata matsayin sa ba da kuma aikin da yake.
Nan AFREEN ta sheda shi sannan tayi mamakin inda ya samu number ta, amma bata tambaye shi ba, nan suka ƙara gaisawa, nan dai ya nemi alfarma ta bashi izinin kiranta anjima akwai maganar da yake so zai gayamata, da har taso taki amincewa kawai sai taji ta na so jin abinda zai faɗa ɗin se kawai tace "Allah ya kaimu"
Sannan sukayi sallama AFREEN ta daɗe a zaune ta na tunanin ina ya samu number ta kuma miye abinda yake son faɗa mata, kamin ta tashi ta nufi douche (bathroom) sabida kiraye kirayan sallah magarib da taji an fara ta na shiga ta dauro alwala ta fito ta shimfida darduma ta tayar da sallah.
AFREED na jin AFREEN ta amince da ya kirata hada ɗan tsalle yayi sannan ya nufi ɗakin shi shima ya dauro alwala ya fito a hanya ya haɗu da Ali suka jera suka tafi masallacin a tare.
Wajen ƙarfe goma na dare AFREEN na kwance a saman makeken gadon ta idonta a lumshe kamar mai bacci amma ba bacci take ba saboda bacci ya gagara daukar ta kawai tana kwance tana jiran kiran da AFREED zai mata bata san miyasa ba amma taji tana mugun son ji abinda zai faɗa mata, saboda tana tunowa da kiran nashi kawai sai taji gaban ta ya faɗi shiyasa ta matsu ya kira amma gashi kuma har yanzu bai kira ba, bata ƙarasa tunanin ta ba ƙarar wayar ta ya katse mata tunani da sauri ta tashi zaune ta ɗauki wayar ta riƙe a hannun tare da kurawa number dake yawo akan screen ɗin, wayar har ta katse bata dauka ba, bata ankara ba taji wayar ta sake ɗaukar ruri tana gab da tsinke ta daga kiran tare da kara wayar a kunne, kamin takai ga yin sallama har na cikin wayar ya riga ta da cewa "Amincin Allah ya tabbata a gareki."
Cikin Wata irin sanyayar muryar da batasan tanada ita ba ta buɗe baki cike da faɗuwar gaba da batasan dalilin shi ba tace "Kaima amincin Allah ya tabbata a gare ka," sannan tace "Ina Yuni."
Daga cikin wayar AFREED ya amsa da "Godiya nake cutie da fatan kin yuni cikin ƙoshin lafiya da farin ciki?"
"Alhamdulilah." AFREEN ta faɗa a takaice
AFREED yace "To masha Allah kamar yanda na sanar dake na kiraki ne don muyi wata magana da ta shafe ni kuma ta shafe ki, nasan zaki iya cewa hadake maganar ta shafa saboda ba wani sanin juna muka yi ba hasali maganar da ta taɓa shiga tsakani na dake bata huce biyu ko uku amma kuma Hakan ba abin mamaki dan haka ina buƙatar hankalin ki akan maganar nan."
AFREEN ta sauke wata yar gajeriyar ajiyar zuciya sannan tace "Ba damuwa ina sauraren ka."
Murmushi AFREED ya saki kamar AFREEN na gabansa sannan yace "Ba wani abu bane nakeso sanar dake illa soyayyar ki da ta mani shigar bazata ba tare da na shirya hakan ba ta mamaye ko wane illahirin jijiyoyin da ke cikin jikin na ta ratsa ɓargo da hanta tabi ta kanainaye min zuciya ta na kasa sukuni AFREEN bansan ya zan misulta maki irin ƙaunar da nake maki ba, sonki ya mamaye duk wani jini dake cikin jiki na, dan Allah AFREEN ki taimaka ki karɓi soyayya ta dan Allah wallahi tunda na fara ganin ki na kasa sukuni zuciya ta kasa hutawa kullum ina cikin tunanin ki." AFREED na kai wannan ya sauke wata irin nauyayyar ajiyar zuciya har sai da AFREEN tajiwo hakan a cikin zuciyarsa ya ke cewa, Allah na godema da ka bani courage ɗin bayyana soyayya ta ka wannan baiwa taka saura amincewar ta Allah ka samin hannun ta amince dani."
AFREEN wada tunda AFREED ya fara magana gaban ta ya yawaita faɗuwa da sauri da sauri dan idan a gaban ta maka ke zaka iya jiyo sautin bugawar zuciyar ta, hakan yasa ta kasa koda ƙwaƙwaren motsi haka ta kasa cewa komai don sai juya maganar take a ƙwaƙwalwar ta gashi bakinta yayi mata nauyi ta kasa furta koda kalma ɗaya ce kuma idan ma tace zata buɗe baki tayi magana mi zata ce mashi."
Jin shiru yayi yawa AFREED ya koma cewa "Dan Allah AFREEN ki daure kiyimin magana ko zuciya ta zata samu sallama please ki taimaka min."
Nan shiru AFREEN bata ce komai don tsakanin ta da Allah bakin ta ya mata nauyi ta kasa buɗe shi tayi magana ji take ma bakin ba a jinkin ta yake ba, dan haka ta koma yin shiru saboda idan har ta mayi jarumta buɗe baki tayi magana to tasan da kuka ne zai kubce mata, kawai sai ta koma yin shiru.
Ganin haka yasa AFREED ƙara duba wayar don ganin ko ta katse kiran ne amma mi sai yaga ba ta katse kiran ba da damuwa a fuskar sa ya mayar da wayar a kunnen sa sannan yace "Allo AFREEN kinaji na ki tausaya min kimin magana in har baso kike rayuwa ta ta kare daga yau ba dan Allah kiyi min magana koda ba zata sakani farin ciki ba, dan bansan ko kinada wanda kike so ba idan haka ta kasance ba zan sa dole sai kin so ni ba, amma ki taimaka yanzun kice wani abu s'il te plaît AFREEN."
Ya buɗe baki zai kara cewa wani abun kawai sai yaji ta fashe masa da kuka ai kuwa hankali AFREED in yafi dubu to ya tashi a firgice yace "Inna lilahi wa inna alaihi raji'un AFREEN ki yafe man ban kiraki dan in takura maki ba har nakai ga sakaki kuka nayi ne dan sanar dake sirrin zuciya ta ɗan Allah kiyi hakuri in har abinda na faɗa ya ɓata maki rai, ki taimaki zuciya ta kiyi shuri sai na katse kiran idan har na kashe tare da sanin na barki cikin wannan halin, bazan taɓa iya samun sukuni ba dan ki tausaya man bazan kara takuraki ba idan har bakison magana dani."
Can AFREED yayi tunanin bari ya fara mata magana ta whatsapp idan tana yi, ai ko take yanke ya shiga whatsapp ɗin sa ya shiga neman sunan da ya sakan mata mai taken ma femme insha Allah (my wife) yana dubawa kam yaga sunanta ya fito a whatsapp kawai ba tare da ɓata lokaci ba ya ɗaga mata hannu tare da rubuta mata salut (hello) sai ya tura cikin sa'a kuma sai a ka yi katarin tana en ligne (online).
*Kashi nayi kokarin wajen ganin na faranta maku har nayi page uku ki da jina kuma sai bayan sallah in da rai da lafiya insha Allahu* 😘😘😘
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
*ZAMBA CIKIN AMINCI*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
Écrit
Par
*QUEEN ZEEFAT*
_Ƴar_
_Mutan_
_Niger_
*Wattpad@nazichou*
💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝
☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️
https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/
*_BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHIM_*
*Page* : 51 & 52
Can AFREED yayi tunanin bari ya fara mata magana ta whatsapp idan tana yi, ai ko take yanke ya shiga whatsapp ɗin sa ya shiga neman sunan da ya sakan mata mai taken ma femme insha Allah (my wife) yana dubawa kam yaga sunanta ya fito a whatsapp kawai ba tare da ɓata lokaci ba ya ɗaga mata hannu tare da rubuta mata salut (hello) sai ya tura cikin sa'a kuma sai a ka yi katarin tana en ligne (online).
AFREEN na cikin chatting da kawayenta a cikin wani group ɗin su da suke tura abubuwan ƙaruwa na Musulunci sai kawai taga alamun saƙo ya shigo da wata bakuwar number da bata sani ba, sai ta fita daga group ɗin ta ƙurawa number ido na kusan minti 3, sai ta sauke ajiyar zuciya tare de cewa can cikin ƙansan zuciyarta "Waye keda wannan number kadai KAMAL ne Idan kuwa shine mi zai ce man kai ba ma shi bane don ba number sa bace, to waye?" AFREEN ta tambayi kanta.
Da har zata huce kuma sai ta buɗe saƙon ta karanta yafi sau uku sannan tayi ta tunanin tashare ko wanene ko kuwa ta mayar danjin ko waye, kawai sai ta yanke shawarar mayar masa da sakon sai ta rubuta masa cewa "salut Xava?"
AFREED nagani ta maido sefa yaji wani farin ciki ya sabko masa a zuciya, bata tare da ɓata lokaci ba ya mayar mata da amsa ta gaisuwa nan dai suka gaisa sannan AFREEN tace "A qui j'ai l'honneur (dawa nake magana)."
Ba tare da wani noke noke ba AFREED ya sanar mata ko shi wanene da kuma inda yasanta sai dai bai faɗa mata matsayin sa ba da kuma aikin da yake.
Nan AFREEN ta sheda shi sannan tayi mamakin inda ya samu number ta, amma bata tambaye shi ba, nan suka ƙara gaisawa, nan dai ya nemi alfarma ta bashi izinin kiranta anjima akwai maganar da yake so zai gayamata, da har taso taki amincewa kawai sai taji ta na so jin abinda zai faɗa ɗin se kawai tace "Allah ya kaimu"
Sannan sukayi sallama AFREEN ta daɗe a zaune ta na tunanin ina ya samu number ta kuma miye abinda yake son faɗa mata, kamin ta tashi ta nufi douche (bathroom) sabida kiraye kirayan sallah magarib da taji an fara ta na shiga ta dauro alwala ta fito ta shimfida darduma ta tayar da sallah.
AFREED na jin AFREEN ta amince da ya kirata hada ɗan tsalle yayi sannan ya nufi ɗakin shi shima ya dauro alwala ya fito a hanya ya haɗu da Ali suka jera suka tafi masallacin a tare.
Wajen ƙarfe goma na dare AFREEN na kwance a saman makeken gadon ta idonta a lumshe kamar mai bacci amma ba bacci take ba saboda bacci ya gagara daukar ta kawai tana kwance tana jiran kiran da AFREED zai mata bata san miyasa ba amma taji tana mugun son ji abinda zai faɗa mata, saboda tana tunowa da kiran nashi kawai sai taji gaban ta ya faɗi shiyasa ta matsu ya kira amma gashi kuma har yanzu bai kira ba, bata ƙarasa tunanin ta ba ƙarar wayar ta ya katse mata tunani da sauri ta tashi zaune ta ɗauki wayar ta riƙe a hannun tare da kurawa number dake yawo akan screen ɗin, wayar har ta katse bata dauka ba, bata ankara ba taji wayar ta sake ɗaukar ruri tana gab da tsinke ta daga kiran tare da kara wayar a kunne, kamin takai ga yin sallama har na cikin wayar ya riga ta da cewa "Amincin Allah ya tabbata a gareki."
Cikin Wata irin sanyayar muryar da batasan tanada ita ba ta buɗe baki cike da faɗuwar gaba da batasan dalilin shi ba tace "Kaima amincin Allah ya tabbata a gare ka," sannan tace "Ina Yuni."
Daga cikin wayar AFREED ya amsa da "Godiya nake cutie da fatan kin yuni cikin ƙoshin lafiya da farin ciki?"
"Alhamdulilah." AFREEN ta faɗa a takaice
AFREED yace "To masha Allah kamar yanda na sanar dake na kiraki ne don muyi wata magana da ta shafe ni kuma ta shafe ki, nasan zaki iya cewa hadake maganar ta shafa saboda ba wani sanin juna muka yi ba hasali maganar da ta taɓa shiga tsakani na dake bata huce biyu ko uku amma kuma Hakan ba abin mamaki dan haka ina buƙatar hankalin ki akan maganar nan."
AFREEN ta sauke wata yar gajeriyar ajiyar zuciya sannan tace "Ba damuwa ina sauraren ka."
Murmushi AFREED ya saki kamar AFREEN na gabansa sannan yace "Ba wani abu bane nakeso sanar dake illa soyayyar ki da ta mani shigar bazata ba tare da na shirya hakan ba ta mamaye ko wane illahirin jijiyoyin da ke cikin jikin na ta ratsa ɓargo da hanta tabi ta kanainaye min zuciya ta na kasa sukuni AFREEN bansan ya zan misulta maki irin ƙaunar da nake maki ba, sonki ya mamaye duk wani jini dake cikin jiki na, dan Allah AFREEN ki taimaka ki karɓi soyayya ta dan Allah wallahi tunda na fara ganin ki na kasa sukuni zuciya ta kasa hutawa kullum ina cikin tunanin ki." AFREED na kai wannan ya sauke wata irin nauyayyar ajiyar zuciya har sai da AFREEN tajiwo hakan a cikin zuciyarsa ya ke cewa, Allah na godema da ka bani courage ɗin bayyana soyayya ta ka wannan baiwa taka saura amincewar ta Allah ka samin hannun ta amince dani."
AFREEN wada tunda AFREED ya fara magana gaban ta ya yawaita faɗuwa da sauri da sauri dan idan a gaban ta maka ke zaka iya jiyo sautin bugawar zuciyar ta, hakan yasa ta kasa koda ƙwaƙwaren motsi haka ta kasa cewa komai don sai juya maganar take a ƙwaƙwalwar ta gashi bakinta yayi mata nauyi ta kasa furta koda kalma ɗaya ce kuma idan ma tace zata buɗe baki tayi magana mi zata ce mashi."
Jin shiru yayi yawa AFREED ya koma cewa "Dan Allah AFREEN ki daure kiyimin magana ko zuciya ta zata samu sallama please ki taimaka min."
Nan shiru AFREEN bata ce komai don tsakanin ta da Allah bakin ta ya mata nauyi ta kasa buɗe shi tayi magana ji take ma bakin ba a jinkin ta yake ba, dan haka ta koma yin shiru saboda idan har ta mayi jarumta buɗe baki tayi magana to tasan da kuka ne zai kubce mata, kawai sai ta koma yin shiru.
Ganin haka yasa AFREED ƙara duba wayar don ganin ko ta katse kiran ne amma mi sai yaga ba ta katse kiran ba da damuwa a fuskar sa ya mayar da wayar a kunnen sa sannan yace "Allo AFREEN kinaji na ki tausaya min kimin magana in har baso kike rayuwa ta ta kare daga yau ba dan Allah kiyi min magana koda ba zata sakani farin ciki ba, dan bansan ko kinada wanda kike so ba idan haka ta kasance ba zan sa dole sai kin so ni ba, amma ki taimaka yanzun kice wani abu s'il te plaît AFREEN."
Ya buɗe baki zai kara cewa wani abun kawai sai yaji ta fashe masa da kuka ai kuwa hankali AFREED in yafi dubu to ya tashi a firgice yace "Inna lilahi wa inna alaihi raji'un AFREEN ki yafe man ban kiraki dan in takura maki ba har nakai ga sakaki kuka nayi ne dan sanar dake sirrin zuciya ta ɗan Allah kiyi hakuri in har abinda na faɗa ya ɓata maki rai, ki taimaki zuciya ta kiyi shuri sai na katse kiran idan har na kashe tare da sanin na barki cikin wannan halin, bazan taɓa iya samun sukuni ba dan ki tausaya man bazan kara takuraki ba idan har bakison magana dani."