Sashe 41
Zamba Cikin Aminci Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
AFREED da Zeinab sun saka wata rantsatsiyar shada golden color wada KAMAL ya kawo masu an masu ɗumkin doguwar riga ba'ayi kwalliyar komai ba a rigunan amma yankan rigar kaɗai abin kallo ne, masha Allah ɗumkin ya karɓe su sosai ba ma kamar AFREEN sosai doguwar rigar ta zauna ajikinta ɗas, suka saka farin hijabi dogo har ƙasa sannan AFREEN ta ƙara da wata golden ɗin niƙaf mai mugun kyau, sai fara safa da ke sanye da ƙafarsa da takalmin musu ɗan tsini golden, sosai ta fito kamar wata cikakkiyar balarabiya irin larabawan na Sudan
Firdaoussi da Fanna da Hasina sukaci ankon da aka fido ta saukar ta wani haɗaɗen materiel fari da maron ɗin hijab, suma kuwa nasu hijab ɗin har ƙasa, bayan sun gama shirin nasu tsaf suka fito falon suka tarar da iyayen nasu suma su gama shiryawa suna jiran saukowar papa dan su wuce wajan saukar, haɗa kakar su AFREEN Hajiya Zakiya za'a je wajen saukar.
Iyayen nasu nata murmushi jin daɗin ganinsu cikin kamala kamin wani yace wani abu Hajiya Zakiya tayi saurin cewa "Ah masha Allah ƴan jikokina kunyi kyau Allah maku albarka" ƙara kai dubanta tayi gun AFREEN kamin tace "Ke kam AFREEN har yau bazaki iya haƙura da wannan abin rufe ido ba? Anyi mutum shi kullum fuskar sa a kulle kamar munafiki, ke dan Allah cire mana wannan abin da sai maras gaskiya ke saka shi, ke kuwa da gaskiyarki haba dan Allah." Hajiya Zakiya ta faɗa tana hararen AFREEN dan ta bata haushi sabida yawan saka niƙaf da takeyi.
Murmushi AFREEN tayi sannan tace "Kaka kinga kin fara ko, to ni wallahi bana fitar da ita ba kawai se ki sakamin ido."
"Kijimin ja'irar yarinya Arahamat ina guje maki zafi kina cewa na saka maki ido, to kada fida man ai dan kanki, ga dangin ki nan kowa da fuskarsa buɗe saike kin wani kayo wannan tashin hankali kin saka."
AFREEN ta ɗan turo bakin daga cikin niƙaf tace "Eh anji ɗin kuma ni ban saka tashin hankali ba ehe."
Arahamat mahaifiyar AFREEN tace "Barta dai mama ai ita ce zataji zafin ba wani ba."
Hajiya Zakiya tace "Ah to Arahamat ke ganar min hanya ni kam sai nafasa zuwa wajan saukar nan tunda naga wada akewa saukar ta gama zama fitsarariya."
Da sauri AFREEN taje ta zauna kusa da Hajiya Zakiya tare da riƙo hannu ta tace "Haba kakata mi yayi zafi haka ai idan baki jeba saukar nan ba, ai ba zatayi armashi ba, kuma cewa kin fasa zuwa nima kam zan cire kayan nan nayi zama gaskiya."
Murmushi Hajiya Zakiya tayi tace "Ina ai bazan fasa zuwa da wasa nake jikokin nawa har biyu su na sauke Alkur'ani mai girma sai naki zuwa nasaka masu albarka haba ai ba zai yiwu ba, kuje muje kawai." ta faɗa tare da miƙewa daga inda ta ke zaune, duka ƴan falon suka kwashe da dariya, daidai na papa ya fito shima cikin shirin sa.
Batare da ɓata lokaci ba suka fice daga falon suna isa harabar gidan suka tarar da Fahad da Imran da yan aikin gidan maza da mata hata mai gadi da matarsa da yaransu uku sun shirya suna jiran su domin halartar wajen saukar, banda mutanen da sukazo taya aikin wato yan uwa da abunkan arziki na nesa da na kusa wanda tun ɗazu direbobin gidan suke jida suna kaisu islamiyya.
Papa ne ya isa kusan motarsa ya fitar da ita daga wajan parking sannan AFREEN shikuwa Fahad ya riga da ya fitar da tasa motar, papa ya buɗe ma Hajiya Zakiya gidan baya yace tashiga, amma ƙiri ƙiri tace kam bazata shiga ya saka matan shi su tafi dan ita kam motar Fahad zata shiga, haka kuwa akayi ta shige motar Fahad gidan bayan shikuwa Imran ya zauna wajen mai zaman banza shi kuwa Fahad mazaunin direba, motar papa kuwa Arahamat ke wajen mai zaman banza, umma da tanti gidan baya, papa mazaunin direba, motar AFREEN, Fanna ke mazaunin direba sabida sunce kam yau ba zasu barin AFREEN yin tuƙi ba, AFREEN zaune wajen mai zaman banza, sai Hasina da Zeinab da Firdaoussi gidan baya.
Sauran motocin guda uku kuwa ƴan aikin gidan ne da direbobin gidan da mai gadi da matarsa da ƴaƴan sa a ciki, motar su AFREEN ta fara fita sabida gani da sukayi lokaci nason ƙurewa sannan ta papa baya ta Fahad sannan na ma'aikatan gidan wanda da suka fito saida suka tsaya mai gadi ya fita ya kulo gidan kamin suka kama hanya wada a lokacin motacin mutanen gidan sun kusa ƙarasawa makarantar islamiyyar.
Suna ƙarasawa islamiyya, AFREEN da Zeinab su kayi saurin fita daga motar suka nufin gun ƴan saukar suka nemi gu suka zauna sabida lokacin fara saukar ya kusa, so anan ne wani malami yazo kusa da AFREEN yace mata ai ba nan ne gun zaman ta ba ga inda aka tanada can domin ita sabida ita ɗaya ce za'a yiwa saukar hada da ta littatafan addini tunda suka shiga filin saukar ake bin su AFREEN da kallo sosai shigarsu ta ɗauki ido mutane wasu kam mamaki suke a ina yarinyar ke samu niƙaf ta ko wane kalan kayanta abin na matuƙar ɗaure masu kai sosai yake basu mamaki, bare niƙaf ɗin da ta saka kala golden ga adon Stone dake mugun kyalli.
Lokacin da suka shigo AFREED kanshi duƙe yake yana ɗane danen waya ya dai ji Ali dake kusan shi yace masha Allah, kuma hakan baisa ya ɗago ba, dan ganin abinda Ali ke faɗawa masha Allah.
Ba musu AFREEN ta bi bayan malamin nan har suka ƙarasa gun wata haɗaɗiya kujera sannan yace mata nanga ne gun zamanta, cikin ladabi ta juyo ta kalli malamin tace "Malam da na zauna tareda su can ɗin zan fi sakewa, kaga tunda muka shigo mutane ke bina da kallo ina ga na zauna ana ni ɗaya zan takura, amma idan can ne, sai na zauna a bayan su kaga na kare kaina daga kallo mutane."
Murmushi malamin yayi yace "AFREEN wannan daraja Allah yayi maki godema sa kawai, dolene ki zauna anan sabida yurin da ke ya dace najima banga yarinya mai kwazo da basira irinki ba, wannan baiwar da Allah yayi maki itace yau har ta saka aka wareki daka cikin duban jama'a aka kawo ki nan yarinya 57 da na miji biyu ake yiwa saukar nan amma babu wani da ya kamo koda farcan ki ne bare kafarki, kuma zancen mutane na kallo ki ba wani abu bane, tunda basu ma fara kollon ki ba, sai idan kin fara karatu tunda ai baki manta cewa kece zaki fara karatu duk a cinkin yawan mutanen ga, ke zaki buɗe hilin saukar muyarki mutane zasu faraji da kuma daga ƙarshen muyar dai nan taki ce zata rufe filin saukar nan da addu'a dan haka ki kwantar da hankalin ki fiskanci abinda ke ganki ba yau bane kika fara haka."
AFREEN tace "To shikenan malam." Murmushi malamin yayi kamin ya bar gun nata.
Taro har taro yuri ya cika sosai da sosai idan kaga yanda ɗan adam ya taru a wajen zakayi tunanin cewa duniyar ce baki ɗaya ta haɗu a wajen alhalin ko kaso 1 bai kai ba a cikin ɗari ba.
Babban malamin wato mai islamiyyar ne yaje ya hayo kan manbari ya yi gyaran murya tare da yin sallama sannan yace mutanen su dawo da hankalinsu wajen ɗaya za'a fara sannan yayi wa mutane godiya halartar taron nan da sukayi, sannan ya ƙara da cewa "Ba tare da ɓata lokaci ba zamu kira malama kuma ɗalibar mu, mai hazaƙa kamilala yarinya mai nutsuwa da tarbiyya mai hankali da girmama kowa da kowa koda kuwa ta girmeka zata baka girman ka wada tasan ya kamata mai jin tsoron Allah, kowa na ƙoƙari sosai a makarantar nan kowa nada hazaƙa sabida mukam mun yarda da ɗaliban mu, sedai babu wanda ya kamo ƙafar wannan ƴar albarkar yarinya, zato zo ne ta buɗe mana fili da addu'a sannan tayi karatun.
AFREED najin yanda malamin ke taɗa wannan yarinyar amma bai ɗago daga duƙin da yake ba yana dana wayar sa, har saida Ali yace masa "Wai AFREED miye haka kaida kazo gun sauka kuma shine ka wani buge da dana waya, dan Allah ka ajiye wayar nan ka kalli abinda ya kawo ka nan."
Ba tare da AFREED ya ɗago ba yace "Ali kaga kada ka takura man, da ma banyi niyyar zuwa ba kuka ta kuraman, idan kuwa angaji da gani nane a gun nan sai nayi tafiya ta dama inada abinyi."
Ali yayi murmushi yace "Hum ai babu inda zaka kana nan tare da mu har sai an kammala saukar ehe."
Ko kollon sa AFREED baiyi ba bare yayi tunanin ya amsa masa, Ali ya mayar da hankali sa wajen saukar AFREED kuwa ya ci gaba da aikin da yake a wayar sa.
Can cikin lasipika babban malamin yace " Ba wata bace wannan ɗiyar albarka sai *AFREEN SADISU ASMANE SANGA* , ta fito tazo ta buɗe mana taro da addu'a."
AFREEN ta taso daga inda take zaune ta nufo malamin a nan take idanun jama'a suka dawo kanta, Ali yaro ido dalilin jin suna mai kama dana AFREED taɓo yayi yace "Broh kaji wata mai kalan sunan ka ashe za'a sami mai irin sunanka kuma mace kai amma nata yafi naka daɗi masha Allah."
Keda kecen AFREED in ya tanka to kin tanka bai ma ɗago ba bare Ali yayi tunanin samun amsa kuma badan baiji shi ba, da Ali yaga haka ya san ba tanka masa ba zaiyi, sai ya mayar da hankali sa gun da yafi masa mahimmanci.
AFREEN na ƙarasowa gun manbarin malamin ya sauka ya mata nuni da ta hayo kan mimbarin, ba musu ta ɗale kan tayi sallama kamin ta ke gabatar da kanta, lokacin da tace "Ni sunana *AFREEN SADISU ASMANE SANGA* ina ma kowa barka da zuwa."
Firdaoussi da Fanna da Hasina sukaci ankon da aka fido ta saukar ta wani haɗaɗen materiel fari da maron ɗin hijab, suma kuwa nasu hijab ɗin har ƙasa, bayan sun gama shirin nasu tsaf suka fito falon suka tarar da iyayen nasu suma su gama shiryawa suna jiran saukowar papa dan su wuce wajan saukar, haɗa kakar su AFREEN Hajiya Zakiya za'a je wajen saukar.
Iyayen nasu nata murmushi jin daɗin ganinsu cikin kamala kamin wani yace wani abu Hajiya Zakiya tayi saurin cewa "Ah masha Allah ƴan jikokina kunyi kyau Allah maku albarka" ƙara kai dubanta tayi gun AFREEN kamin tace "Ke kam AFREEN har yau bazaki iya haƙura da wannan abin rufe ido ba? Anyi mutum shi kullum fuskar sa a kulle kamar munafiki, ke dan Allah cire mana wannan abin da sai maras gaskiya ke saka shi, ke kuwa da gaskiyarki haba dan Allah." Hajiya Zakiya ta faɗa tana hararen AFREEN dan ta bata haushi sabida yawan saka niƙaf da takeyi.
Murmushi AFREEN tayi sannan tace "Kaka kinga kin fara ko, to ni wallahi bana fitar da ita ba kawai se ki sakamin ido."
"Kijimin ja'irar yarinya Arahamat ina guje maki zafi kina cewa na saka maki ido, to kada fida man ai dan kanki, ga dangin ki nan kowa da fuskarsa buɗe saike kin wani kayo wannan tashin hankali kin saka."
AFREEN ta ɗan turo bakin daga cikin niƙaf tace "Eh anji ɗin kuma ni ban saka tashin hankali ba ehe."
Arahamat mahaifiyar AFREEN tace "Barta dai mama ai ita ce zataji zafin ba wani ba."
Hajiya Zakiya tace "Ah to Arahamat ke ganar min hanya ni kam sai nafasa zuwa wajan saukar nan tunda naga wada akewa saukar ta gama zama fitsarariya."
Da sauri AFREEN taje ta zauna kusa da Hajiya Zakiya tare da riƙo hannu ta tace "Haba kakata mi yayi zafi haka ai idan baki jeba saukar nan ba, ai ba zatayi armashi ba, kuma cewa kin fasa zuwa nima kam zan cire kayan nan nayi zama gaskiya."
Murmushi Hajiya Zakiya tayi tace "Ina ai bazan fasa zuwa da wasa nake jikokin nawa har biyu su na sauke Alkur'ani mai girma sai naki zuwa nasaka masu albarka haba ai ba zai yiwu ba, kuje muje kawai." ta faɗa tare da miƙewa daga inda ta ke zaune, duka ƴan falon suka kwashe da dariya, daidai na papa ya fito shima cikin shirin sa.
Batare da ɓata lokaci ba suka fice daga falon suna isa harabar gidan suka tarar da Fahad da Imran da yan aikin gidan maza da mata hata mai gadi da matarsa da yaransu uku sun shirya suna jiran su domin halartar wajen saukar, banda mutanen da sukazo taya aikin wato yan uwa da abunkan arziki na nesa da na kusa wanda tun ɗazu direbobin gidan suke jida suna kaisu islamiyya.
Papa ne ya isa kusan motarsa ya fitar da ita daga wajan parking sannan AFREEN shikuwa Fahad ya riga da ya fitar da tasa motar, papa ya buɗe ma Hajiya Zakiya gidan baya yace tashiga, amma ƙiri ƙiri tace kam bazata shiga ya saka matan shi su tafi dan ita kam motar Fahad zata shiga, haka kuwa akayi ta shige motar Fahad gidan bayan shikuwa Imran ya zauna wajen mai zaman banza shi kuwa Fahad mazaunin direba, motar papa kuwa Arahamat ke wajen mai zaman banza, umma da tanti gidan baya, papa mazaunin direba, motar AFREEN, Fanna ke mazaunin direba sabida sunce kam yau ba zasu barin AFREEN yin tuƙi ba, AFREEN zaune wajen mai zaman banza, sai Hasina da Zeinab da Firdaoussi gidan baya.
Sauran motocin guda uku kuwa ƴan aikin gidan ne da direbobin gidan da mai gadi da matarsa da ƴaƴan sa a ciki, motar su AFREEN ta fara fita sabida gani da sukayi lokaci nason ƙurewa sannan ta papa baya ta Fahad sannan na ma'aikatan gidan wanda da suka fito saida suka tsaya mai gadi ya fita ya kulo gidan kamin suka kama hanya wada a lokacin motacin mutanen gidan sun kusa ƙarasawa makarantar islamiyyar.
Suna ƙarasawa islamiyya, AFREEN da Zeinab su kayi saurin fita daga motar suka nufin gun ƴan saukar suka nemi gu suka zauna sabida lokacin fara saukar ya kusa, so anan ne wani malami yazo kusa da AFREEN yace mata ai ba nan ne gun zaman ta ba ga inda aka tanada can domin ita sabida ita ɗaya ce za'a yiwa saukar hada da ta littatafan addini tunda suka shiga filin saukar ake bin su AFREEN da kallo sosai shigarsu ta ɗauki ido mutane wasu kam mamaki suke a ina yarinyar ke samu niƙaf ta ko wane kalan kayanta abin na matuƙar ɗaure masu kai sosai yake basu mamaki, bare niƙaf ɗin da ta saka kala golden ga adon Stone dake mugun kyalli.
Lokacin da suka shigo AFREED kanshi duƙe yake yana ɗane danen waya ya dai ji Ali dake kusan shi yace masha Allah, kuma hakan baisa ya ɗago ba, dan ganin abinda Ali ke faɗawa masha Allah.
Ba musu AFREEN ta bi bayan malamin nan har suka ƙarasa gun wata haɗaɗiya kujera sannan yace mata nanga ne gun zamanta, cikin ladabi ta juyo ta kalli malamin tace "Malam da na zauna tareda su can ɗin zan fi sakewa, kaga tunda muka shigo mutane ke bina da kallo ina ga na zauna ana ni ɗaya zan takura, amma idan can ne, sai na zauna a bayan su kaga na kare kaina daga kallo mutane."
Murmushi malamin yayi yace "AFREEN wannan daraja Allah yayi maki godema sa kawai, dolene ki zauna anan sabida yurin da ke ya dace najima banga yarinya mai kwazo da basira irinki ba, wannan baiwar da Allah yayi maki itace yau har ta saka aka wareki daka cikin duban jama'a aka kawo ki nan yarinya 57 da na miji biyu ake yiwa saukar nan amma babu wani da ya kamo koda farcan ki ne bare kafarki, kuma zancen mutane na kallo ki ba wani abu bane, tunda basu ma fara kollon ki ba, sai idan kin fara karatu tunda ai baki manta cewa kece zaki fara karatu duk a cinkin yawan mutanen ga, ke zaki buɗe hilin saukar muyarki mutane zasu faraji da kuma daga ƙarshen muyar dai nan taki ce zata rufe filin saukar nan da addu'a dan haka ki kwantar da hankalin ki fiskanci abinda ke ganki ba yau bane kika fara haka."
AFREEN tace "To shikenan malam." Murmushi malamin yayi kamin ya bar gun nata.
Taro har taro yuri ya cika sosai da sosai idan kaga yanda ɗan adam ya taru a wajen zakayi tunanin cewa duniyar ce baki ɗaya ta haɗu a wajen alhalin ko kaso 1 bai kai ba a cikin ɗari ba.
Babban malamin wato mai islamiyyar ne yaje ya hayo kan manbari ya yi gyaran murya tare da yin sallama sannan yace mutanen su dawo da hankalinsu wajen ɗaya za'a fara sannan yayi wa mutane godiya halartar taron nan da sukayi, sannan ya ƙara da cewa "Ba tare da ɓata lokaci ba zamu kira malama kuma ɗalibar mu, mai hazaƙa kamilala yarinya mai nutsuwa da tarbiyya mai hankali da girmama kowa da kowa koda kuwa ta girmeka zata baka girman ka wada tasan ya kamata mai jin tsoron Allah, kowa na ƙoƙari sosai a makarantar nan kowa nada hazaƙa sabida mukam mun yarda da ɗaliban mu, sedai babu wanda ya kamo ƙafar wannan ƴar albarkar yarinya, zato zo ne ta buɗe mana fili da addu'a sannan tayi karatun.
AFREED najin yanda malamin ke taɗa wannan yarinyar amma bai ɗago daga duƙin da yake ba yana dana wayar sa, har saida Ali yace masa "Wai AFREED miye haka kaida kazo gun sauka kuma shine ka wani buge da dana waya, dan Allah ka ajiye wayar nan ka kalli abinda ya kawo ka nan."
Ba tare da AFREED ya ɗago ba yace "Ali kaga kada ka takura man, da ma banyi niyyar zuwa ba kuka ta kuraman, idan kuwa angaji da gani nane a gun nan sai nayi tafiya ta dama inada abinyi."
Ali yayi murmushi yace "Hum ai babu inda zaka kana nan tare da mu har sai an kammala saukar ehe."
Ko kollon sa AFREED baiyi ba bare yayi tunanin ya amsa masa, Ali ya mayar da hankali sa wajen saukar AFREED kuwa ya ci gaba da aikin da yake a wayar sa.
Can cikin lasipika babban malamin yace " Ba wata bace wannan ɗiyar albarka sai *AFREEN SADISU ASMANE SANGA* , ta fito tazo ta buɗe mana taro da addu'a."
AFREEN ta taso daga inda take zaune ta nufo malamin a nan take idanun jama'a suka dawo kanta, Ali yaro ido dalilin jin suna mai kama dana AFREED taɓo yayi yace "Broh kaji wata mai kalan sunan ka ashe za'a sami mai irin sunanka kuma mace kai amma nata yafi naka daɗi masha Allah."
Keda kecen AFREED in ya tanka to kin tanka bai ma ɗago ba bare Ali yayi tunanin samun amsa kuma badan baiji shi ba, da Ali yaga haka ya san ba tanka masa ba zaiyi, sai ya mayar da hankali sa gun da yafi masa mahimmanci.
AFREEN na ƙarasowa gun manbarin malamin ya sauka ya mata nuni da ta hayo kan mimbarin, ba musu ta ɗale kan tayi sallama kamin ta ke gabatar da kanta, lokacin da tace "Ni sunana *AFREEN SADISU ASMANE SANGA* ina ma kowa barka da zuwa."