← Book details Zamba Cikin Aminci Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 58 OF 69

Sashe 58

Zamba Cikin Aminci Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Kamar yanda yayi mata alƙawari dare bayi ba sosai ya kira ta bayan anyi sallah isha suka dan taɓa hira ta kusan minti arba'in sannan yayi mata saida safe, haka ga goben ma yayi mata kira uku kamin na dare, dare nayi ya kirata kamar yanda ya saba bayan anyi sallah isha, nan suka gaisa ya tambaye ta alƙawarin da tayi masa na bashi amsa yau, bata wani bata lokaci ba ta ce masa ta amince, farin ciki kamar ya kashe AFREED a ranar jiyake bai taɓa shiga farin ciki irin na wannan ranar ba nan suka shiga fira soyayya mai ratsa zuciyar masoya, da yake AFREED ba gwani bane wajen gayin kalaman soyayya tunda bai ta yi ba amma duk da haka ya ƙoƙarta sun sha soyayyar su harda dare yayi sosai sannan suka yiwa junansu sallama badan sun so ba, sai dan lokacin sallah dare da AFREEN keyi yayi, tunda ga wannan ranar soyayya mai tsanani ta shiga tsakani AFREEN da AFREED dan ko basu awa ɗaya basu ji muryar juna ba.

Kwanci tashi babu wuya a wajen Ubangiji yau yakama saura kwana guda auren Khairat kuma yau ne dadyn AFREED da docter Inusa zasu zo Maraɗi dan su halarci ɗaurin auren diyar aminin su wato Alhaji sadisu da ake yi gobe misalin ƙarfe takwas na safe.

Sun baro garin Niamey ƙarfe tara daidai amma da yake mota personnel ce ƙarfe huɗu nayi su na cikin garin maraɗi, a wani gida injiniya Sumana dake cikin anguwar Zaria, gidan ko ina a share a gyare kamar dai da mutane a ciki, ba su wani ɓata lokaci ba sukayi wanka suka huta, sai ga kiran Alhaji Sadisu ya shigo wayar injiniya Sumana yana tambayar su har yanzu basu ƙarso ba, yace masa su ji ma da ƙaraso wa dan sunyi har wanka sun huta, nan ya tambaye sa inda suke ya sanar da shi sannan Alhaji Sadisu ya ce gashinan zuwa ya ɗauko su zuwa gidan sa tare, da an riga da anyi abincin tarbar su bansu, ba tare da sunyi musu ba suka amince, kusan minti ashirin da gama wayar sai gashi yazo basu wani bata lokaci ba suka kule gidan tare da da shiga motar Alhaji Sadisu suka ɗauki hanyar gidan sa wani minti ashirin ɗin suka ɓata kamin suke isa gida, direct ɓangaren Alhajin suka nufa, suna shiga suka sauka saman mayan kujerun da ke falon daga nan suka ƙara gaisawa, sai ga uwan gidan suna shigowa da ɗaiɗaya suna gaisawa, nan fa aka fara servir ɗin su aka cika falon papa da kayan ciye ciye da lashe lashe kamar sunzo restaurant daga ƙarshe AFREEN ta shigo da sallama da juice 🥤 ɗin gwaba da yaji kayan haɗin sosai sai kamshi yake a hannun ta daga ji kasan zai yi ɗaɗin ɗanɗano, ciki shigar ta ta ƙaton hijabi har ƙasa tana shiga ta duka har ƙasa ta gaishe su da ladabi kan ta a duƙe."

Kallo injiniya Sumana ya bita dashi sannan ya amsa gaisuwar ta, sannan AFREEN ta mike ta fice, tana fita injiniya ya kalli Alhaji Sadisu yace "Alhaji wannan ma yarinyar Arahamat ce ko saboda ga kama nan masha Allah kyakkyawa da ita har ta fi maman ta, se kuma ta ɗauko kalar fatar ka ba tayi hasken mahaifiyar ta din ba, ni ina tunanin daga Khairat Arahamat bata da wata yarinyar sai in maza ashe akwai wannan."

Murmushi papa yayi kamin yace wani abun docter Inusa yace "AFREEN ba ɗiyar jannah kenan ai yanzu da muka yi waya da ita take ce min dan Allah idan zan dawo na zo mata da yara ta wato AFREEN."

Wani murmushin papa ya koma yi sannan yace "Ai jininsu ya haɗu da jannah sosai fiye da yanda kake tsammani."

Injiniya Sumana yace "Hakane yanzu nan zata iya yin wata shawara da jannah bata yi ta da mahaifiyar ta, amma nikam da za'a ban ita na bawa yaron nan AFREED, da ya kasa fitar da wace ya keso gashi nan kannin sa har saura wata biyu auren su so yake sai ya gama zama tuzuru nasan ko zaiyi auren, yaro sai taurin kan tsiya babu wanda banyi ya fitar da wace ya ke so ba ya ki ko dan a saka masu rana ɗaya da yan uwansa amma yaki." Dady ya fada dan ɓacin rai kaɗan a fuskar sa

Murmushi Alhaji Sadisu yayi sannan yace "Ai kam da nayi farin ciki idan hakan ta faru zumunci mu zai ƙara ƙarfi sosai, ko maman su nasan da sai tayi farin ciki sosai da hakan kuma Allah sa alkairi ne zamu haɗa."

Docter Inusa ma murmushin ya yi kamin yace gaskiya hakan kuwa abu ne me kyau, kuma insha Allahu alkairi ne gashi ma sunan yaran nawa kusan irin ɗaya ne AFREEN da AFREED kamar wasu yan tagwaye kuma dukan su akwai hankali da nutsuwa sosai a tatare da su daga gani zaman su zai yi armashi insha Allahu, sedai wani hanzari ba gudu ba ya kamata Ku sanar dasu ko sun amince ba auren dole zaku masu ba, dan ba kusan ko wani daga cikin yana da wanda yake so gaskiya a basu zaɓi."

Da sauri injiniya Sumana yace "Ko alama bazan sanar da AFREED komai ba sedai ya ga amarya komai nine zanyi dama na faɗa masa idan har ya yarda ya kaini bango zan nema masa matar da kaina, gashi kuma yanzu na samu yarinya mai hankali da tarbiyya ɗiyar aminina ai babu abinda zai hanani yi masa auren nan, sedai in ita yarinyar ce bata so ko kuma tana da wanda take so nan babu wanda ya isa ya mata dole wallahi ni ne nan zan tsaya mata har sai an aura mata wanda take so." Nan ranshi a ɗan ɓace ya ida maganar."

Alhaji Sadisu yace kwantar da hankalin injiniya insha Allahu haɗin zai yiwu kuma zai zama alkairi da yardar Ubangiji, duk da banjin cewa AFREEN na da wani sauri bayan wancen, da har bata faɗa min ba amma zan tuntuɓe ta, kuma zan faɗa maka shawara da na yanke daga nan idan ta amince sai muyi abinda ya dace dan nasan zata min biyayya insha Allahu.

Farin ciki gun injiniya Sumana ba'a magana kamar ance masa yarinyar ta amince ko kuwa gashi har an kaita gidan sa a matsayin matar AFREED, shima docter Inusa ya nata farin ciki kamar wata ɗiyar sa.

Daga nan suka sauka saman kafet suka fara cin abinci, sosai suka ci suka koshi, suka yi hamadah tare da ci gaba da fira su, sai wajajen ƙarfe goma na dare suka yiwa papa sallama suka kuma ma sauƙin su duk da babu yanda papa bayi ba su kwana a gidan suka tare da cewa haba Alhaji kai baka ga yanda baƙi suka cika gidan ba mu koma masaukin mu zai fi gobe in Allah ya yarda zamuyo samakon ɗaurin aure, haka suka ɗauki motar aminin na su suka tafi da ita,

Washegari tun ƙarfe biyar kowa na gidan sai shirin ɗaurin aure suke, kamin karfe takwas tayi har kowa ya shirya ga gidan ya cika makil da yan ɗaurin aure, waje ko hanyar yucewa babu sai ka ɗan karkata kamin kasa mu shi ga gidan iyayen gidan mata gaba ɗaya sunci shiri cikin wasu narkakun shadadodi na ganin na faɗa kana gani kasan a kashi kuɗi a wajen nan, haka yaran gidan su ma da kalar tasu shadar mai mugun tsada.
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
*ZAMBA CIKIN AMINCI*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸

Écrit

Par

*QUEEN ZEEFAT*

_Ƴar_
_Mutun_
_Niger_

*Wattpad@nazichou*

_*BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHIM*_

*Page* : 55 & 56

Sai kam ta AFREEN da tafi ta kowa haɗuwa dan ko ta iyayen nasu sai tayi saboda son da Alhaji Sadisu ke yiwa AFREEN ya saka komai na ta daban yake a gidan ta fito ta yi shar da ita, kamar wata matar shugaban kasa, kowa sai yaba kyaun ta da mamakin irin wannan kyau na ta mara misali, sai mutane ke mamakin kyau irin na AFREEN Ita dai tafi mahaifiyar ta kyau nesa ba kusa ba amma kana kallon ta ka san ita ta haife ta sabida suna ɗan kama sedai maman ta ta fita haske sosai, kalar fatar mahaifinta ta ɗauko mai ɗan duhu da sheƙi da haske wanda ba za'a iya saka ta a layin farare ba, sai ƙwayar idon ta dake kalar chocolat color amma cikin su fari tas ne mai walk'iya da ɗaukar ido har da ɗan ƙaramin baki da surcecen hanci har baka masha Allah.

Ƙarfe takwas daidai duban jama'a suka shaida ɗaurin auren Khairat Alhaji Sadisu da angon ta Ahmed sufiyane bisa sadaki 100000F CFA, kamin kace mi labari har yaje ga kunnan Khairat wace ana gayama ta, tayi hamdalah ga Ubangiji a cikin zuciyar ta, taron ɗaurin aure ya watse lafiya ida aka maida taron yinin biki, Alhaji yana cen kofar gida cikin inuwa wata babba bishiya tare da abokansa kusan su goma suna ta fira su cikin farin ciki.

Biki ya yi biki ida aka shirya amarya cikin wani haɗaɗan lace marron ta haɗu har ta gaji da haɗuwa, nan fa aka fitar da ita babban falon gidan ana ta photo, nan su AFREEN an shirya cikin wani haɗaɗan matériel blue 🔵 sai sheƙi yake mutane na ta photo da ita kamar ita ke amarya.

Ƙarfe takwas daidai na dare aka tafi kai amarya gidan mijinta ta sai wajen tara da arba'in yan kan amarya suka dawo, masha Allah taro ya watse lafiya sai fatan zaman lafiya tsakanin ango da amarya.

A gajiye su AFREEN ƴan kai amarya suka dawo gida, direct ɗakin ta nufa ta faɗa toillet ta yi wanka tare da ɗauro alwala ta zo ta gabatar da shafa'i da wutiri sannan taje gan mirror ta ɗauko wayar ta kashe tun farkawar ta da asuba bayan tayiwa AFREED Barka da safiya ta kashe ta ɗan ta samu tayi bikin ƴar uwar ta hankali kwance da nutsuwa.
Chapter 58 · 0% Book details