Sashe 48
Zamba Cikin Aminci Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Juyowa Ali yayi ya rungume Momy yana share hawayen sa shima yace "Dan Allah momy kiyi hakuri na daina kukan wallahi hankali na a mugun tashe yake gani nake kamar za su fito su ceman ya mutu wallahi da bazan taɓa yafewa kaina ba momy, kuma ni a rayuwar nan ba nida wata uwa sai ke ni ban sa ɗaɗin tawa mahaifiyar ba dan ko kamanin tama bansani ba sai a hoto ta kawoni duniya sai ta tafi ta barni bakina da ita addu'a dan samun rahamar Ubangiji da soyayyar dake tsakanin ɗa da uwa in bashi ba bu wani abun, in badan mahaifina dake raye ba ni nasa da bazan taɓa sani cewa dake da dady ba kune kuka haifeni ba dan kun riƙe ni matsayin ku na iyaye fiye da wasu iyayen ma, da akwai wani matsayi da ya fi matsayin iyaye a wajen ɗa ga iyayen sa to da na baku matsayi wannan matsayin dan kune komai na rayuwa ta sai kuma mahaifin na, ina mama(mahaifiyar Ali) addu'a cewa Allah ya sadata da Mala'ikun rahama kuma ya sadamu a aljanar Firdaoussi." Ali ya faɗa ya ƙarasa share hawayen sa kuma har yanzu yana rugume jikin Momy, itama a boye tana share hawayen ta dan bai kamata ita dake babba ba tayi tayi abu kamar wata karamar yarinya dan tasan suna gane tana cikin ta shin hankali zata iya tayar masu dana su, dama gashi a tashan yake dan ta nuna masu dauriya ne suma suke ɗan rage damuwa.
Kamin momy tace wa Ali wani abu wayar ta ta ɗauki rururi da sauri ta duba tana ganin dady ne ta tuna da ta shiga tashi hankali nan ta ma manta bata faɗa masa halin da ake ciki ba, da sauri ta saki Ali ta shiga ƴar couloir (korkorda) da ke bayan ɗakin da AFREED yake ta ɗaga wayar sallama yayi tayi shiru ya kara ta biyu babu amsa sai yace "Mama ƴan biyu kina jina kuwa, kodai yau sai angama min jan ajin irin naku na mata kamin za'a amsa min, oh kodai dan ɗazu da safe kin kirani ne ban ɗaga ba? wallahi ina wajen meeting wayar kuma tana cikin bureau na (office)."
Shiru batace komai ba dan ita tana ƙoƙarin mayar da kukan da ke shirin zuwar mata idan ta yarda ta buɗe baki da niyyar yin magana."
Kusan minti uku yana jiran yaji tace wani abu amma shiru sai yayi tunanin ko ta kashe wayar ne, saiya sauke wayar a kunanan shi ya duba amma yaga ba kashe kiran bane tayi, sai yaci ka da mamaki yayi saurin mayar da wayar a kunanan sa tare da cewa maman ƴan biyu (da yake haka yake kiranta da shi) laifin nawa har yakai a ƙiyi min magana wallahi ina meeting ne shiyasa ban ɗaga kiran ki ba, Ni bansan nayi wani laifi ba in ba wanan ba, dan haka kiyi hakuri idan wani laifin ne nayi da ban sani ba shima ayi hakuri Allah ya huci zuciyar uwar gida na kuma uwa ƴaƴana masu albarka, ko dayake nasan anjima zaki huce bari na kashe zan ƙara kiranki anjima (ya faɗi hakan cikin zolaya kuma yasan da yace zai kashe to zatayi masa magana, ah ni tsofaffi da soyayya).
Momy najin alamun dady zai kashe wayar cikin sauri da wani irin kuka da ya kubce mata tace "Dady AFREED." Ta faɗa ba tare dama sunan ya fito da kyau ba sabida kukan daya ci ƙarfin ta, kuma ta ƙasa ƙarasa abinda tayi niyyar faɗa."
Ai dady najin kukan matar shi farin cikin shi abin alfahari sa kuma mafi soyuwa a cikin zuciyarsa ai sai hankalinsa ya tashi iya tashi baisan lokacin da ya faɗi sunanta ta zane ba yace "Falmata lafiya mike faruwa ya naji muyar cikin tashi hankali haka rabon da naji ko na gani kiyi kuka tun rasuwar yar uwarki kuma ƙanwar ki mahaifiyar Ali ko kuma tashin hankali irin wannan dan Allah faɗa min mike faru yawe ya rasu ko ya tayar min da hankalin ki ko waye babu lafiya? wallahi tun safe da natashi naji hankali na ya ƙi kwanciya naso na kiraki kuma mutane suka azazaleni sai na fito mun shiga meeting, haka ba dan hankali na ya kwanta ba na bisu muka shiga meeting sannan kuma ina fito na tarda appelle manque (miss call) ɗin ki kawai sai gabana ya faɗi dan Allah daure faɗa min abinda ke faru kisan hankali na ya ƙara tashi."
Cikin kuka da ta ɗan rage tace "Dady AFREED dama AFREED ne......." Kuma sai kuka ya kwace mata ta kasa ƙarasa abinda tayi niyyar faɗa.
Ai kuwa hankalin dady in yafi dubu to ya tashi jin abin ma saman kan ɗan sa ne gudan jininsa abin kaunar sa, da sauri cikin ɗaga muyar cike da tashin hankali yace "Maman ƴan biyu daure ki faɗa miyasa mi yaro na da kuka boyemin, mike faruwa dashi ne idan kuka yar wani abun ya sameshi dani daku ba zamu shirya ba, kada ki yarda ki faɗa man cewa bashi da rai?"
Hankali momy ya ƙara mugun tashi ganin har mahaifin nasa da take gani zai yi dangana amma ya rikice har haka wai wane irin so ne suke yiwa AFREED haka dan ma Allah yasa basa nunawa sosai da babu san ko AFREED zai iya zama mai wani juyayan hali ba duk da ko yanzu ɗin halin sai a hankali uwa uba miskilanci, kawar da wannan tunanin tayi, lokacin da taji dady AFREED ya daka mata tsawa yana cewa "Ba zaki faɗa min abinda ya sami yarona ba."
Da sauri momy itama cikin dusashewar muyar tace "Dady AFREED wallahi nima ban sani ba ina ganin ciwon sa ne ya tashi nima ina cikin falo nida su Farisa, Ilya direba ya shigo yace man ga Ali cen ya tafi da AFREED asibiti kuma AFREED ɗin baya cikin hankalin sa yana tunanin a some yake lokacin da ya tafi da shima, ba tare da na tsaya ya ƙarasa maganar saba, na shige ɗaki na saɓo hijab ya kawo mu asibitin muna zuwa kuwa har an shiga dashi urgence (emergency) mun tardo Ali a bakin ƙofar ɗakin dayake cikin, nayi masa tambayar duniyar nan ya faɗa abinda ya sami AFREED ya kasa faɗa min sai kuka yake da kair na samu na rarashe sukayi shiru kuma mun kusan awa huɗu anan har yanzu babu likitan da ya fito daga ɗakin ma bare su faɗa mana hali da yake ciki kwata kwata hankali na yaƙin kwanciya na kasa daurewa zuciyata ta ƙarye gani nake zan rasa shine abu shiru haka dan Allah dady AFREED kayi wani abu."
Sai a sannan dady ya sauke wata ajiyar zuciya, ba dan hankali sa ya kwanta ba a'a dan dai shin ke namiji kuma shine babban indan bai kwantar masu da hankali ba ko ya nuna dangana ba to su ya zasuyi, ɗan nisawa dady yayi cikin sanyayar muryar mai kwantar da hankali yace "Ke kina kuka yaranki nayi wa zai bawa wani haƙura a cikin ku gashi kuma ke ce babba idan baki nuna dangana da kawaici ba su ya kike so suyi kuje asibiti kuyita koke koke kamar wasu maras hankali kece babba fah ke zaki basu haƙura ba wai ki biye masu ba ayita kukaba, je ki ƙara kwantar masu da hankali sannan ki rarashesu da ikon Allah, Allah zai tashi ƙafaɗu sa in Allah ya yarda zai sami lafiya, sannan batun inyi wani abun bai taso ba nida bani gari, ke koma a gari nake ba zanja da ikon Allah ba, ba zan iya bashi lafiya ba saidai wanda ya aza mashi shi zai yaye masa wahala nima kuma ina a hanya nan da ƙarfe biyu jirgin mu zai sauka insha Allahu faɗa man wani asibiti kuke dan ina sauka nan zan wucike."
"Clinique HADAMALAH" momy ta faɗa a taƙaice.
Ok ta Dr Inusa kenan ai abokinna ne gayamin number ɗakin da yake zan kira yanzu Dr Inusa na faɗa masa yaje ya duba shi da kanshi kamin na karaso."
Momy tace "Bon ɗakin dayake ciki numéro (number)45 amma idan sun fito dashi za a kaishi ɗaki personnel inda zai huta ba za'a haɗasa da kowa ba yanzu zanje nasa Ali yaje ya biya kuɗin babban ɗaki mai komai da komai a cikin."
"Eh hakanan ya kamata yi sauri ki koma gurin su kin barsu su ɗaya yanzu haka suna cen su na kukan."
Momy tace "To shikenan sai kazo Allah ya kawo ka lafiya."
Da ameen dady ya amsa tare da kashe wayar, dady na kashe kiran momy ta koma wajen su Ali tace "Ya je ya biya kuɗin ɗakin da za'a saka AFREED idan an fito da shi. ba musu Ali ya miƙe ya nufi inda ake biyan kuɗin."
Shiku dady ya na gama waya da momy ya kiran Dr Inusa ya sanar da shi Dr Inusa najin cewa ɗan abokinsa ne kuma a matse yake, yasa shi saurin miƙewa ya kashe kiran dady ba tare da ya bari ya idasa jin abinda dady zai ce ba ya tashi ya nufi ɗakin da AFREED ke ciki su momy na nan zaune saida sukaga muntun ya buɗe ɗaki ya shige suka ƙara baza ido.
Dr Inusa bai fi minti talatin da shiga ba sai gashi ya fito, ida su momy ke zaune ya nufa yace "Madame kune ku ka kawo AFREED Sumana ko naga kama"
Da sauri momy da su Farisa su ka miƙe momy tace "Eh mune."
Dan murmushi ya saki yace "Kun kwantar da hankalin ku biyoni office."
Momy tace "To." Tana ƙoƙarin kiran Ali a waya dan ta faɗa masa cewa ya tardosu office ɗin Dr Inusa.
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
*ZAMBA CIKIN AMINCI*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
Écrit
Par
*QUEEN ZEEFAT*
_Ƴar_
_Mutan_
_Niger_
*Wattpad@nazichou*
💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝
☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️
https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/
*_BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHIM_*
*Page* : 45 & 46
*Wanene DR Inusa*
Kamin momy tace wa Ali wani abu wayar ta ta ɗauki rururi da sauri ta duba tana ganin dady ne ta tuna da ta shiga tashi hankali nan ta ma manta bata faɗa masa halin da ake ciki ba, da sauri ta saki Ali ta shiga ƴar couloir (korkorda) da ke bayan ɗakin da AFREED yake ta ɗaga wayar sallama yayi tayi shiru ya kara ta biyu babu amsa sai yace "Mama ƴan biyu kina jina kuwa, kodai yau sai angama min jan ajin irin naku na mata kamin za'a amsa min, oh kodai dan ɗazu da safe kin kirani ne ban ɗaga ba? wallahi ina wajen meeting wayar kuma tana cikin bureau na (office)."
Shiru batace komai ba dan ita tana ƙoƙarin mayar da kukan da ke shirin zuwar mata idan ta yarda ta buɗe baki da niyyar yin magana."
Kusan minti uku yana jiran yaji tace wani abu amma shiru sai yayi tunanin ko ta kashe wayar ne, saiya sauke wayar a kunanan shi ya duba amma yaga ba kashe kiran bane tayi, sai yaci ka da mamaki yayi saurin mayar da wayar a kunanan sa tare da cewa maman ƴan biyu (da yake haka yake kiranta da shi) laifin nawa har yakai a ƙiyi min magana wallahi ina meeting ne shiyasa ban ɗaga kiran ki ba, Ni bansan nayi wani laifi ba in ba wanan ba, dan haka kiyi hakuri idan wani laifin ne nayi da ban sani ba shima ayi hakuri Allah ya huci zuciyar uwar gida na kuma uwa ƴaƴana masu albarka, ko dayake nasan anjima zaki huce bari na kashe zan ƙara kiranki anjima (ya faɗi hakan cikin zolaya kuma yasan da yace zai kashe to zatayi masa magana, ah ni tsofaffi da soyayya).
Momy najin alamun dady zai kashe wayar cikin sauri da wani irin kuka da ya kubce mata tace "Dady AFREED." Ta faɗa ba tare dama sunan ya fito da kyau ba sabida kukan daya ci ƙarfin ta, kuma ta ƙasa ƙarasa abinda tayi niyyar faɗa."
Ai dady najin kukan matar shi farin cikin shi abin alfahari sa kuma mafi soyuwa a cikin zuciyarsa ai sai hankalinsa ya tashi iya tashi baisan lokacin da ya faɗi sunanta ta zane ba yace "Falmata lafiya mike faruwa ya naji muyar cikin tashi hankali haka rabon da naji ko na gani kiyi kuka tun rasuwar yar uwarki kuma ƙanwar ki mahaifiyar Ali ko kuma tashin hankali irin wannan dan Allah faɗa min mike faru yawe ya rasu ko ya tayar min da hankalin ki ko waye babu lafiya? wallahi tun safe da natashi naji hankali na ya ƙi kwanciya naso na kiraki kuma mutane suka azazaleni sai na fito mun shiga meeting, haka ba dan hankali na ya kwanta ba na bisu muka shiga meeting sannan kuma ina fito na tarda appelle manque (miss call) ɗin ki kawai sai gabana ya faɗi dan Allah daure faɗa min abinda ke faru kisan hankali na ya ƙara tashi."
Cikin kuka da ta ɗan rage tace "Dady AFREED dama AFREED ne......." Kuma sai kuka ya kwace mata ta kasa ƙarasa abinda tayi niyyar faɗa.
Ai kuwa hankalin dady in yafi dubu to ya tashi jin abin ma saman kan ɗan sa ne gudan jininsa abin kaunar sa, da sauri cikin ɗaga muyar cike da tashin hankali yace "Maman ƴan biyu daure ki faɗa miyasa mi yaro na da kuka boyemin, mike faruwa dashi ne idan kuka yar wani abun ya sameshi dani daku ba zamu shirya ba, kada ki yarda ki faɗa man cewa bashi da rai?"
Hankali momy ya ƙara mugun tashi ganin har mahaifin nasa da take gani zai yi dangana amma ya rikice har haka wai wane irin so ne suke yiwa AFREED haka dan ma Allah yasa basa nunawa sosai da babu san ko AFREED zai iya zama mai wani juyayan hali ba duk da ko yanzu ɗin halin sai a hankali uwa uba miskilanci, kawar da wannan tunanin tayi, lokacin da taji dady AFREED ya daka mata tsawa yana cewa "Ba zaki faɗa min abinda ya sami yarona ba."
Da sauri momy itama cikin dusashewar muyar tace "Dady AFREED wallahi nima ban sani ba ina ganin ciwon sa ne ya tashi nima ina cikin falo nida su Farisa, Ilya direba ya shigo yace man ga Ali cen ya tafi da AFREED asibiti kuma AFREED ɗin baya cikin hankalin sa yana tunanin a some yake lokacin da ya tafi da shima, ba tare da na tsaya ya ƙarasa maganar saba, na shige ɗaki na saɓo hijab ya kawo mu asibitin muna zuwa kuwa har an shiga dashi urgence (emergency) mun tardo Ali a bakin ƙofar ɗakin dayake cikin, nayi masa tambayar duniyar nan ya faɗa abinda ya sami AFREED ya kasa faɗa min sai kuka yake da kair na samu na rarashe sukayi shiru kuma mun kusan awa huɗu anan har yanzu babu likitan da ya fito daga ɗakin ma bare su faɗa mana hali da yake ciki kwata kwata hankali na yaƙin kwanciya na kasa daurewa zuciyata ta ƙarye gani nake zan rasa shine abu shiru haka dan Allah dady AFREED kayi wani abu."
Sai a sannan dady ya sauke wata ajiyar zuciya, ba dan hankali sa ya kwanta ba a'a dan dai shin ke namiji kuma shine babban indan bai kwantar masu da hankali ba ko ya nuna dangana ba to su ya zasuyi, ɗan nisawa dady yayi cikin sanyayar muryar mai kwantar da hankali yace "Ke kina kuka yaranki nayi wa zai bawa wani haƙura a cikin ku gashi kuma ke ce babba idan baki nuna dangana da kawaici ba su ya kike so suyi kuje asibiti kuyita koke koke kamar wasu maras hankali kece babba fah ke zaki basu haƙura ba wai ki biye masu ba ayita kukaba, je ki ƙara kwantar masu da hankali sannan ki rarashesu da ikon Allah, Allah zai tashi ƙafaɗu sa in Allah ya yarda zai sami lafiya, sannan batun inyi wani abun bai taso ba nida bani gari, ke koma a gari nake ba zanja da ikon Allah ba, ba zan iya bashi lafiya ba saidai wanda ya aza mashi shi zai yaye masa wahala nima kuma ina a hanya nan da ƙarfe biyu jirgin mu zai sauka insha Allahu faɗa man wani asibiti kuke dan ina sauka nan zan wucike."
"Clinique HADAMALAH" momy ta faɗa a taƙaice.
Ok ta Dr Inusa kenan ai abokinna ne gayamin number ɗakin da yake zan kira yanzu Dr Inusa na faɗa masa yaje ya duba shi da kanshi kamin na karaso."
Momy tace "Bon ɗakin dayake ciki numéro (number)45 amma idan sun fito dashi za a kaishi ɗaki personnel inda zai huta ba za'a haɗasa da kowa ba yanzu zanje nasa Ali yaje ya biya kuɗin babban ɗaki mai komai da komai a cikin."
"Eh hakanan ya kamata yi sauri ki koma gurin su kin barsu su ɗaya yanzu haka suna cen su na kukan."
Momy tace "To shikenan sai kazo Allah ya kawo ka lafiya."
Da ameen dady ya amsa tare da kashe wayar, dady na kashe kiran momy ta koma wajen su Ali tace "Ya je ya biya kuɗin ɗakin da za'a saka AFREED idan an fito da shi. ba musu Ali ya miƙe ya nufi inda ake biyan kuɗin."
Shiku dady ya na gama waya da momy ya kiran Dr Inusa ya sanar da shi Dr Inusa najin cewa ɗan abokinsa ne kuma a matse yake, yasa shi saurin miƙewa ya kashe kiran dady ba tare da ya bari ya idasa jin abinda dady zai ce ba ya tashi ya nufi ɗakin da AFREED ke ciki su momy na nan zaune saida sukaga muntun ya buɗe ɗaki ya shige suka ƙara baza ido.
Dr Inusa bai fi minti talatin da shiga ba sai gashi ya fito, ida su momy ke zaune ya nufa yace "Madame kune ku ka kawo AFREED Sumana ko naga kama"
Da sauri momy da su Farisa su ka miƙe momy tace "Eh mune."
Dan murmushi ya saki yace "Kun kwantar da hankalin ku biyoni office."
Momy tace "To." Tana ƙoƙarin kiran Ali a waya dan ta faɗa masa cewa ya tardosu office ɗin Dr Inusa.
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
*ZAMBA CIKIN AMINCI*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
Écrit
Par
*QUEEN ZEEFAT*
_Ƴar_
_Mutan_
_Niger_
*Wattpad@nazichou*
💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝
☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️
https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/
*_BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHIM_*
*Page* : 45 & 46
*Wanene DR Inusa*