← Book details Zamba Cikin Aminci Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 60 OF 69

Sashe 60

Zamba Cikin Aminci Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Arahamat da yaran ta kawai ke abinda suke so sabida ta amshe gida yaran ta biyar har maza biyu ke da ɗaya ita kuwa wacen mafaɗaciyar da uku ita kuwa duk mata, kin ga kuwa idan yau Alhaji ya faɗi ya mutu har ƙorarki ana iya yi daga gidan nan dan haka nake so ki samu ki mallaki wasu ƙadarori na Alhaji kamin mai tonan asiri tazo dan kuwa ya na komawa ga mahaliccin sa, wallahi kin banu sabida abinda za'a baki na gadon yarinyar ki da na wankan da zaki masa bai taka ƙara ya karye ba dan a lokacin ne zakiyi dana sani wallahi kin tashi a tutar babu dan ma wai kinada ɗiya da shi da ace baki da kowa wallahi da kin fi banuwa."

"Wallahi haka ne Aunty ai duk sai naga bayan su sai na koma babu wanda ke faɗa aji in bani ba dan ba zanyi tallata ba sai Laraba dan wallahi bani tashi a taulauce kuma na mutu a haka gaskiya il faut que nayi arziki dan zan dinga zuwa Dubaï duk sati nima matan manyan su dama dani ba wai na zauna ina kallon kawai na wasu suna fantamawa ba yanda suke so ba ni banda ni wallahi da sake."

Anty hawa tace "Ah ai dai na faɗa maki tun ba yau nake sanar dake wannan abin kin ƙi ki fahimta kiyi abinda ya dace."

Tanti tace "karki damu anti yanzu dai mu fara maganin wannan matsalar kamin akai da wacen ɗin."

Da sauri Aunty hawa ta tari numfashi ta ce "Ke daka ta ai a bari ya huce shi ke kawo rabon wani duka za'ayi gobe idan Allah ya kaimu ba waje guda ba zamu je, sannan ki kira wannan ƙawar taki ita ma ta raka mu wajen wannan babban bokan na ta, sannan muje wajen wanda ya ke maki aiki nima na san guda uku duka zamu je ayi aiki mai yawa kowa ya yi kalan nashi se ki ga ya yi saurin ci dan wanga karon ko ƙur'ani take zazzage wa a kanta tana kwana da shi dole muyi galaba a kan ta ke dai kawai gobe ki fito da kuɗin isasshi."

"To shikenan anty Allah ya tada mu lafiya."

Ta amsa da ameen sannan suka ajiye waya

Tanti na ajiye wayar ta fara kai kawo cikin ɗakin ta ce yanzu najin sun ce zasu tuntuɓi AFREEN kan maganar idan ta yarda ni zan hure ma ta kunne ince ka ta yadda duk da naga kamar yanzu bata sanki jiki dani, amma zan gwada ko dai ta fara gane shirin da nake a kanta kai ba haka bane indai ba wannan munafuka Khairat kin ce ta fara hure ma ta kunnuwa dan naga ita ba wani yarda tayi dani ba, ko da yake itama zanyi maganin ta zan hana ta zaman lafiya da mijin nata, har sai ya watso ta gida insha Allahu kowa na shirya yanda zanga bayan shi ita fauziya ta daina farin cikin cewa tayi aure har yanzu mijinta bai yi mata kishiya ba zan yi abinda zai ƙara aure kuma irin kishiyar da zata maida ta kamar ƴar aiki za'a mata duka dai zan san yanda za'ayi, ba dai da ni suke ja ba za su sha mamaki duka sai na sa sun gane kurin su, sai na kuntata masu rayuwa kamar yanda yanzu suke cikin farin ciki mu kuma an mayar damu bare ga gida ba matsala zasu gani."

Da safe wajen ƙarfe tara bayan sun gama petite déjeuner (breakfast) 🍳🍜🥗🍱 papa yana dakin sa bai fita ba tanti ta shiga da sallama papa ya amsa mata sannan ta nemi guri ta zauna tace "Papan yara da ma inaso naje gidan Aunty hawa na duba ta kwana biyu bata ji daɗin jikin ta ba shine na ce bari na sanar maka."

Papa da idonsa ke ga télé (TV) ya juwo ya kale ta yace "Asha asha Allah ya bata lafiya kije kawai Allah koro sauƙi, amma ai kinsan bana son za'a fita a ƙi sanar da ni har sai ranar fitar ta zo ko."

Tace "Eh wallahi nasan wannan jiya da dadare ne take sanar dani wallahi shi ne yasa ban sanar da kai da wuri ba."

"To shikenan idan kinje kice ina gaishe ta da jiki."

Tace "Insha Allahu zan sanar mata"

"To shikenan ba damuwa tashi ki shirya kije dan ki samu ki dawo da yuri."

Tanti har ta miƙe zata fita sai papa yace "Karɓi wannan ki sayi ɗan abinda dubiya ki biya mata da shi."

Da sauri tanti ta karɓe 10000 da papa ke miƙo mata kamar yace zai fasa bata idan bata ƙarɓa ba da sauri.

Bata tsaya komai ba ta ga ɗaki, ta nufi nata ɗakin tana shiga ta faɗa toillet tayi wanka ta tayi shirya cikin dogon hijab inta tayi kamar wata ta kwarai ta fice daga gidan.

Maman na zaune ɗakin papa suna hira yace taje ta kira masa AFREEN itama ta dawo dan ayi komai a gaban ta.

Maman ta shi ta fita ta nufi ɗakin AFREEN tana shiga ta tardo ta makale da waya ta na hira da masoyin nata sallama tayi sannan ta idasa shiga ɗakin, AFREEN da ta kashe wayar tunda ta ji sallamar mahaifiyar ta ta ɗago ta kalle tace "Maman barka da warhaka."

"Yawa AFREEN na shigo kina waya ko har kin gama."

"Eh maman dama da fanna muke magana."

"Ok to ta shi mahaifin ki na neman ki."

Dam dam gaban ta ya faɗi bata san dalili ba, idan kiran Mahaifin ta ne ai ta saba dashi tun ba yau ba to miyasa yau taji faɗuwar gaba daga ance yana neman ta.

Ta ɗago tace wa maman gata nan tafe sai kawai taga maman har ta fice daga ɗakin jiki a sanyaye ta sauko daga saman bed 🛏️ ɗin ta ɗauki hijab ɗin ta nufi gun mahaifin ta, tana kaiwa bakin ƙofa ta yi sallama aka amsa ma ta sannan ta murɗa ta shiga kai tsaye duk jikin ta a mace ta nemi gu ta zauna kusa da ƙafafun mahaifiyar ta sannan ta ɗago tace "Papa gani maman tace kana nema na."

"Eh hakane AFREEN ni nace ta kira minke akwai maganar da za muyi dake inaso ki nutsu kiji abinda zan faɗa kin gane ko dan maganar tana da mahimmanci sosai."

Nan ma AFREEN taji gaban ta ya sake faɗuwa sannan ta ce "To papa ina sauraren ka."

Yace "Yawa kinga mahaifiyar ki nan jiya mukayi maganar da 'ita shi ne naga ya dace ke ma a sanar dake, dan haka ba wani abu bane nakeson faɗa maki illa inason faɗa maki cewa na maki miji."

Dam dam gaban ta ya yanke yayi wata irin muguwar faɗuwa ta ɗago da sauri tayi sauke idon cikin na Mahaifin ta suka yi ido huɗu da shi sannan da sauri kuma ta sunne kanta ta na kallon kasa tare da rumtse idonta da ƙarfi ta furta inna lilahi wa inna ilaihi raji'un cikin zuciyar ta.

Papa ba tare da ya lura da hali da AFREEN ta shiga ba ya cigaba da cewa "Yaron ne me hankali da nutsuwa da sanin ya kamata in taƙaice maki dai yaron kirki ne iyayen sa suka nemi na ba shi auren ki ganin dacewar haka yasa na amince masu ba tare da na nemi shawarar ki ba saboda sannan halin yaron da kuma la'akari da nayi da gidan da ya fito gidan tarbiyya, gidan mutunci ne gidan mayan mutane ne ina nufin iyayen sa datawan kware ne haka kuma nasan da za'a riƙe ki da daraja da muntunci saboda mahaifinsa amini na ne tare muke tun muna yara tare mukayi komai har aure da kuma karatu kinga mahaifiyar ki nan itama ta sanshi farin sani dan mahaifiyar yaron ma kawarta ce, amma wani hanzari ba gudu ba, AFREEN ba doli ba ne za'a yi maki zaɓi ne kuma shawara ce idan har kin ga zaki iya auren ɗan amini na idan kuma ba zaki iya ba, babu mai takura ki ko kina da wanda kike so duk babu wata damuwa ni farin cikin ki kawai nakeso ba na wani, idan kin ce baki amince ba, zan iya kiran injiniya in ba sa hakuri kuma na san zai fahimce ni dan haka kina da zaɓi AFREEN ɗin papa gayaman yanda kike so ayi, zanyi farin ciki da duk amsar da zaki ban, kuma gaskiya nakeson ki faɗa man abinda ke cikin ranki kada ki kuskure ki man ƙaya saboda baki saba yin haka da sauri zan gano inda kika dosa."

Cike da tashin hankali AFREEN ta ɗago ta kalli mahaifin nata taga ita yake kallo babu yabo ba fallasa cikin kwanciyar hankali ba ta ga alamun zai yi mata dole ba, kuma haka ta ga alamun ba zai ji haushi duk abinda zai fito daga bakin ta ba, da sauri ta mayar da kanta kasa ta na kallon kafet wani irin bugawa ne zuciyar keyi kamar zata fito waje kuka keson kubce ma ta amma tayi ƙoƙarin mayar dashi saboda idan ta bari kukan ya fito mata zai nunawa papa cewa batayi na'am da zaɓin sa duk da a cikin zuciyar ta hakan ne batason wanda papa ke shirin haɗa ta dashi sabida tana AFREED ɗin shi take so take kauna a cikin zuciyar ta ga halin yanzu duk da basu yi ko wata da haɗuwa ba har yanzu, gashi kuma papa na shirin faraƙa tsakanin su ita ya zatayi dan bai kamata tayi rejeté zaɓin mahaifin ta ba bai komai kawai zata aminci kodan papa ya gama mata komai a rayuwa ko a cikin gidan ya kan take farin ciki kowa da ita tayi farin ciki bai kamata ta yi masa butulci ba gaskiya...

Bata ƙarasa zancen zucin da take ba papa na cewa "Ke nake saurare AFREEN kaki kuskura ki yi ma kanki gashé ɗin farin ciki da ganin kin faranta man dan kuwa ina maraba da duk amsa da zaki bani saboda kinsan ce ta farko a cikin gidan mai min biyayya yanda ya kamata idan aka cire mahaifiyar ki dan gaba ɗaya halayyar kika gado, dan haka ina sauran ki faɗa man duk abinda ke ranki."
Chapter 60 · 0% Book details