← Book details Zamba Cikin Aminci Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 37 OF 69

Sashe 37

Zamba Cikin Aminci Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Fatan alkairi ZAMBA CIKIN AMINCI FANS🥰🥰🥰
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
*ZAMBA CIKIN AMINCI*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸

Écrit

Par

*QUEEN ZEEFAT*

_Ƴar_
_Mutan_
_Niger_

*Wattpad@nazichou*

💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝

☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

*_BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHIM_*

*Page* : 33 & 34

Ali na ganin AFREED ya ƙaraso gun motar yace "Dan Allah AFREED miye haka ka wani zo ka shanyani anan kamar wani kayan wanki tun ɗazu ina nan inata jiranka, tunkuna ma ina kaje kayi zamanka har ka jima haka nidai nasan tare muka fito daga masallaci muna cikin tafiya na waiga ban ganka ba."

Kollon sa AFREED yayi ya sakar masa murmushi kawai sannan ya buɗe motar ya shige, mamaki ne ya cika Ali kamin shima ya buɗe mazaunin direba ya shiga tare da tayar da motar yaja suka tafi.

A hanya sai sakin murmushi yake shi kadai, Ali ya juyo ya kallesa da mamaki yace "Wai AFREED lafiya kake kuwa naga sai sakin murmushi kake kai ɗaya ko wani abun ne ya samu."

Lumshe idonsa yayi tare da sakin ajiyar zuciya sannan ya buɗe su kan Ali yayi fuska kamar ba shine yanzu ya gama sakin murmushi ba sannan yace "Kai Ali sa idonka ya min yawa, toh sai da wani abu zan dinga murmushi ko baka taɓa gani na ina murmushi bane, har kake son damuna da tambayoyi???"

Juwowa Ali yayi ya kallesa kamin ya maida hankali sa ga tuƙi sannan yace "Hum in tayi wari munji."

Shiru AFREED yayi ba tare da ya tanka masa ba, sai lumshe idonsa da ya komayi kamar mai bacci tare da kwantar da kujerar sai ya ɗan gincira har suka kai kida yana a haka kamar mai bacci alhalin bahaka ba ne, kawai ya faɗa duniyar tunanin ta ne.

Suna shiga gidan Ali na gama parking ya buɗe motar ya fice, direct ɓangaren su ya nufa ba tareda yayi ɓangaren tanti Aicha ba, Ali na ganin haka a ransa yace "To mike damunshi ne har haka? sai kuma yace bari naje tanti taga dawowar mu sai naje na tambaye shi ko mike damunsa."

Yana shiga falon babu kowa, sai Khadijah ita kuwa tana jin ƙarar buɗe ƙofar ta ɗago dan ganin ko waye ya shigo aiko sai idanuwansu suka sarƙe cikin juna, murmushi Ali ya sakar mata yanajin wanda soyayyarta ke ƙara shigar sa, a zuciyarsa yace "Yakamata na fito na faɗa mata abinda ke raina kada wajan kallon ruwa kwalo ya mani ƙafa, idan haka ta faru kuwa bansan ya zanyi ba, sabida ba ƙaramin so nake mata ba."

Ƙarasawa yayi gun datake zaune shima zama yayi kan kujerar dake kallon tata, ita kuwa tun shigowar sa da suka haɗa ido tayi saurin duƙe kanta ƙasa bata sake ɗagowa ba har yazo ya zauna sannan tace cikin siririyar muryar ta "Yaya ina wuni, barka da juma'a." Ta faɗa ba tare da ta ɗago ba.

Kallon ta yake yana murmushi batare da ya amsa ba, jin shiru yasa ta ɗago dan taka ko bai jita bane, aiko sai take idanunta suka sauka cikin nashi, dam dam gabanta ya faɗi, da sauri ta ɗauke idanunta daga nashi tare da duƙe kanta, a zuciyarta tana cewa "ko dai yaya Ali ya naji abinda nakeji game da shine idan ko haka ne da naji daɗi."

Bata ƙarasa tunanin ta ta tsintsi muryar nacewa "Khadijah zaki iya aure wani garin ki bar maraɗi?"

Kamar daga sama taji tambayar tashi da sauri ta ɗago ta kalleshi suna haɗa ido ta sune kanta ba tareda tace komai ba amma cikin zuciyarta ta sai tace "Mizai hana yaya idai kaine mijin zan iya barin maraɗi na zauna duk ida kake, wani ɓangaren na zuciyarta yace kenan zakiyi iya tafiya ki bar mamanki da dadyn ki?" Atake kuma jikinta yayi sanhi.

Ali ya ɗan nunfasa yace "Khadijah tambayar yaki nake, ko bakiji minace ba?"

Cikin bugun zuciya ta buɗe bakinta ta ce "Ta ni yaya banda zaɓin kaina sai na Allah, idan Allah ya tsaro rayuwa ta akan zan bar garin nan ta dalilin aure to j'ai pas la choix, Ubangiji shi ne yasan daidai, kuma shine kan daidai ni ina farin ciki da duk inda Allah ya ajiye ni."

Wata ɓoyaya ajiyar zuciya Ali ya sauke sannan yace "Alhamdulilah hakane kuma ƙanwata kinada gaskiya to bani labarin samarin dan ni tunda mukazo nan ban taɓa ganin kinyi fira ba ko miyasa, ai yakamata ace yanzu aure za'ayi maki dan kam yanzu kin girma."

"Lah yaya saurayi kuma ni yaya banida wani saurayi dady bai barin mu kula samari kuma ni banda wannan ma duk a nawa nike da zan fara wani kula samari," Khadijah ta faɗa cikin shagwaɓar da ba tasan tayi ba.

Shagwaɓar da tayi ba ƙaramin tafiyar masa da imani tayi ba, a zuciyarsa wani farin ciki ne ya luɓeɓe sa jin cewa babu wanda yayi masa rigagin shiga zuciyarta, dan haka yanzu yanzu ba sai anjima ba zaiyi mata bayanin abinda kecin ransa, gyaran murya yayi ya ƙara gyara zaman sa tare da maida hankalinsa sosai akanta yace "Ƙanwata kinason na zaki aure ni."

Duk da abinda Khadijah keson jine ya fito daga bakinsa, sabida son da take masa amma haka bai hana gabanta faɗuwa ba, cikin sauri ta ɗago da niyar satar kallon sa aiko se idanunsu suka sarƙe cikin juna, da gudu ta tashi ta nufi sama tana murmushi direct dakin su ta nufa.

Shikuwa Ali baiyi ƙoƙarin tsayar da itaba sabida yasan dole zai bata lokaci tayi tunani, amma sosai ya cika da farin ciki sabida ganin hakan ma da tayi ya nuna masa ta amince da tayinsa, a fili ya furta "Alhamdulilah yaudai na faɗa mata Allah na gode da kabani ƙaurin gwiwar bai yana abinda ke raina." Murmushi ya saki tareda tashi ya bar gun shima ya nufi ɓangaren su.

Khadija na shiga ɗaki ta tardo Fariya da Farisa zaune saman gado suna fira suna dariya kana ganin su zaka gane cewa firar da suke suna jin daɗin ta, da gudu tayi wajen su ta faɗa tsakansu tare da rungume su tana dariya, kamin ta ɗan sassauta rungumar da ta masu tana kallon ɗaya bayan ɗaya, suma ita suke kallon cike da mamakin miyasa ta farin ciki haka, dan daga ganin yanayin aikasan tana cikin farin ciki mara misali, ganin mamaki ta suke kuma sun kasa cewa komai, kawai sai tajuyo ta sakesu baki ɗaya ta zaune tsakiyar su sannan tace "Sisters albishirin ku," Khadijah ta faɗa tana murmushi.

Haɗa baki sukayi da sauri wajen cewa "Goro" cike da zaƙuwar jin wane albishirin ne tazo masu dashi.

Sai ta ce "Fari ko ja?"

A tare suke cewa "Fari tass sœurette dan Allah yi sauri ki faɗa mana har mun ƙagu muji ko miye."

Tsalle tayi ta sauka daga saman gadon ta juyo ta na fuskantar su har yanzu dai murmushi ɗoke a fuskarta tace "Yaya Ali ya tambaye ina son shi zan auresh...... bata ƙarasa faɗar abinda tayi niyar faɗa ba sukayi tsalle suka sauka daga gadon tare da yowa kanta suka rungume ta su duka biyu har suna dariya da murnar jin wannan labarin har saida suka kai ƙasa da tsanani farin ciki da rungumar da suka ma juna, na saman kafet ɗin dake ɗakin suka faɗa tare dayin zama dirshan suna maida numfashin murna.

Fariya ce tayi ƙarfin halin buɗe bakinta dan sun kasa ma yi magana dan tsanin farin ciki tace "Wayo Allah sœurette Khadijah zata koma Niamey da zama zatayi aure garin mu tana yiyuwa ma a kusan gida zaku zauna ko a gidan mu ɗin dama ba tun yau nakeso kikoma gidan mu ba amma na kasa samun hayar da zaki koma ɗin, yanzu dai gashi yaya zai mayar mana dake weeeeeee tayi ihu mara sauti sosai tare da daka tsalle farin ciki sannan ta koma ta zauna da murmushi kwance a fuskar ta tace "Alhamdulilah."

Ita kuwa Farisa sai ta kamo hannuta na dama da duk hannayenta tace "Anty Khadijah to ke mi kikace ma yaya da yace maki hakanan injin dai kin amince?"

Murmushi tasaki tace "Ah har na koma antyn kenan, ashe duk zakuyi farin cikin hakan, kenan kuma kuna so na auri yaya Ali, kun san mi nima sosai na faɗa soyayyarsa a zuciyata amma ai kunsan da haka dan ba tun yau nake faɗa cewa ina son ba amma na kasa faɗa masa sai gashi shi da kansa ya furtamin hakan, amma ni bance masa komai ba yana min tambayar na ji kunya na gudo ɗakin ban tsaya ba."

Fariya tace "Ina ai dole ne ki koma anty tun yanzu, kuma hakan da kikayi shine daidai dama ba daga mutum ya faɗi yana sonka ba kake ce masa ka amince ba, hakan da kikayi ya nuna masa da amincewar taki yanzu kawai ya kamata tanti A'isha taji wannan dadaɗan labarin, dan a faɗa ma dady sai a saka ranar auren nan da yuri kokuwa Farisa?" Fariya ta tambayi Farisa tare da kallon ɓangaren da take zaune Farisa tayi saurin ɗaga kanta alamar eh ta na murmushi.

"Ah kijimin Sisters ɗin nan kawai daga magana kuma sai shirya aure ai kun bari har mu ƙarasa daidaitawa kamin akai maganar ga manya mana, wannan sauri haka kamar dai kune angon."

Murmushi sukayi sannan Farisa tace "Ah to mi za'a jira? Batun daidaitawa kuma ai kun riga da gun daidaita tunda kun daɗe da soyayyar juna a cikin zuciyar ku dan nasan yaya Ali ba tun yau bashi ma yake sonki baide faɗa ba ne dan haka mu alkairin abin kawai muke nema."

Fariya tace "Lale dai kama Allah sanya alkairi kawai zamuce yanzu ku tashi muje mu ci abinci sai mu dawo mu zauna mu fara tsara yanda bikin nan zai ƙayatar da yardar Allah."

Da ameen suka amsa sannan suka miƙe suka fita a ɗakin.

*****. ******. ******. ******

Ali na shiga ɓangaren su ɗakin AFREED ya nufa, tardo shi yayi kwance ya lumshe lumsashin idanunsa kamar mai bacci da murmushi kwance a fuskar sa, ba tareda yaji shigowar Ali ba sabida faɗa wa da yayi duniyar tunanin, saida Ali yace "frèro waini yau wane irin farin ciki ne kake ciki haka da kakasa sanarmin ne har yaushe ka fara ɓoyemin abinda ke damun ka?"
Chapter 37 · 0% Book details