← Book details Zamba Cikin Aminci Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 50 OF 69

Sashe 50

Zamba Cikin Aminci Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Cikin zolaya dady yace "Oh ni ƴan biyun Momy su zasu kayar dani ban san ranar da zasu girma ba su daina rigima da shagwaɓa, tunda sun girma sun ƙi yarda da hakan gashi yanzu suna shirin karya ni daga dawowa na."

Sakin sa sukayi suna dariya tare dan toro baki gaba suna ɗan bubuga ƙafafun su a ƙasa cikin shagwaɓa suka ce a tare "Gaskiya mu kam papa bamu girma ba har yanzu yan pici pici muke."

Gaba ɗaya ɗakin suka kwashe da dariya Dr Inusa yace "Kai lale ƴan biyu akwai rigima irin wannan shagwaɓa haka, da sauri suka koma mazaunin su suka zauna suna rufe fuska da murmushi kwance a fuskar su wai su sunji kunya.

Dariya duka ɗakin suka komayi sannan doctor ya koma cewa "Haka nake da su kai kasan cewa ma ƴan matan ne ke shagwaɓaɓi ni har ƴan mazan haka suke da girmansu gwaɗe gwaɗe basu jin kunya haka suke zama suyi ta zuba min shagwaɓa."

Dariya sukayi sannan dady ce "Yaran ne namu na yanzu duk sangartaci ne gata ya masu yawa, har wannan mara lafiyar wata ran haka yake Ali ne kaɗai ya nuna ya girma amma shima ba kullum ba idan ka tarda su suna yiwa mahaifiyar nan tasu shagwaɓa zaka ce wasu ƙananun yara baiwar Allah ai tana fama dasu ta iya ɗaukar rigimar kowa a cikin ni har tausayin ta nake idan suka mamaye ta suna mata rigima ba babba ba yaro kuma kamar haɗin kai lokaci guda suke aza tabara su ka dai gansu."

'To Allah dai ya raya ma musu cikin koyi da addinin musuluncin nikam duk sun fi takura man kan mahaifiyar tasu inda ina gari ta kullum suna liƙe da ni suna min taɓara ba kamar yanda mahaifiyar zasu mata ba su mata shagwaɓa kamar yanda suke ko fa bani ƙasar zakaga sun kirani suna ta zuba min shirme, ita mahaifiyar tasu kaga AFREEN ɗiyar ƴar uwar ta wato matar Alhaji Sadisu, idan kaga tana zuba mata shagwaɓa tana biye mata kamar wata ƴar jinjira sosai suka shaku da ita kamar zata mayar da ita ciki har dariya suke ban idan suna appelle video ita da ita suna shirmen su kwani ban dariya."

Lokacin da doctor ya faɗi sunan AFREEN sedai AFREED dake kwana yaji wani irin faɗuwar gaba dan har cikin baccin sa yaji an faɗi sunanta har sai da ya ɗan motsa ƙafar sa da hannu sa na dama amma ba wanda ya lura.

Dady yace "Hakane dama wata soyayyar Allah ke haɗa ta, ni kamayi batun Alhaji Sadisu ka tuno man da auren ɗiyar sa nan da sati ɗaya ban san ko ka sani ba?"

Dr Inusa yace eh na sani ya faɗaman shi yasa ma har yanzu banje Maraɗi ba so nake nayi tafiya guda da ta zuwa ɗaurin aure da sabida aiki, kuma madame ta kirani ta ce tana son zuwa hidimar bikin nace ta bari har ƴar lelan ta AFREEN za tayi aure sai su taho su duka a lokacin Inayah tayi nisa da karatu shi Aban ya riga da ya ƙarasa har ya fara aiki Fujai ne dai bai fara aiki ba tukuna sauran wata bakwai ya ƙarasa karatu sa ka kenan sai su zo tare baki ɗaya."

"To madala Allah masu albarka idan bikin ya tashi sai kamin magana mu tafi tare har da maman ƴan biyu za muje tare insha Allahu da ƴan biyun ma idan zasu je, ya jikin yaron naka." Dady ya ta tambayi doctor."

Dr Inusa yace "Ah jikin sa da sauƙi sosai nan da awa ɗaya zai farka insha Allahu tunda yanzu ya samu baccin kusan awa ɗaya."

"To madala Allah tashi kafaɗun sa." Inji dady

Nan doctor ya masu sallama ya fita dan ya barsu su gana da iyalansa, dady yace masa ya iskoshi office ɗin sa suyi fira yaushe gamo.

Doctor na fita dady ya isa kusan gadon AFREED ya ke kwance ya ɗan kamo hannu sa ya yayi masa kiss sannan ya shiga jero masa addu'oi, da ya gama ya nufi wajen matar sa ta kallesa da murmushi tayi masa sannu da zuwa sannan tace "Dady AFREED kaje direba ya mayar da kai gida kayi wanka sai ka kwanta ka huta tunda mu gamu a wajen AFREED ɗin kuma doctor yace da sauƙi sosai."

Dady yace "To shikenan madame in haka kike so ai shikenan."

Bai ƙarasa rufe bakinsa ba Ali ya ce momy da kema tare da dady kuka tafi gida da su Fariya sai ni na zauna da shi kamin ya farka sai su Fariya su yi masa girki su taho da shi ko."

Ba karamin daɗi dady yaji ba da yaji furucin Ali dan sosai ya keda buƙatar matar sa a kusa da shi tunda dai jinkin AFREED ɗin da sauƙi gara su tafi gida shi ta kula da shi, dan haka sai yayi saurin cewa "Eh to haka za ayi ku tashi mu tafi."

Ba musu suka miƙe suka fita tare da cema Ali sai sun dawo, shima Ali ya faɗi hakane saboda ya san dady yanzu ya dawo da gajiya ya na bukatar kulawar momy."

Suna fita ya koma kusa da AFREED ya zauna yayi tagumi yana kallon sa yan jiran farkawarsa,

Bayan awa ɗaya

KU BIYO NI DAN MI ZAI FARU

TA KU HAR KULLUM MAI KAUNAR KU

🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
*ZAMBA CIKIN AMINCI*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸

Écrit

Par

*QUEEN ZEEFAT*

_Ƴar_
_Mutan_
_Niger_

*Wattpad@nazichou*

💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝
☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

*_BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHIM_*

*Page* : 45 & 46

Suna fita ya koma kusa da AFREED ya zauna yayi tagumi yana kallon sa yana jiran farkawarsa.

Bayan awa ɗaya shiru AFREED bai farka ba kuma bai motsa koda hannun sa ba bare ayi tunanin zai farka, haka wata awa gudar tazo ta wuce shiru, Ali na zaune wajen awa biyu yana jiran farkawar sa amma babu ko alamun zai farka, bayan awa biyu da minti ishirin hankali Ali in ya yi dubu to ya tashi ganin har yanzu AFREED bai farka ba, shida ake ce ma sa nan da awa ɗaya zai farka amma har yanzu shiru, hakan yasa shi miƙewa da sauri ya tashi ya fita bai tsaya ko ina ba sai office ɗin Dr Inusa, amma sai yayi rinshin sa'a baya nan da sauri ya fito yana ƙoƙarin kiransa sai ga wata infirmière (nurse) ta fito daga wani ɗaki, kawai sai Ali ya tare ta yana tambayar ta dan Allah bata ga inda Dr Inusa ya shiga ba?"

Nurse din tace "Ai yana block opération (ɗakin tiyata)."

Ali da zufah ta Kariki ke masa yace "Tun yaushe yashi ga"

"Ya kai awa biyu da shiga dan ina saran nan ba da jimawa ba zai iya fitowa."

"Kamar nan da minti nawa kike ganin zai fito?"

To wallahi ban sani ba, inaga dai ba zai wuce minti talatin ba zuwa arba'in zai fito."

"Kai har minti talatin gaskiya yayi yawa ɗan uwana nacen cikin wani hali, dan doctor yace sai nan da awa ɗaya zai farka amma har ya haura awa ɗaya da minti talatin da biyar shiruko motsi baiyi ba, dan Allah muje ki du bashi ki gani idan kuwa akwai wani doctor dai zai duba shi kamin Dr Inusa ya fito to muje ki masa magana."

Infirmière ɗin mai kirki, gani hali da Ali ya shiga dalilin ɗan uwan sa tace " Eh akwai muje na kaika office ɗin sa sai kama sa bayani."

Suna kaiwa bakin ƙofar doctor kin sai nuser ɗin tace masa ka shiga da ga ciki ka sanar mashi, ni gaba zan ƙara akwai masu jirana."

Godiya yayi mata sannan ya kama hannun ƙofar office ɗin Dr da ta kawo shi, kawai kamar ance ya juya sai ya tsikayi Dr Inusa na tafowa ai da sauri ya saki ƙofar ya nufe sa ya faɗa masa cewa AFREED ya ƙi farfaɗowa."

Bata tare da ya ƙarasa jin bayani Ali ya shige ɗakin da AFREED ke kwance a ciki dama sun kawo bakin kofar ɗakin.

Suna shiga ɗakin suka tardo AFREED zaune da ƴan biyu a kusa dashi suna jero masa sannu da sauri Ali ya ƙarasa kusa dashi yace "Kai ɗan uwa yaushe ka farka ina can hakalina ya tashi da naga baka farka, yanzu ina kema ciwo?" Ali ya faɗa yana ta taɓa shi, da ido kawai AFREED ya bishi bai ce masa komai.

Dr ya ƙaraso inda suke yana mai sannu da murmushi a fuskar sa sannan yace "Minista ya ƙarfin jikin?"

AFREED ya ɗaga idonsa ya duba shi sannan yace "Da sauƙi."

Doctor yace "To madala yanzu ina kema maka ciwo sannan kuma mi kake ji?"

AFREED yayi shiru bai ce komai ba saida Dr ya ƙara mai maitata masa tambayar sannan a matuƙar gajiye da magana yace "Alhamdulilah babu inda ke mani ciwo dady."

"To masha Allah tashi kaje cikin douche ka wanko bakinka sai kazo ka ci abinci da ɗan thé (tea) sai kasha magungunan ka."

Ba musu AFREED ya miƙe ya nufi douche (toillet) yana kaiwa baƙin kofa yayi tagata zai faɗi da gudu Ali ya yi wajen sa ya riko sa yace "Yi sannu man AFREED kada ka faɗi in ba zaka iya ba sai kace na rakoka ba da fa yanzu ka faɗi kuma sai ka ƙara tayar mana da hankali dan Allah kabi a hankali."

AFREED dai baice masa komai ba ya buɗe ƙofar douche ɗin ya shige, bai jima ba ya fito ya na tafiya ya na dafa bango sabida jiri yake gani Ali yaje ya riƙo shi suka dawo bakin gado ya zauna.

Fariya ta haɗa masa tea mai kauri da zafi kamshi sai tashi yake, ta miƙo masa ba musu ya ƙarɓa sabida yunwa ya keji sosai. Cikin ƙaƙanan lokacin ya kammala sannan ta zubasa tuwon shinkafa da biyar kuɓewa ɗanya ta ji kifi da man shanu, nan ma bai musa ba ya ƙarba ya sabida abincinsa ne wanda ya fi so, bai ci wani da yawa ba ya ajiye, Ali na ganin haka yace "Dan Allah AFREED ka ƙara mana regarde tu n'as pas beaucoup mangé (bakaci sosai ba)."

Da kyar AFREED ya buɗe bakin kamar mai raɗa yace "Na ƙoshi."
Chapter 50 · 0% Book details