Sashe 84
Ga Irinta Nan Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Zaune na mike a sanyaye nace." Khalid ka dawo ashe."? a dakile yace." Na dawo ina fatan kuna lafiya."? Nace." Lafiya kalau Ya hanya."? shuru yayi min kawai ya zuba min ido." Nace." Kana bukatar wanka na had'a maka ruwa."?
"A'a idan ina bukata zan shiga na had'a da kaina yanzu inaso nayi magana dake ne." Yanda yake magana a harzu'ke yasa na gane cewa lallai da tashin hankali ya shigo gidan.
*103*
A nutse nace."To Allah yasa alkairi ne ina sauraranka." Cikin sigar tuhuma yace."Har yanzu akwai sauran alaqa a tsakanin ki da Alhaji Nura ko."? Gabana yayi wani irin fad'uwa! Ido na tsira masa raina idan yayi dubu ya 'baci nace."Khalid wace irin magana ce wannan."?
Hannu ya d'aga min "Kinga tambayarki nayi yana da kyau ki bani amsa ba ki tambaye ni ba." Ajiyar zuciya na sauke tare da bawa zuciyata hakuri nace."Tunda nayi aure alaqa ta yanke a tsakanimu.''
"To mai yasa yake bibiyarki har yanzu."? Kallonsa nayi duk ya tsareni da ido Nace." A'ina zan ganshi da har zai bini."
Tsaki yaja cikin tsananin kishi yace."Yau yaje can Mandawari ya samu Kawu yana cin mutuncinsa har da fad'in ba ayi masa adalci ba kin san Allah wannan mutumin yana cin darajar abu guda ne da ba don haka ba da tuni na dauki mataki mai tsauri a kansa sabida haka ki fad'a masa cewa komai maitar sa dole ya hakura dake idan kuma yaqi zai k'are rayuwarsa a prison."
"Ka daina wannan maganar Khalid yanzu ni a ina zan sameshi har na fad'a masa sa'kon ka a kansa don Allah ka rage kishi ba abune mai kyau ba.''
" Wannan abun da nake ba kishi bane gyara ne na lura dake dashi baku da Ilimin addini ba kusan menene hakkin aure ba shiyasa kuke abinda kuka ga dama to ke d'in ma tsatstsauran mataki zan dauka a kanki mutukar baki daidaita sahun ki ba."
"Khalid ni kake kira da suna jahila har kana fadin ban san hakkin aure ba har yaushe aka haife ka? yaushe kazo duniyar da zaka dinga yi wa mutune rashin kunya ko ka manta cewa a gabana aka haife k..........Kafin ta 'kara maganar ya kifa mata lafiyayyan mari! yana wani irin huci yace." Kada ki kuskura kice zaki min wannan haukan! ranki ne zai 'baci wallahi ina ruwana da wani shekarun ki duk girman ki a k'arkashina kike dole kibi umarnina idan ba haka ba ki fuskanci bacin raina."
Yana gama maganar ya bar gurin yana numfarfashi na bacin rai.
Hannu dafe da fuska na bishi da kallo har ya bude kofar toilet din ya shige.
Wasu hawaye masu tsananin zafi ne suka tsinke min wai yau yaron nan ni yake mari ikon Allah! wani abu mai nauyi ne yazo ya tsaya min a makogwaro shin wai menene mafita? ta yaya zan daidaita alaka ta dashi wai shin gabad'aya haka halin maza yake? babu shakka idan duk haka halinsu yake dole aure ya dinga saurin mutuwa babu uziri a cikin al'amuransu duk mazan data aura hakan suke da irin wannan halin.
Ina jin motsin fitowarsa nayi saurin Kwanciya ido na rintse ina nanata kalmar innalillahi wa'ina ilahi raji'un a cikin zuciyata.......Ina jinsa ya gama shirye-shiryen sa yazo ya kwanta gefe na amma ko da wasa baiyi kuskuran ta'ba wani sashe na jiki na ba......Cikin mintinan da basu wuce goma ba naji saukar numfashinsa bacci har ya daukeshi, ajiyar zuciya na sauke a hankali na lalla'ba na sauka daga gadon toilet na nufa domin daura alwala Nafila zanyi domin na kaiwa Allah kuka na.''
Alhaji Nura kuwa tsabar tension ya sanya sitiyarin mota ya k'wace daga hannunsa a take motar ta dinga walagigi a kan titi abinka da daran sanyi sahun mutane ya dauke sai jefi-jefi Cikin tashin hankali ya dinga kokarin kashe motar domin ta tsaya abun yaci tura sai kawai ya shiga kalmar shahada Mussaman daya hango wata katuwar akori kura cike da katako tayo kansa. hannu na karkarwa ya fara kokarin bude motar domun ya fita daga ciki sai kawai yaji motar ta hantsila dashi 'kasa......"Innalillahi wa'ina ilaihi raji'un." A take motar tashi ta fara hayaki wuta na kokarin tashi, hayaniyar jama'a ya dinga ji sama-sama a kunnenshi ya dinga kiran sunan Allah yana kalmar shahada wutar ce ta tashi a daidai lokacin da jama'a ke kokarin taimakon sa ganin haka yasa kowa ya watse daga gurin wuta ta tashi a motarsa da motar katakon da suka had'u. da kyar 'yan a gaji suka samu nasarar kashe wutar gurin ya turnuke da haya'ki Alhaji Nura k'urmus aka fito dashi duk wani mai imani idan ya ganshi sai ya zubar da hawaye Allah sarki duniya ashe dama Alhaji Nura daf yake da barin duniya babu wanda ya san gaibu sai Allah....Labarin mutuwarsa ya zagaye garin Kano saboda shi din sanannan mutum wanda duk mutumin da yake shiga kasuwar Kwari ya san da zaman shi Abokan kasuwancin sa suka shiga alhini da damuwa.
Gwaggo kuwa kuka ta dinga yi tana fad'in "Allah Sarki Alhaji Nura Allah ya jikan ka mutumin arziki babu kai babu shiga wutar jahannama Allah ya jikan ka ya kar'bi shahadar ka." Rigima tasa akan lallai sai Kawu ya shirya ya kaita gidan mutuwar domin ayi jana'iza da ita.
Kawu da yake shima a cikin alhini yake bai mata gardama ba ta shirya ya d'auketa a motarsa domin zuwa gidan jana'izar DUNIYA KENAN ALLAH KASA MU CIKA DA KYAU DA IMANI.
Koda Khalid yazo gidan Ummatu ke sheda masa mutuwar jikinsa ne yayi sanyi damuwa da nadama suka baibayeshi ashe ma dik wannan hargitsin mutumin saura kad'an ya mutu kai gaskiya al'amarin ya girgiza shi mutuka, adduar samun rahamar Allah yayi masa yayi mata sallama domin tafiya harkokinsa.
To koda ya dawo da daddara kasa fad'a mata mutuwar yayi ya dai sassauta fuskarsa Sa'i da lokaci kuma yana satar kallonta da tunanin yanda zaiyi ya fad'a mata mutuwar mutumin.
Washe gari da safe yana shiryawa na shiga dakin cikin rashin kuzari nace." Amma Zaka tsaya kayi break fast ko."? Ya kalleta da fadin." Ba zanci abu mai nauyi ba don bana so jikina ya mutu za muyi wasa da abokaina sai dai idan na dawo.
Nace."Ai ko tea kasha ka gasa cikin ka ko." Yace." To shikkenan muje ki had'a min.'' Gaba nayi ya biyo bayana, tea din na had'a masa ya dauka yana sha yana kallona ni kam gabad'aya jikina a mace yake na rasa abinda yake damuna.
"Kina da labarin mutuwar.....Kasa 'karasawa yayi kawai ya zuba min ido.
Cikin fad'uwar gaba nace." Mutuwa waye ya mutu."?
Sunkuyar da kansa yayi yana motsa tea din gabansa yace." Sai hakuri dukkanin mai rai mamaci ne Alhaji Nura ya rigamu gidan gaskiya kwana biyu da suka wuce."
Wani irin kallo nake masa kafin wasu zafafan hawaye su wanke min fuska nace." Yanzu Alhaji Nura ya mutu har anyi kwana biyu amma a rasa wanda zai fad'a min."
Haushi ta bashi ganin tana kuka, sai kawai yaja bakinsa yayi shuru ya cigaba da kur'bar tea d'insa.
"Khalid me yasa kasan da mutuwar baka fad'a mun ba ashe shiyasa kwana biyu gabad'aya na rasa abinda ke damuna Allah Sarki Alhaji Nura ya mutu ya bar wannan duniyar mai cike da rud'ani."
Ya kalleta da fad'in." Wannan kukan dai da kike bashi da fa'ida addua zaki masa idan kuma zaki bishi lahirar dama hanya a bud'e take."
Cikin hawaye tace." Eh idan lokaci na yayi dole na tafi ko inaso ko bana so babu wanda zai zauna ya dawwama a duniya can ne gidan gaskiya sabida haka dik wanda ya dauki zafi da duniya to gwara ya sauke domin ba matabbata bace."
'Bata rai yayi yace." Sa'ida maganar nan ta isa haka bana bukatar ta." Miqewa nayi na bashi gurun, ina jin sanda yake jan dogon tsaki a kaina.
Bayan Kwana uku da faruwar al'amarin Hauwwa har gida tazo tayi min gaisuwa muka jima muna jajanta al'amarin yanda take bani labarin irin mutuwar da yayi yasa na dinga zubar da hawaye nace." Hauwwa aini gabadaya Khalid bai fada min ba yace kawai ya mutu amma bece dani accident yayi ba."
Tace." Aikuwa yana da kyau kije gaisuwa domin a ranar da mukaje gaisuwa da jama'ar gidanmu Mahaifiyarsa da matarsa Murja sai tambayarki suke."
Nace."Allah Sarki Insha Allahu zanje nai musu gaisuwa Hauwwa amma bana tsammanin har ya mutu da aure a tsakaninsa da Murja kin san tunda asirinta ya tuno shikkenan suka rabu."
Hauwwa tace." Allah sarki amma ba kiga yanda ta shiga damuwa ba ni dai har muka fito daga gidan bata daina kuka ba.''
Nace."Hauwwa ai dole aunty Murja tayi kuka Uban 'ya'yanta ne fa kuma ta cutar dashi sosai ta yaudareshi ya dauki amana da yarda ya bata amma ta zalince shi take masa fasikanci a gida."
Hauwwa tace." To Allah ya shiryeta yasa mutuwar tasa ta zama silar shiryuwarta Allah kuma ya raya abin da ya bari."
Hawaye na share da fad'in." Ameeen ameeen Ya Allah."
Mun jima tare da Hauwwa muna hira nan take bani labarin tsakaninta da Yaya Aminu sun fahimci juna sosai amma kuma tana jin tsoron auransa saboda kada ya kasa biya mata bukata.
Kwantar mata da hankali nayi nace." Hauwwa insha Allahu ba zaki samu matsala ba domin kuwa ina ji a jikina cewar Yaya Aminu ya samu lafiya saboda haka ki aureshi da kyakykyawar manufa."
Tace."To shikkenan Sa'ida ki taya ni da addua akan al'amarin." Nace."Insha Allahu zan miki addua Hauwwa Allah ya baku zaman lafiya."
Ta amsa da "Ameen ya Allah 'kawata."
Duk da nasan ba a gurina yake ba sai da na zauna zaman jiran shigowarsa domin sheda masa uziri na na zuwa gidan gaisuwar Alhaji Nura, to har wajen goma da Rabi na dare ina zaune a falo bai shigo ba mikewa nayi na nufi bakin window domin na duba naga ya dawo ko kuwa wani sa'in haka yake yi ko ya dawo baya shigowa yayi min sallama sai da safe idan zai fita, duka motocinsa suna nan alamu ya nuna ya jima da dawowa, girgiza kaina kawai nayi na saki labulan window din daki na nufa domin na kwanta na samu nutsuwa amma a zahirin gaskiya al'amarin yaron ya soma isa ta.
"A'a idan ina bukata zan shiga na had'a da kaina yanzu inaso nayi magana dake ne." Yanda yake magana a harzu'ke yasa na gane cewa lallai da tashin hankali ya shigo gidan.
*103*
A nutse nace."To Allah yasa alkairi ne ina sauraranka." Cikin sigar tuhuma yace."Har yanzu akwai sauran alaqa a tsakanin ki da Alhaji Nura ko."? Gabana yayi wani irin fad'uwa! Ido na tsira masa raina idan yayi dubu ya 'baci nace."Khalid wace irin magana ce wannan."?
Hannu ya d'aga min "Kinga tambayarki nayi yana da kyau ki bani amsa ba ki tambaye ni ba." Ajiyar zuciya na sauke tare da bawa zuciyata hakuri nace."Tunda nayi aure alaqa ta yanke a tsakanimu.''
"To mai yasa yake bibiyarki har yanzu."? Kallonsa nayi duk ya tsareni da ido Nace." A'ina zan ganshi da har zai bini."
Tsaki yaja cikin tsananin kishi yace."Yau yaje can Mandawari ya samu Kawu yana cin mutuncinsa har da fad'in ba ayi masa adalci ba kin san Allah wannan mutumin yana cin darajar abu guda ne da ba don haka ba da tuni na dauki mataki mai tsauri a kansa sabida haka ki fad'a masa cewa komai maitar sa dole ya hakura dake idan kuma yaqi zai k'are rayuwarsa a prison."
"Ka daina wannan maganar Khalid yanzu ni a ina zan sameshi har na fad'a masa sa'kon ka a kansa don Allah ka rage kishi ba abune mai kyau ba.''
" Wannan abun da nake ba kishi bane gyara ne na lura dake dashi baku da Ilimin addini ba kusan menene hakkin aure ba shiyasa kuke abinda kuka ga dama to ke d'in ma tsatstsauran mataki zan dauka a kanki mutukar baki daidaita sahun ki ba."
"Khalid ni kake kira da suna jahila har kana fadin ban san hakkin aure ba har yaushe aka haife ka? yaushe kazo duniyar da zaka dinga yi wa mutune rashin kunya ko ka manta cewa a gabana aka haife k..........Kafin ta 'kara maganar ya kifa mata lafiyayyan mari! yana wani irin huci yace." Kada ki kuskura kice zaki min wannan haukan! ranki ne zai 'baci wallahi ina ruwana da wani shekarun ki duk girman ki a k'arkashina kike dole kibi umarnina idan ba haka ba ki fuskanci bacin raina."
Yana gama maganar ya bar gurin yana numfarfashi na bacin rai.
Hannu dafe da fuska na bishi da kallo har ya bude kofar toilet din ya shige.
Wasu hawaye masu tsananin zafi ne suka tsinke min wai yau yaron nan ni yake mari ikon Allah! wani abu mai nauyi ne yazo ya tsaya min a makogwaro shin wai menene mafita? ta yaya zan daidaita alaka ta dashi wai shin gabad'aya haka halin maza yake? babu shakka idan duk haka halinsu yake dole aure ya dinga saurin mutuwa babu uziri a cikin al'amuransu duk mazan data aura hakan suke da irin wannan halin.
Ina jin motsin fitowarsa nayi saurin Kwanciya ido na rintse ina nanata kalmar innalillahi wa'ina ilahi raji'un a cikin zuciyata.......Ina jinsa ya gama shirye-shiryen sa yazo ya kwanta gefe na amma ko da wasa baiyi kuskuran ta'ba wani sashe na jiki na ba......Cikin mintinan da basu wuce goma ba naji saukar numfashinsa bacci har ya daukeshi, ajiyar zuciya na sauke a hankali na lalla'ba na sauka daga gadon toilet na nufa domin daura alwala Nafila zanyi domin na kaiwa Allah kuka na.''
Alhaji Nura kuwa tsabar tension ya sanya sitiyarin mota ya k'wace daga hannunsa a take motar ta dinga walagigi a kan titi abinka da daran sanyi sahun mutane ya dauke sai jefi-jefi Cikin tashin hankali ya dinga kokarin kashe motar domin ta tsaya abun yaci tura sai kawai ya shiga kalmar shahada Mussaman daya hango wata katuwar akori kura cike da katako tayo kansa. hannu na karkarwa ya fara kokarin bude motar domun ya fita daga ciki sai kawai yaji motar ta hantsila dashi 'kasa......"Innalillahi wa'ina ilaihi raji'un." A take motar tashi ta fara hayaki wuta na kokarin tashi, hayaniyar jama'a ya dinga ji sama-sama a kunnenshi ya dinga kiran sunan Allah yana kalmar shahada wutar ce ta tashi a daidai lokacin da jama'a ke kokarin taimakon sa ganin haka yasa kowa ya watse daga gurin wuta ta tashi a motarsa da motar katakon da suka had'u. da kyar 'yan a gaji suka samu nasarar kashe wutar gurin ya turnuke da haya'ki Alhaji Nura k'urmus aka fito dashi duk wani mai imani idan ya ganshi sai ya zubar da hawaye Allah sarki duniya ashe dama Alhaji Nura daf yake da barin duniya babu wanda ya san gaibu sai Allah....Labarin mutuwarsa ya zagaye garin Kano saboda shi din sanannan mutum wanda duk mutumin da yake shiga kasuwar Kwari ya san da zaman shi Abokan kasuwancin sa suka shiga alhini da damuwa.
Gwaggo kuwa kuka ta dinga yi tana fad'in "Allah Sarki Alhaji Nura Allah ya jikan ka mutumin arziki babu kai babu shiga wutar jahannama Allah ya jikan ka ya kar'bi shahadar ka." Rigima tasa akan lallai sai Kawu ya shirya ya kaita gidan mutuwar domin ayi jana'iza da ita.
Kawu da yake shima a cikin alhini yake bai mata gardama ba ta shirya ya d'auketa a motarsa domin zuwa gidan jana'izar DUNIYA KENAN ALLAH KASA MU CIKA DA KYAU DA IMANI.
Koda Khalid yazo gidan Ummatu ke sheda masa mutuwar jikinsa ne yayi sanyi damuwa da nadama suka baibayeshi ashe ma dik wannan hargitsin mutumin saura kad'an ya mutu kai gaskiya al'amarin ya girgiza shi mutuka, adduar samun rahamar Allah yayi masa yayi mata sallama domin tafiya harkokinsa.
To koda ya dawo da daddara kasa fad'a mata mutuwar yayi ya dai sassauta fuskarsa Sa'i da lokaci kuma yana satar kallonta da tunanin yanda zaiyi ya fad'a mata mutuwar mutumin.
Washe gari da safe yana shiryawa na shiga dakin cikin rashin kuzari nace." Amma Zaka tsaya kayi break fast ko."? Ya kalleta da fadin." Ba zanci abu mai nauyi ba don bana so jikina ya mutu za muyi wasa da abokaina sai dai idan na dawo.
Nace."Ai ko tea kasha ka gasa cikin ka ko." Yace." To shikkenan muje ki had'a min.'' Gaba nayi ya biyo bayana, tea din na had'a masa ya dauka yana sha yana kallona ni kam gabad'aya jikina a mace yake na rasa abinda yake damuna.
"Kina da labarin mutuwar.....Kasa 'karasawa yayi kawai ya zuba min ido.
Cikin fad'uwar gaba nace." Mutuwa waye ya mutu."?
Sunkuyar da kansa yayi yana motsa tea din gabansa yace." Sai hakuri dukkanin mai rai mamaci ne Alhaji Nura ya rigamu gidan gaskiya kwana biyu da suka wuce."
Wani irin kallo nake masa kafin wasu zafafan hawaye su wanke min fuska nace." Yanzu Alhaji Nura ya mutu har anyi kwana biyu amma a rasa wanda zai fad'a min."
Haushi ta bashi ganin tana kuka, sai kawai yaja bakinsa yayi shuru ya cigaba da kur'bar tea d'insa.
"Khalid me yasa kasan da mutuwar baka fad'a mun ba ashe shiyasa kwana biyu gabad'aya na rasa abinda ke damuna Allah Sarki Alhaji Nura ya mutu ya bar wannan duniyar mai cike da rud'ani."
Ya kalleta da fad'in." Wannan kukan dai da kike bashi da fa'ida addua zaki masa idan kuma zaki bishi lahirar dama hanya a bud'e take."
Cikin hawaye tace." Eh idan lokaci na yayi dole na tafi ko inaso ko bana so babu wanda zai zauna ya dawwama a duniya can ne gidan gaskiya sabida haka dik wanda ya dauki zafi da duniya to gwara ya sauke domin ba matabbata bace."
'Bata rai yayi yace." Sa'ida maganar nan ta isa haka bana bukatar ta." Miqewa nayi na bashi gurun, ina jin sanda yake jan dogon tsaki a kaina.
Bayan Kwana uku da faruwar al'amarin Hauwwa har gida tazo tayi min gaisuwa muka jima muna jajanta al'amarin yanda take bani labarin irin mutuwar da yayi yasa na dinga zubar da hawaye nace." Hauwwa aini gabadaya Khalid bai fada min ba yace kawai ya mutu amma bece dani accident yayi ba."
Tace." Aikuwa yana da kyau kije gaisuwa domin a ranar da mukaje gaisuwa da jama'ar gidanmu Mahaifiyarsa da matarsa Murja sai tambayarki suke."
Nace."Allah Sarki Insha Allahu zanje nai musu gaisuwa Hauwwa amma bana tsammanin har ya mutu da aure a tsakaninsa da Murja kin san tunda asirinta ya tuno shikkenan suka rabu."
Hauwwa tace." Allah sarki amma ba kiga yanda ta shiga damuwa ba ni dai har muka fito daga gidan bata daina kuka ba.''
Nace."Hauwwa ai dole aunty Murja tayi kuka Uban 'ya'yanta ne fa kuma ta cutar dashi sosai ta yaudareshi ya dauki amana da yarda ya bata amma ta zalince shi take masa fasikanci a gida."
Hauwwa tace." To Allah ya shiryeta yasa mutuwar tasa ta zama silar shiryuwarta Allah kuma ya raya abin da ya bari."
Hawaye na share da fad'in." Ameeen ameeen Ya Allah."
Mun jima tare da Hauwwa muna hira nan take bani labarin tsakaninta da Yaya Aminu sun fahimci juna sosai amma kuma tana jin tsoron auransa saboda kada ya kasa biya mata bukata.
Kwantar mata da hankali nayi nace." Hauwwa insha Allahu ba zaki samu matsala ba domin kuwa ina ji a jikina cewar Yaya Aminu ya samu lafiya saboda haka ki aureshi da kyakykyawar manufa."
Tace."To shikkenan Sa'ida ki taya ni da addua akan al'amarin." Nace."Insha Allahu zan miki addua Hauwwa Allah ya baku zaman lafiya."
Ta amsa da "Ameen ya Allah 'kawata."
Duk da nasan ba a gurina yake ba sai da na zauna zaman jiran shigowarsa domin sheda masa uziri na na zuwa gidan gaisuwar Alhaji Nura, to har wajen goma da Rabi na dare ina zaune a falo bai shigo ba mikewa nayi na nufi bakin window domin na duba naga ya dawo ko kuwa wani sa'in haka yake yi ko ya dawo baya shigowa yayi min sallama sai da safe idan zai fita, duka motocinsa suna nan alamu ya nuna ya jima da dawowa, girgiza kaina kawai nayi na saki labulan window din daki na nufa domin na kwanta na samu nutsuwa amma a zahirin gaskiya al'amarin yaron ya soma isa ta.