Sashe 24
Ga Irinta Nan Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ummatu zaman dirshan! tayi a gurin tana kuka tare da fad'in "Ni kam ba zan yarda da wannan k'azafin ba duk inda za muje a haka nake kuma ina da 'yan uwan da zasu tsaya min a gaban al'kali amma inaji ina gani ba zan yarda ayiwa yaro na qazafi ba."
Gwaggo tace."Ummatu ashe wu'ka zaki d'abawa kanki wane mahaukacin ne ya fad'a miki ana fita da irin wannan sirrin."?
Shuru tayi tana lalube a wayarta Gwaggo tace."To Wallahi tallahi kada ki kuskura naji maganar nan a wani guri Rabi idan kika sake kika fad'awa dangin ki abinda yake faruwa to zakiyi nadama mai tsananin gaske."
Hawaye ta share hannu na rawa tasa wayar a kunnenta tana fara ringing ta katse ta sake kiran wayar ta sake katsewa a sanyaye tace."Duk inda yake nasan yana kan hanyar dawowa gida gwara yazo ayi komai a gabansa ."
Gwaggo tace."Ko yazo ko bai zo ba shine munafiki kuma dole ya fuskanci hukunci domin shi da shigowa gidan nan har abadah."
Saurin kallonta tayi rai a tsananin 'bace tace."To idan bai shigo ba ina kike so yaje ya kwana."? kai tsaye tace."Ya tafi can dangin ki dama su suke d'aure masa gindi."
Ummatu ranta ya 'baci! kawai sai ta shiga farfad'ar bak'aken maganganu wanda Gwaggon ta kasa hakuri itama ta shiga mayar mata da martani suka dinga cacar baki Ummatu ta dage sai rashin kunya takewa Gwaggo........''To dama me nake samu a gidan idan ba wahala ba lafiya lau aka dauko ni daga gidan ubana da kuzari na da qiba ta amma tsabar wahala da yunwa tasa duk na lalace sai me idan kin sa shi ya sake ni."
Ummatu ce ke wannan maganar tana sakin wani irin nishi na bacin rai! Gwaggo tace."Rabi ba zan sa Ibrahim ya sake ki ba amma zan sashi yayi miki kishiya tunda ke baki da mutunci wato dama zuwa kike gidanku kina kwance mana zani ko duk tsiyarki Ibrahim yayi miki abinda uwarki da ubanki ba suyi miki ba."
Ummatu ta fashe da kuka da fad'in "Ni dai Allah ka jarrabe ni da jarabar Suruka tinda na auri d'anta banji dadi ba."
Nace."Gwaggo Ummatu kuyi hakuri dan darajar Allah kada makota su fara shigowa gidan asiri ya tono ni akai wa laifi kuma na barwa Allah."
Gwaggo tace."Dama shi ne alkali shi kuma wanda ya aikata zai girbi abinda ya shuka a nan gaba."
Ummatu da sauri tace."Insha Allahu zina ba dai a zuria ta b.......Shuru tayi ganin Kawu ya shigo gidan.
Ganin fuskarta jage-jage da hawaye yace."Me yake faruwa ne."? Ummatu ta tsuguna gurin tare dasa kuka.
Sai ya daga labulan dakin Gwaggo yana tambayarta...Tace."Shigo ciki ka samu nutsuwa na sheda maka abinda ya faru a gidan."
Jikinsa a sanyaye ya cire takalminsa ya shiga dakin ya zauna har lokacin Ummatu kuka take tana girgiza kanta ya ma za'ayi ta yarda da wannan qazafin.
Hankalinsa akan Sa'ida yace."Me ya samu fuskarki ta kumbura haka ga idanunki sunyi jawur kamar wacce taci kuka ta koshi."
Zuciya tace ta karye naji hawaye na nema ya kufce min cikin rawar murya nace"Babu komai Kawu."
Sai ya kalli Gwaggo yana neman 'karin bayani. tace."Rabi mi'ko min zanin gadon nan idan kin gama d'ibar albarkar."
Ummatu a sanyaye ta dauki zanin gadon ta shiga dashi dakin ta miqa mata ta juya zata fita tace."Aa ai babu inda zakije zauna nan tunda ga Ibrahim din ya dawo ayi magana a gabansa."
Ummatu gabanta ya buga tana jin tsoro kada ya sake aunata gidansu. jiki a sanyaye ta nemi bakin kofa ta zauna.
Gwaggo ta shiga warware zanin gadon... da sauri nasa hannu na 'karbe ina girgiza mata kai hawaye na zuba a saman fuskata.
Murya na rawa tace."Sa'ida ki bari a nuna masa sheda." nace."Gwaggo dan Allah dan Annabi maganar nan ta isa haka a barta ni na barwa Allah." da kyar na'karasa maganar saboda kuka mai karfin daya kufce min na miqe da saurin gaske na fita daga dakin guri na samu na tsuguna na dinga kuka ina kiran kalmar innalillahi wa'ina ilaihi raji'una."
Baba Ibrahim jiki a mace yace."Gwaggo dukkanin abinda yake faruwa a gidan nan nake so ki fad'a min dan girman Allah kada ki 'boye min komai."
Ta girgiza kai tare da fad'in "Ibrahim ai ranar wanka ba'a 'boyan cibi wannan lamari ya zama dole ka sanshi domin kana da hakkim sanin abinda d'anka Khalid ya aikata akan marainiyar Allah."
Hawaye ta share tace."Ibrahim Khalid tinda ya samu labarin auran Sa'ida da Alhaji Nura ya tayar da hankalinsa ya dinga jifan al'amarin da mugwayen kalmomi tare da yin ikirari mai muni kancewar mutukar ba'a janye maganar auran Alhaji Nura ba to ba zai yarda ba sai ya dauki mataki! jin haka yasa na zaunar dashi na dinga rarrashinsa akan yayi hakuri ya barwa Allah komai na rayuwa rabo ne ashe yaron nan bai dauki nasiha ta ba ya shirya mugun abu.....'Dazu nida Rabi muka tafi gidan bikin 'yar gidan Jummai muka bar Sa'ida a gidan ita kadai tana bacci to wannan damar khalid ya samu ya haike mata a takaice dai Khalid shi yayiwa Sa'ida fyad'e abinda nake so na fada maka kenan."
Kawu Iro yayi 'kasa da kansa wani irin gumi! mai d'umi ya dinga tsatstsafo masa! hular saman kansa ya cire baki a bushe? yace."Gwaggo Khalid irin tozarcin da xaiyi mana kenan ? me mukayi masa a rayuwa? me kuma Sa'ida tayi masa da zai keta mata rigar mutumci wane irin kallo Alhaji Nura zaiyi mana a matsayin mu na iyayen yarinyar nan Gwaggo da sadakin wani Khalid ya aikata wannan 'barnar? idan Alhaji Nura ya kusanci yarinyar yaji ba daidai ba wani irin kallo zaiyi mata? me zai biyo baya a zamantakewar auranta."
Gwaggo ta goge hawaye a sanyaye tace."Shine dama babban tashin hankali da damuwar ai kawai Ibrahim ka ajiye maganar Alhaji Nura a gefe a mayar masa sa kud'insa Sa'ida babu namijin da zata aura a cikin wannan halin ta samu nutsuwa Khalid din dai shi zamu hakura ta aura asirinmu ya rufu.''
Kawu ya girgiza kansa cikin mugun takaici da nadamar haihuwar yaron yace."Gwaggo Sa'ida bata dace da macucin yaron nan ba saboda haka ki daina wannan maganar tsayin wattani biyar mun kar'bi sadaki a hannun mutumin nan ya za'ayi ace za mayar masa hakuri kawai za muyi a daura auran mu cigaba da addua kafin muga abinda Allah zaiyi."
Tace."To ai shikkenan Ibrahim yanzu wane mataki ka dauka akan Khalid din......Girgiza kansa yayi da fad'in "Kotu zan kai shi Alkali ya yanke masa hukunci daidai da abinda ya aikata wallahi ba zan bari mutucin marainiyar Allah ya tafi a banza ba.
Ummatu ta fashe da kuka da fad'in " Haba kai kuwa wace irin magana ce wannan? kana nufin d'an cikin ka zaka kai kotu akan abinda baka da tabbas a kansa."
Ya kalleta yace."Rabi ke zaki qalubalanci maganar mahaifiyata a gabana me kike nufi? kina so ki fada min cewa Gwaggo sharri tayi wa d'anki kome."
Girgiza kanta tayi tace."Aa ni ba haka nake nufi ba naji kana maganar kai shi kotu nace kafin ka yanke wannan hukunci ka tsaurara binkice akan al'amarin."
Cikin fusata! yace."Ba zan tsautsara binkicen ba! ni d'an halak ne kuma nasan *ZAMANI* Khalid babu abinda ba zai aikata ba tunda yasa son zuciya a ransa. mahaifiyata ba zata 'kir'kiri sharri ta d'ora masa ba."
Tace."Ai ba haka nake nufi ba ita Sa'idar me yasa bakwa ganin laifinta Khalid fa yaro ne akanta to har yaushe ma zai iya sarrafata ballanatana yayi mata fyad'e."
Takaici ya cika zuciyar Kawu Iro yace."Rabi idan baki daina magana anan gurin ba ranki zai mummunan 'baci! wane irin rashin tarbiya ne wannan a gabana kike kokarin 'karya ta mahaifiyata."
Gwaggo tayi murmushi wanda bai kai ciki ba tace."Ibrahim rabu da ita haka ita 'karya ai fure take bata 'ya'ya ita wai tana so ta kare d'anta akan abinda ya aikata idan kin kareshi a duniya a lahira fa."?
Ummatu tayi shuru tana shaqar hanci....Kawu Iro ya dauki wayarsa yana lalube number Khalid din ya nemo ya shiga kira.....Is swich Up. wayar a kashe take.
Ya dinga kira ana fada masa a kashe take...Gwaggo tace."Ai dole ya kashe waya tunda yasa abun da ya aikata ai da tuni ya shigo gidan."
Kawu Iro ya mike da sauri ya fita daga dakin.....tsayuwarsa naji a kaina na dago da sauri ina kallonsa....'bacin rai da damuwar da nagani a fuskarsa yasa wasu hawayen sake yankowa hakika Khalid ya jefa zuciyoyin mu cikin masifar tashin hankali
A sanyaye yace."Ki daina kuka kinji ko ki barwa Allah zai saka miki sannan inaso ki dauki wannan al'amari a matsayin qaddara wacce ta riga fata insha Allahu Allah zai dubi maraicinki Khalid kuma da ya aikata miki wannan abu ni da kaina zan kaishi a hukuntashi .
"Ajiyar zuciya na sauke ina goge hawayen fuskata nace." Kawu insha Allahu zan sanyawa raina dangana akan wannan al'amari sannan maganar kai khalid hukuma ka janye nasan tunda zalinci ya aikata sai Allah ya hukuntashi a duniya ko a lahira."
Girgiza kansa yayi yace."Sa'ida idan nayi haka naci amanar zumuncin Allah kuma duniya zata zage ni dole ne na dauki mataki akan dukkanin wanda ya ta'ba martabarki."
Kafin nace wani abu yayi gaggawar fita daga gidan...jiki a mace na bishi da kallo ina girgiza kaina.
Ummatu yun'kurawa tayi zata mi'ke Gwaggo ta dakatar da ita da fad'in "Rabi kin gama koke-koken ne."? Ummatu ta zuba mata ido tana kallonta, Tace." To wallahi kada naji da wai! maganar nan ta fita waje al'amarin nan ya zama sirri a tsakaninmu idan kika fad'awa dangin ki maganar nan wallahi kinji na rantse sai kin fi kowa 'bacin rai."
Ummatu girgiza kanta tayi ba tare da tace mata komai ba ta kad'a kanta ta fita daga dakin ranta a mugun 'bace.
Inda nake bata kalla ba ballanatana ta tanka min ta bude kofar gurin ta ta shige tare da bugo kofar da karfin gaske!
A hankali na mi'ke na nufi dakin jiri da hajijiya na neman su kayar dani a gurin.
Gwaggo tace."Ummatu ashe wu'ka zaki d'abawa kanki wane mahaukacin ne ya fad'a miki ana fita da irin wannan sirrin."?
Shuru tayi tana lalube a wayarta Gwaggo tace."To Wallahi tallahi kada ki kuskura naji maganar nan a wani guri Rabi idan kika sake kika fad'awa dangin ki abinda yake faruwa to zakiyi nadama mai tsananin gaske."
Hawaye ta share hannu na rawa tasa wayar a kunnenta tana fara ringing ta katse ta sake kiran wayar ta sake katsewa a sanyaye tace."Duk inda yake nasan yana kan hanyar dawowa gida gwara yazo ayi komai a gabansa ."
Gwaggo tace."Ko yazo ko bai zo ba shine munafiki kuma dole ya fuskanci hukunci domin shi da shigowa gidan nan har abadah."
Saurin kallonta tayi rai a tsananin 'bace tace."To idan bai shigo ba ina kike so yaje ya kwana."? kai tsaye tace."Ya tafi can dangin ki dama su suke d'aure masa gindi."
Ummatu ranta ya 'baci! kawai sai ta shiga farfad'ar bak'aken maganganu wanda Gwaggon ta kasa hakuri itama ta shiga mayar mata da martani suka dinga cacar baki Ummatu ta dage sai rashin kunya takewa Gwaggo........''To dama me nake samu a gidan idan ba wahala ba lafiya lau aka dauko ni daga gidan ubana da kuzari na da qiba ta amma tsabar wahala da yunwa tasa duk na lalace sai me idan kin sa shi ya sake ni."
Ummatu ce ke wannan maganar tana sakin wani irin nishi na bacin rai! Gwaggo tace."Rabi ba zan sa Ibrahim ya sake ki ba amma zan sashi yayi miki kishiya tunda ke baki da mutunci wato dama zuwa kike gidanku kina kwance mana zani ko duk tsiyarki Ibrahim yayi miki abinda uwarki da ubanki ba suyi miki ba."
Ummatu ta fashe da kuka da fad'in "Ni dai Allah ka jarrabe ni da jarabar Suruka tinda na auri d'anta banji dadi ba."
Nace."Gwaggo Ummatu kuyi hakuri dan darajar Allah kada makota su fara shigowa gidan asiri ya tono ni akai wa laifi kuma na barwa Allah."
Gwaggo tace."Dama shi ne alkali shi kuma wanda ya aikata zai girbi abinda ya shuka a nan gaba."
Ummatu da sauri tace."Insha Allahu zina ba dai a zuria ta b.......Shuru tayi ganin Kawu ya shigo gidan.
Ganin fuskarta jage-jage da hawaye yace."Me yake faruwa ne."? Ummatu ta tsuguna gurin tare dasa kuka.
Sai ya daga labulan dakin Gwaggo yana tambayarta...Tace."Shigo ciki ka samu nutsuwa na sheda maka abinda ya faru a gidan."
Jikinsa a sanyaye ya cire takalminsa ya shiga dakin ya zauna har lokacin Ummatu kuka take tana girgiza kanta ya ma za'ayi ta yarda da wannan qazafin.
Hankalinsa akan Sa'ida yace."Me ya samu fuskarki ta kumbura haka ga idanunki sunyi jawur kamar wacce taci kuka ta koshi."
Zuciya tace ta karye naji hawaye na nema ya kufce min cikin rawar murya nace"Babu komai Kawu."
Sai ya kalli Gwaggo yana neman 'karin bayani. tace."Rabi mi'ko min zanin gadon nan idan kin gama d'ibar albarkar."
Ummatu a sanyaye ta dauki zanin gadon ta shiga dashi dakin ta miqa mata ta juya zata fita tace."Aa ai babu inda zakije zauna nan tunda ga Ibrahim din ya dawo ayi magana a gabansa."
Ummatu gabanta ya buga tana jin tsoro kada ya sake aunata gidansu. jiki a sanyaye ta nemi bakin kofa ta zauna.
Gwaggo ta shiga warware zanin gadon... da sauri nasa hannu na 'karbe ina girgiza mata kai hawaye na zuba a saman fuskata.
Murya na rawa tace."Sa'ida ki bari a nuna masa sheda." nace."Gwaggo dan Allah dan Annabi maganar nan ta isa haka a barta ni na barwa Allah." da kyar na'karasa maganar saboda kuka mai karfin daya kufce min na miqe da saurin gaske na fita daga dakin guri na samu na tsuguna na dinga kuka ina kiran kalmar innalillahi wa'ina ilaihi raji'una."
Baba Ibrahim jiki a mace yace."Gwaggo dukkanin abinda yake faruwa a gidan nan nake so ki fad'a min dan girman Allah kada ki 'boye min komai."
Ta girgiza kai tare da fad'in "Ibrahim ai ranar wanka ba'a 'boyan cibi wannan lamari ya zama dole ka sanshi domin kana da hakkim sanin abinda d'anka Khalid ya aikata akan marainiyar Allah."
Hawaye ta share tace."Ibrahim Khalid tinda ya samu labarin auran Sa'ida da Alhaji Nura ya tayar da hankalinsa ya dinga jifan al'amarin da mugwayen kalmomi tare da yin ikirari mai muni kancewar mutukar ba'a janye maganar auran Alhaji Nura ba to ba zai yarda ba sai ya dauki mataki! jin haka yasa na zaunar dashi na dinga rarrashinsa akan yayi hakuri ya barwa Allah komai na rayuwa rabo ne ashe yaron nan bai dauki nasiha ta ba ya shirya mugun abu.....'Dazu nida Rabi muka tafi gidan bikin 'yar gidan Jummai muka bar Sa'ida a gidan ita kadai tana bacci to wannan damar khalid ya samu ya haike mata a takaice dai Khalid shi yayiwa Sa'ida fyad'e abinda nake so na fada maka kenan."
Kawu Iro yayi 'kasa da kansa wani irin gumi! mai d'umi ya dinga tsatstsafo masa! hular saman kansa ya cire baki a bushe? yace."Gwaggo Khalid irin tozarcin da xaiyi mana kenan ? me mukayi masa a rayuwa? me kuma Sa'ida tayi masa da zai keta mata rigar mutumci wane irin kallo Alhaji Nura zaiyi mana a matsayin mu na iyayen yarinyar nan Gwaggo da sadakin wani Khalid ya aikata wannan 'barnar? idan Alhaji Nura ya kusanci yarinyar yaji ba daidai ba wani irin kallo zaiyi mata? me zai biyo baya a zamantakewar auranta."
Gwaggo ta goge hawaye a sanyaye tace."Shine dama babban tashin hankali da damuwar ai kawai Ibrahim ka ajiye maganar Alhaji Nura a gefe a mayar masa sa kud'insa Sa'ida babu namijin da zata aura a cikin wannan halin ta samu nutsuwa Khalid din dai shi zamu hakura ta aura asirinmu ya rufu.''
Kawu ya girgiza kansa cikin mugun takaici da nadamar haihuwar yaron yace."Gwaggo Sa'ida bata dace da macucin yaron nan ba saboda haka ki daina wannan maganar tsayin wattani biyar mun kar'bi sadaki a hannun mutumin nan ya za'ayi ace za mayar masa hakuri kawai za muyi a daura auran mu cigaba da addua kafin muga abinda Allah zaiyi."
Tace."To ai shikkenan Ibrahim yanzu wane mataki ka dauka akan Khalid din......Girgiza kansa yayi da fad'in "Kotu zan kai shi Alkali ya yanke masa hukunci daidai da abinda ya aikata wallahi ba zan bari mutucin marainiyar Allah ya tafi a banza ba.
Ummatu ta fashe da kuka da fad'in " Haba kai kuwa wace irin magana ce wannan? kana nufin d'an cikin ka zaka kai kotu akan abinda baka da tabbas a kansa."
Ya kalleta yace."Rabi ke zaki qalubalanci maganar mahaifiyata a gabana me kike nufi? kina so ki fada min cewa Gwaggo sharri tayi wa d'anki kome."
Girgiza kanta tayi tace."Aa ni ba haka nake nufi ba naji kana maganar kai shi kotu nace kafin ka yanke wannan hukunci ka tsaurara binkice akan al'amarin."
Cikin fusata! yace."Ba zan tsautsara binkicen ba! ni d'an halak ne kuma nasan *ZAMANI* Khalid babu abinda ba zai aikata ba tunda yasa son zuciya a ransa. mahaifiyata ba zata 'kir'kiri sharri ta d'ora masa ba."
Tace."Ai ba haka nake nufi ba ita Sa'idar me yasa bakwa ganin laifinta Khalid fa yaro ne akanta to har yaushe ma zai iya sarrafata ballanatana yayi mata fyad'e."
Takaici ya cika zuciyar Kawu Iro yace."Rabi idan baki daina magana anan gurin ba ranki zai mummunan 'baci! wane irin rashin tarbiya ne wannan a gabana kike kokarin 'karya ta mahaifiyata."
Gwaggo tayi murmushi wanda bai kai ciki ba tace."Ibrahim rabu da ita haka ita 'karya ai fure take bata 'ya'ya ita wai tana so ta kare d'anta akan abinda ya aikata idan kin kareshi a duniya a lahira fa."?
Ummatu tayi shuru tana shaqar hanci....Kawu Iro ya dauki wayarsa yana lalube number Khalid din ya nemo ya shiga kira.....Is swich Up. wayar a kashe take.
Ya dinga kira ana fada masa a kashe take...Gwaggo tace."Ai dole ya kashe waya tunda yasa abun da ya aikata ai da tuni ya shigo gidan."
Kawu Iro ya mike da sauri ya fita daga dakin.....tsayuwarsa naji a kaina na dago da sauri ina kallonsa....'bacin rai da damuwar da nagani a fuskarsa yasa wasu hawayen sake yankowa hakika Khalid ya jefa zuciyoyin mu cikin masifar tashin hankali
A sanyaye yace."Ki daina kuka kinji ko ki barwa Allah zai saka miki sannan inaso ki dauki wannan al'amari a matsayin qaddara wacce ta riga fata insha Allahu Allah zai dubi maraicinki Khalid kuma da ya aikata miki wannan abu ni da kaina zan kaishi a hukuntashi .
"Ajiyar zuciya na sauke ina goge hawayen fuskata nace." Kawu insha Allahu zan sanyawa raina dangana akan wannan al'amari sannan maganar kai khalid hukuma ka janye nasan tunda zalinci ya aikata sai Allah ya hukuntashi a duniya ko a lahira."
Girgiza kansa yayi yace."Sa'ida idan nayi haka naci amanar zumuncin Allah kuma duniya zata zage ni dole ne na dauki mataki akan dukkanin wanda ya ta'ba martabarki."
Kafin nace wani abu yayi gaggawar fita daga gidan...jiki a mace na bishi da kallo ina girgiza kaina.
Ummatu yun'kurawa tayi zata mi'ke Gwaggo ta dakatar da ita da fad'in "Rabi kin gama koke-koken ne."? Ummatu ta zuba mata ido tana kallonta, Tace." To wallahi kada naji da wai! maganar nan ta fita waje al'amarin nan ya zama sirri a tsakaninmu idan kika fad'awa dangin ki maganar nan wallahi kinji na rantse sai kin fi kowa 'bacin rai."
Ummatu girgiza kanta tayi ba tare da tace mata komai ba ta kad'a kanta ta fita daga dakin ranta a mugun 'bace.
Inda nake bata kalla ba ballanatana ta tanka min ta bude kofar gurin ta ta shige tare da bugo kofar da karfin gaske!
A hankali na mi'ke na nufi dakin jiri da hajijiya na neman su kayar dani a gurin.