Sashe 40
Ga Irinta Nan Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Hannu ya daga mata yace."Murja kin san bana magana biyu ko saboda haka ki bar maganar kawai ni nake auran Sa'ida ba ita ke aurena ba dan haka zan nuna mata cewa ni cikakken namiji ne."
Tace."To shikkenan tunda kace haka sai dai nace Allah ya kyauta ya rufa asiri." shuru yayi bai amsa ba ya nata wani muzurai kamar gaske.
Nayi ta tsammanin dawowarsa dakin naji shuru cikin takaici da bakin ciki na kwanta da kyar bacci ya dauke ni.
Na d'auka da safe zai shigo mu gaisa naji shuru har goma da rabi babu labarinsa, falon na fita shuru matar gidan na sama yara kuma sun tafi makaranta.
Jiki a sa'bule na zauna gurin cikin abincin.
haka na yini cikin 'kunci da damuwa ga Khalid ya ishe ni da kiran waya lallai sai na bashi Gwaggo sun gaisa sai da nayi masa jan ido sannan ya rabu dani muka rabu cikin Jin haushin juna.
Haka na cigaba da kasancewa a gidan Alhaji Nura tsayin sati guda babu wani zaman Arziki a tsakanina dashi, tun ranar da mukayi musayar yawu dashi bai sake shigowa dakina ba haka nan kuma idan zan ganshi a falo na gaishe shi baya ko kallon inda nake ballantana ya amsa min gaisuwata.
Sosai na shiga cikin tsaka mai wuya nadama mara amfani duk ta buwaye ni gabadaya kaina ya kulle na rasa wane irin tunani zanyi.
Ranar Lahadi nasan baya fita kasuwa da wuri sai na fito falon na samesu suna zaune suna hira na zauna kan kujerar dake fuskantarsu a nutse nace."Aunty Murja kin tashi lafiya ya kwanan su Yusura."
Ta amsa fuska a sake kamar ko da yaushe....kallonsa nayi yana duba jarida wanda zama na a gurin ne yasa shi daukar jaridar "Barka da asubah Alhaji."
Ciki ciki ya amsa hankalinsa nakan jaridar nace."Ina so zanyi magana da kai." ba tare da ya kalle ni ba yace."Ki fada ina sauraranki.
Shuru nayi na minti biyu kafin nace."Akan maganar aiki na ne dama hutun sati biyu suka bani to kaga yau sati na uku ban je ba shine nake so insha Allahu gobe zan koma bakin aiki."
Ba tare da ya kalleni ba yace."Babu maganar aiki a gidana tunda da ban gaza da komai ba saboda haka ki ajiye maganar aiki a gefe mutukar ni nake auranki na soke maganar zuwa gurin aiki."
Wani irin gumi! ya shiga yanko min murya na rawa nace."Alhaji wannan wace irin magana ce? kada ka zama 'karamin mutum mai magana biyu mana ya za'ayi muyi da wajewa da kai kafin muyi aure amma sai bayan bukatarka ta biya sai kuma ka sanja magana."
A fusace! ya daga min hannu da fad'in "Sa'ida me kike so ki mayar dani ne? wato nine ma nake magana biyu."? Cikin rawar baki nace" Eh hak.......'Barin makauniya yayi a fuskata! nasa hannu na dafe kumatuna ina mamakin sanda yazo inda nake har ya samu nasarar mari na.
Yana tsaye a kaina yana huci da kumfar baki sai bambami yake Ita kuma gwanar tasa tana rirrikeshi tana bashi hakuri da fad'in "Haba Sa'ida ashe haka kike da tsayayya me ya sanya zaki dinga jayayya da mijinki."
Cikin b'acin rai na mike tsaye da fad'in "Kinga saurara aunty Murja nifa ba 'kan'kanuwar yarinya bace ballanatana ki dinga wasa da hankalina duk abinda yake faruwa a gidan nan da sanya hannuki a ciki saboda haka kiyi shuru da bakin ki bana son munafurci."
Kalar tausayi ta koma da fad'in "Sa'ida ni kike kira munafuka." Cikin rawa murya nace."Idan ba ita bace mecec....Marin dai ya k'ara kawo min na kauce da sauri ina kallonsa hawaye na ambaliya a fuskata nace."Wallahi dana san kai mijin tace ne a gidanka da ban aureka ba."
Yana numfarfashi yace."Ki fice min daga gidana." da sauri tace."Subahanallahi Abban Yusura kada ka yanke wannan hukuncin.
Rai a 'bace yace."Murja na fada miki babu wata mace da zan aura ta ta'ba martabarki na 'kyaleta saboda haka mutukar Sa'ida tana bukatar ta zauna lafiya dani to sai ta baki hakuri."
Na dinga kallonsa ina mamakin maganarsa wato sai na bata hakuri sannan zai zauna dani lafiya. kallona yayi yace."Ki bata hakuri ko bakya ji ne."
Kaina kawai na girgiza ba tare da nace komai ba na kad'a kaina na bar gurin.
Dakina na shiga na samu gefan gado na zauna kuke ne ya 'kwace min na dinga yi ina girgiza kaina wannan takaici da bakin ciki har inaa! lallai babu shakka dole na bar masa gidansa domin ba zan zauna bawa wata 'yar iska hakuri ba.
Sai da naci kuka na na koshi tukkuna na shiga toilet na wanke fuskata kaya na na hada cikin akwati nasa hijabi na na fito.
Har yanzu suna zaune a falon suna mayar da magana kai tsaye hanyar fita na nufa. ina kokarin bude kofa tazo ta rike akwatin hannuna. "Haba Sa'ida mai yayi zafi haka dan Allah kiyi hakuri kada ki tafi abun kunya ne ace aure sati uku kacal har an fara yaji sam bai dace ba.
Akwatin kaya na na fizge daga hannunta nace." Aunty Murja ai zama da Alhaji Nura sai ke kamar yanda ya fada cewa komai naku a tsare yake keda shi to bai kamata wani yazo ya rusa muku tsari ba kamata yayi ace ku biyu kacal zaku zauna sai 'ya'yanku.
Girgiza kanta ta shiga yi kamar wata mutuniyar arziki sai hakuri take bani shi kuma yana zaune 'kwam akan kujera na d'an hango nadama a fuskarsa amma tsabar girman kai ya hanashi yayi magana.
Ganin ta juya ta nai masa magana yasa da sauri na kwace akwatina a hannunta na bude kofa da sauri na fita.
Gwaggo na zaune a tsakar gida da kayan kad'i a gabanta gefe guda kuma tana sauraran redio tashar freedom suna gabatar da shirin barka da hantsi....Ummatu na bakin rijiya tana wanke-wanke suna hira yanzu tsakanin Gwaggo da Ummatu an samu daidaito sun daina fad'a kullum suka zauna hirar Khalid da Sa'ida suke gabadayansu suna cikin alhinin rabuwa dasu.......Gwara Khalid suna gaisawa dashi dan da ya gaji da kiran wayar Sa'ida tana yi masa yawo da hankali kawai sai ya yanke shawarar kiran wayar mahaifiyarsa su gaisa sannan ta bawa Gwaggo itama su gaisa.
Khalid bai samu damar zuwa gidan ba sabida yanda Oga Laraban da sauran abokanansa suka taushe shi gami da nuna masa muhimmacin abinda ke gabansu, a cikin satin daya gabata Mr William yazo daga america aka gabatar da shahararran wasan daya daukaka 'kungiyar kano pillars Khalid dashi da Ahamad Musa sunyi kokari sosai kuma sun zama zakaran gwajin dafi domin sune suka cinye kofin da ko wane team suke 'kwa'kwa Oga Laraban tamkar ya zuba ruwa a kasa yasha sabida tsabar murna da farin cikin kungiyarsa ta cinye kofi......To wannan dalilin ne yasa bai samu damar zuwa gidan ba a lokacin daya fad'a zai zo sai yanzu da hankalinsu ya kwanta suka shirya tafiyar shida Salmanu.
Sallamar ta a cikin gidan itace ta katse musu hirar da suke. gabadaya suka bita da kallo a lokacin da take shiga gidan da akwatin kayanta a hannunta.
Gwaggo a sa'bule ta amsa sallamar ta cigaba da bin ta da kallo har ta cire takalmanta ta shiga daki ba tare da tace musu komai ba.
Ummatu tace."Gwaggo anya lafiya kuwa Sa'ida ta shigo jiki a sab'ule ga kuma a kwati a hannunta.
Gwaggo ta ajiye makad'in hannunta ta yunkura da nufin mi'kewa tace"Aa Rabi ai wannan zuwan na Sa'ida ba na lafiya bane kina ganin ta shigo gidan kai tsaye ta shiga daki bari nabi bayanta.
Ummatu shuru tayi jikinta duk ya mutu........Kuka ta shiga ta same ni inayi. a sanyaye ta tsaya kaina da fad'in "Sa'ida me yake faruwa? kada kice min Alhaji Nura ya sake ki bayan ya tabbatar da babu budurci a tare dake."?
Kaina na girgiza nace." Gwaggo Alhaji Nura Bashi da kirki ashe mijin tace ne a gidansa sai abinda matarsa tace dashi."
Ajiyar zuciya ta sauke ta nemi guri ta zauna da fad'in "Wallahi na dauka ko saboda rashin budurci ne ya koro ki gida ashe ba wannan matsalar bace.''
Girgiza kaina nayi nace" Ba wannan matsalar bace Gwaggo........Tiryan tiryan na fad'a mata dukkanin abubuwan da suke faruwa ban rage mata komai ba
Gwaggo ta dinga mamaki tana girgiza kanta tace."Ashe duk kirkin matar nan da jama'a suke fad'a na gaibu ne ashe fuska biyu gare ta.''
Nace."Wallahi kuwa Gwaggo aunty Murja muguwar makira ce shi kuma kamar tsoronta yake duk abinda tace shine daidai wai dole sai na bata hakuri sannan zan zauna a gidan Gwaggo babban abinda yafi tayar min da hankalina shine maganar gurin aikina wai bai yarda na k'ara zuwa ba."
Gwaggo shuru tayi tana girgiza kanta gami da jajanta al'amarin.
*Kuyi manege babu yawa ana bikin 'yar yar Mamana sannan yau ma kuyi min uziri ba zaku samu na dare ba nagode*
*47&48*
Gwaggo tace.''Yanzu dai kiyi hakuri ki daina kuka zamu jira Ibrahim ya dawo domin muji hukuncin da zai yanke amma gaskiya Alhaji Nura ya bani mamaki ashe mace ke juya shi." Nace."Gwaggo ai ba kiji mamaki da takaici ba sai kinga abin da idonki." Tace."To Allah ya sawake yasa ya zama jajurtacce a gidansa.
shuru kawai nayi ina tunanin abinda zai biyo baya.
To koda Kawu ya dawo ya samu labarin a binda yake faruwa shima ransa ya 'baci sosai da irin abinda Alhaji Nuran yake a gidansa ya kalleni cikin kulawa yace."Kiyi hakuri kinji ko yanzu za mu jira zuwan sa domin shime muji da abinda zai zo amma maganar zuwa aiki ki ajiye ta tunda dai baya so sai ki hakura.''
Cikin kuka nace."Kawu ya za'ayi na saki aiki na bayan kafin auranmu sai da mukayi da wajewa dashi ya amince zan cigaba da aiki na sai kuma yanzu yazo ya sanja magana."
Yace."Sa'ida aikin nan ba dole bane tunda Allah ya rufawa mijinki asiri baki da wata matsala sai ki hakura ki zauna kiyi zaman auranki lafiya."
Hawaye na share ina jin wani irin d'aci a ma'kogwarona anya kuwa zan iya hakura da aiki na kuwa."
Washe gari da sassafe Ummatu ta shigo da waya a hannunta tana fad'in "Gwaggo Khalid ne ya kira yanzu yanzu yake sheda min cewa yana kan hanya."
Tace."To shikkenan tunda kace haka sai dai nace Allah ya kyauta ya rufa asiri." shuru yayi bai amsa ba ya nata wani muzurai kamar gaske.
Nayi ta tsammanin dawowarsa dakin naji shuru cikin takaici da bakin ciki na kwanta da kyar bacci ya dauke ni.
Na d'auka da safe zai shigo mu gaisa naji shuru har goma da rabi babu labarinsa, falon na fita shuru matar gidan na sama yara kuma sun tafi makaranta.
Jiki a sa'bule na zauna gurin cikin abincin.
haka na yini cikin 'kunci da damuwa ga Khalid ya ishe ni da kiran waya lallai sai na bashi Gwaggo sun gaisa sai da nayi masa jan ido sannan ya rabu dani muka rabu cikin Jin haushin juna.
Haka na cigaba da kasancewa a gidan Alhaji Nura tsayin sati guda babu wani zaman Arziki a tsakanina dashi, tun ranar da mukayi musayar yawu dashi bai sake shigowa dakina ba haka nan kuma idan zan ganshi a falo na gaishe shi baya ko kallon inda nake ballantana ya amsa min gaisuwata.
Sosai na shiga cikin tsaka mai wuya nadama mara amfani duk ta buwaye ni gabadaya kaina ya kulle na rasa wane irin tunani zanyi.
Ranar Lahadi nasan baya fita kasuwa da wuri sai na fito falon na samesu suna zaune suna hira na zauna kan kujerar dake fuskantarsu a nutse nace."Aunty Murja kin tashi lafiya ya kwanan su Yusura."
Ta amsa fuska a sake kamar ko da yaushe....kallonsa nayi yana duba jarida wanda zama na a gurin ne yasa shi daukar jaridar "Barka da asubah Alhaji."
Ciki ciki ya amsa hankalinsa nakan jaridar nace."Ina so zanyi magana da kai." ba tare da ya kalle ni ba yace."Ki fada ina sauraranki.
Shuru nayi na minti biyu kafin nace."Akan maganar aiki na ne dama hutun sati biyu suka bani to kaga yau sati na uku ban je ba shine nake so insha Allahu gobe zan koma bakin aiki."
Ba tare da ya kalleni ba yace."Babu maganar aiki a gidana tunda da ban gaza da komai ba saboda haka ki ajiye maganar aiki a gefe mutukar ni nake auranki na soke maganar zuwa gurin aiki."
Wani irin gumi! ya shiga yanko min murya na rawa nace."Alhaji wannan wace irin magana ce? kada ka zama 'karamin mutum mai magana biyu mana ya za'ayi muyi da wajewa da kai kafin muyi aure amma sai bayan bukatarka ta biya sai kuma ka sanja magana."
A fusace! ya daga min hannu da fad'in "Sa'ida me kike so ki mayar dani ne? wato nine ma nake magana biyu."? Cikin rawar baki nace" Eh hak.......'Barin makauniya yayi a fuskata! nasa hannu na dafe kumatuna ina mamakin sanda yazo inda nake har ya samu nasarar mari na.
Yana tsaye a kaina yana huci da kumfar baki sai bambami yake Ita kuma gwanar tasa tana rirrikeshi tana bashi hakuri da fad'in "Haba Sa'ida ashe haka kike da tsayayya me ya sanya zaki dinga jayayya da mijinki."
Cikin b'acin rai na mike tsaye da fad'in "Kinga saurara aunty Murja nifa ba 'kan'kanuwar yarinya bace ballanatana ki dinga wasa da hankalina duk abinda yake faruwa a gidan nan da sanya hannuki a ciki saboda haka kiyi shuru da bakin ki bana son munafurci."
Kalar tausayi ta koma da fad'in "Sa'ida ni kike kira munafuka." Cikin rawa murya nace."Idan ba ita bace mecec....Marin dai ya k'ara kawo min na kauce da sauri ina kallonsa hawaye na ambaliya a fuskata nace."Wallahi dana san kai mijin tace ne a gidanka da ban aureka ba."
Yana numfarfashi yace."Ki fice min daga gidana." da sauri tace."Subahanallahi Abban Yusura kada ka yanke wannan hukuncin.
Rai a 'bace yace."Murja na fada miki babu wata mace da zan aura ta ta'ba martabarki na 'kyaleta saboda haka mutukar Sa'ida tana bukatar ta zauna lafiya dani to sai ta baki hakuri."
Na dinga kallonsa ina mamakin maganarsa wato sai na bata hakuri sannan zai zauna dani lafiya. kallona yayi yace."Ki bata hakuri ko bakya ji ne."
Kaina kawai na girgiza ba tare da nace komai ba na kad'a kaina na bar gurin.
Dakina na shiga na samu gefan gado na zauna kuke ne ya 'kwace min na dinga yi ina girgiza kaina wannan takaici da bakin ciki har inaa! lallai babu shakka dole na bar masa gidansa domin ba zan zauna bawa wata 'yar iska hakuri ba.
Sai da naci kuka na na koshi tukkuna na shiga toilet na wanke fuskata kaya na na hada cikin akwati nasa hijabi na na fito.
Har yanzu suna zaune a falon suna mayar da magana kai tsaye hanyar fita na nufa. ina kokarin bude kofa tazo ta rike akwatin hannuna. "Haba Sa'ida mai yayi zafi haka dan Allah kiyi hakuri kada ki tafi abun kunya ne ace aure sati uku kacal har an fara yaji sam bai dace ba.
Akwatin kaya na na fizge daga hannunta nace." Aunty Murja ai zama da Alhaji Nura sai ke kamar yanda ya fada cewa komai naku a tsare yake keda shi to bai kamata wani yazo ya rusa muku tsari ba kamata yayi ace ku biyu kacal zaku zauna sai 'ya'yanku.
Girgiza kanta ta shiga yi kamar wata mutuniyar arziki sai hakuri take bani shi kuma yana zaune 'kwam akan kujera na d'an hango nadama a fuskarsa amma tsabar girman kai ya hanashi yayi magana.
Ganin ta juya ta nai masa magana yasa da sauri na kwace akwatina a hannunta na bude kofa da sauri na fita.
Gwaggo na zaune a tsakar gida da kayan kad'i a gabanta gefe guda kuma tana sauraran redio tashar freedom suna gabatar da shirin barka da hantsi....Ummatu na bakin rijiya tana wanke-wanke suna hira yanzu tsakanin Gwaggo da Ummatu an samu daidaito sun daina fad'a kullum suka zauna hirar Khalid da Sa'ida suke gabadayansu suna cikin alhinin rabuwa dasu.......Gwara Khalid suna gaisawa dashi dan da ya gaji da kiran wayar Sa'ida tana yi masa yawo da hankali kawai sai ya yanke shawarar kiran wayar mahaifiyarsa su gaisa sannan ta bawa Gwaggo itama su gaisa.
Khalid bai samu damar zuwa gidan ba sabida yanda Oga Laraban da sauran abokanansa suka taushe shi gami da nuna masa muhimmacin abinda ke gabansu, a cikin satin daya gabata Mr William yazo daga america aka gabatar da shahararran wasan daya daukaka 'kungiyar kano pillars Khalid dashi da Ahamad Musa sunyi kokari sosai kuma sun zama zakaran gwajin dafi domin sune suka cinye kofin da ko wane team suke 'kwa'kwa Oga Laraban tamkar ya zuba ruwa a kasa yasha sabida tsabar murna da farin cikin kungiyarsa ta cinye kofi......To wannan dalilin ne yasa bai samu damar zuwa gidan ba a lokacin daya fad'a zai zo sai yanzu da hankalinsu ya kwanta suka shirya tafiyar shida Salmanu.
Sallamar ta a cikin gidan itace ta katse musu hirar da suke. gabadaya suka bita da kallo a lokacin da take shiga gidan da akwatin kayanta a hannunta.
Gwaggo a sa'bule ta amsa sallamar ta cigaba da bin ta da kallo har ta cire takalmanta ta shiga daki ba tare da tace musu komai ba.
Ummatu tace."Gwaggo anya lafiya kuwa Sa'ida ta shigo jiki a sab'ule ga kuma a kwati a hannunta.
Gwaggo ta ajiye makad'in hannunta ta yunkura da nufin mi'kewa tace"Aa Rabi ai wannan zuwan na Sa'ida ba na lafiya bane kina ganin ta shigo gidan kai tsaye ta shiga daki bari nabi bayanta.
Ummatu shuru tayi jikinta duk ya mutu........Kuka ta shiga ta same ni inayi. a sanyaye ta tsaya kaina da fad'in "Sa'ida me yake faruwa? kada kice min Alhaji Nura ya sake ki bayan ya tabbatar da babu budurci a tare dake."?
Kaina na girgiza nace." Gwaggo Alhaji Nura Bashi da kirki ashe mijin tace ne a gidansa sai abinda matarsa tace dashi."
Ajiyar zuciya ta sauke ta nemi guri ta zauna da fad'in "Wallahi na dauka ko saboda rashin budurci ne ya koro ki gida ashe ba wannan matsalar bace.''
Girgiza kaina nayi nace" Ba wannan matsalar bace Gwaggo........Tiryan tiryan na fad'a mata dukkanin abubuwan da suke faruwa ban rage mata komai ba
Gwaggo ta dinga mamaki tana girgiza kanta tace."Ashe duk kirkin matar nan da jama'a suke fad'a na gaibu ne ashe fuska biyu gare ta.''
Nace."Wallahi kuwa Gwaggo aunty Murja muguwar makira ce shi kuma kamar tsoronta yake duk abinda tace shine daidai wai dole sai na bata hakuri sannan zan zauna a gidan Gwaggo babban abinda yafi tayar min da hankalina shine maganar gurin aikina wai bai yarda na k'ara zuwa ba."
Gwaggo shuru tayi tana girgiza kanta gami da jajanta al'amarin.
*Kuyi manege babu yawa ana bikin 'yar yar Mamana sannan yau ma kuyi min uziri ba zaku samu na dare ba nagode*
*47&48*
Gwaggo tace.''Yanzu dai kiyi hakuri ki daina kuka zamu jira Ibrahim ya dawo domin muji hukuncin da zai yanke amma gaskiya Alhaji Nura ya bani mamaki ashe mace ke juya shi." Nace."Gwaggo ai ba kiji mamaki da takaici ba sai kinga abin da idonki." Tace."To Allah ya sawake yasa ya zama jajurtacce a gidansa.
shuru kawai nayi ina tunanin abinda zai biyo baya.
To koda Kawu ya dawo ya samu labarin a binda yake faruwa shima ransa ya 'baci sosai da irin abinda Alhaji Nuran yake a gidansa ya kalleni cikin kulawa yace."Kiyi hakuri kinji ko yanzu za mu jira zuwan sa domin shime muji da abinda zai zo amma maganar zuwa aiki ki ajiye ta tunda dai baya so sai ki hakura.''
Cikin kuka nace."Kawu ya za'ayi na saki aiki na bayan kafin auranmu sai da mukayi da wajewa dashi ya amince zan cigaba da aiki na sai kuma yanzu yazo ya sanja magana."
Yace."Sa'ida aikin nan ba dole bane tunda Allah ya rufawa mijinki asiri baki da wata matsala sai ki hakura ki zauna kiyi zaman auranki lafiya."
Hawaye na share ina jin wani irin d'aci a ma'kogwarona anya kuwa zan iya hakura da aiki na kuwa."
Washe gari da sassafe Ummatu ta shigo da waya a hannunta tana fad'in "Gwaggo Khalid ne ya kira yanzu yanzu yake sheda min cewa yana kan hanya."