Sashe 30
Ga Irinta Nan Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Nace."Yau kuma d'an wake kike sha'awa."'? Tana cigaba da kad'i tace.Aikam kin san rai da marmari." Girgiza kaina kawai nayi cikin zuciyata nace."Gwaggo sar'ka kenan mai rikicin gangan.
Mikewa nayi zan fita tace."Ina kuma zakije da ina so muyi wata magana mai muhimmanci.
Nace."Zan duba almajiri ne ya siyo min kayan miya nayi miya dan ba zanci farar taliya da mai ulcer zata tayar min.
Tace."Yawwa to tunda hakane nima na fasa siyan d'anwaken Allah yasa a samu almajirin."
Ameen nace na fita daga dakin....daga cikin soron na tsaya ina le'kawa can na hango almajirai su uku hannu na daga musu gabad'ayansu suka 'karaso inda nake na mikawa daya daga cikinsu dari biyu da fad'in "Dan Allah kayan miya zaku siyo min na duka.''
Da sauri suka ce to suka tafi ni kuma na koma cikin gidan
Tana zaune a inda take na nemi guri na zauna ina kallonta da fad'in " Wace magana za muyi."
Ta dago a nutse tace."Ya jikin naki ina fatan gurin ya daina ciwo.'' nace."Eh alhamdulillahi." Tace."Masha Allah haka ake so."
Dakin yayi shuru na minti biyar kafin tace." Dazu bayan tafiyar ki makaranta Ina sauraran shirin *TAMBAYA MABUDIN ILIMI* wanda Malam *AMINU DAURAWA* yake gabatarwa a tashar freedom redio naji yana amsa wata tambaya da akayi masa akan budurwar da akayi mata fyad'e ko kuma karuwar da ta tuba ta dawo gida domin tayi tsarkakken aure shine yake cewa ba kai tsaye za'a daura aure ba sai mace tayi tsarki uku an tabbatar da cewa babu ciki a tare da ita sai a d'aura auran wannan shine daidai da abinda addinin musulunci ya tanada sai duk jikina yayi sanyi Sa'ida ina so kiyi tsarkakken aure gashi yau saura kwana biyar daurin auranki yanzu ya kike ganin za'ayi me zamu cewa da Alhaji Nura nasan dai shi yanzu ya gama shirye-shiryensa lokaci kawai yake jira yanzu ya kike ganin za'ayi."?
Cikin wani irin yanayi nace."Gwaggo wallahi nima ban san ya za'ayi ba gabad'aya na mance da hakan kinga Amfanin sauraran redio kenan da tuni an daura aure akan kwamacala."
Tace." To Sa'ida ai ita redio tamkar makaranta take domin babu abinda basa koyawa mutane wallahi sauraran redio yafi mutum ya kalli akwatin talabijin mutukar ba tashoshin addinin musulunci mutum zai kalla ba."
Nace."Hakane maganarki Gwaggo yanzu wace shawara za 'a yanke."? Tace." Bari Babanki Iro ya dawo mu tattauna shima nasan hankalinsa ne ya dauke baiyi tunanin hakan ba nasan idan ya dawo yaji abinda yake da akwai dole a nemo mafita."
Ajiyar zuciya na sauke nace"Gwaggo Allah yayi mana maganin masifa.'' ta amsa da "ameen 'yan nan."
To kusan awa guda kenan da aiken da nayi wa almajirai shuru basu dawo ba, Nace"Gwaggo kinga awa guda almajiran nan basu kawo kayan miyan ba.
Tace."Sa'ida Ai almajiran unguwar nan su zama abinda suka zama Allah yasa dai basu gudu da kudin ba domin sau nawa suka gudar min da kudi shiyasa kika ina zuwa nayi uzirina da kaina.
Girgiza kaina nayi nace." Allah ya kyauta to.'' tace"Sai dai fa kiyi hakuri ki bada wani kudin a siyo kayan miyan." Nace."Bani dasu tunda kin san yanzu dai a karshen wata muke ki siyo ai nasan kina da kudi.
Tace."To bari na 'karasa abinda nake sai naje na siyo." Tana rufe baki naji alamar shigowar text wayata daukar wayar nayi ina dubawa, Khalid ne wai dan Allah yana so yayi magana da Gwaggo yanzu zai kira sai na bata wayar. takaici ya sani na kashe wayar gabadaya na ajiyeta.
'Bangaransa kuwa hankalinsa ne ya tashi sosai lokacin daya kira wayar yaji ta a kashe ya kalli Salmanu a raunane yace."Kaga ta kashe wayar gabadaya.'' Salmanu yace."Ka kira ta mahaifinka mana." shiru yayi yana tunani kafin ya yanke hukuncin kiran mahaifin nasa.
Baba Iro yana kasuwa yaga kiran D'an nasa 'kin daga wayar yayi har ta karaci ringing d'inta ta katse. Khalid sai da ya kira sau kusan biyar Kawu Ibrahim bai daga ba. sai ya yanke shawarar kiran ta mahaifiyarsa a lokacin ta dawo daga zauran Malam Sammani suna tattaunawa da mahaifiyarta Baito ganin Khalid din ke kiranta a waya sai farin ciki ya isheta hakika babu abinda za tace da malam sammani gashi tun kafin aje ko'ina aiki yayi kyau Khalid din ya kira wayarta.
Hannu na rawa ta dauki wayar tasa a kunnenta tana kiran sunansa.
Ajiyar zuciya ya sauke yace."Ummatu ku gafarce ni." sai kawai ta fashe da kuka da fadin."Khalid kana ina ne? me yasa ka gudu bayan baka ka aikata ba nasan ni yaro na kamili ne ba zai aikata abinda ake zarginsa ba.
Yace."Ummatu ni na aikata ba wani mahaluki ba wallahi nine." sai hawaye suka 'kwace mata tana rawar baki tace."Khalid kaine fa kace."
Yace."Eh Ummatu tsautsayi da qaddara ne ku gafarce ni." hannu tasa ta sharce gumin fuskarta tace."To yanzu kana ina."?
Yace."Ummatu ina gidansu abokina a halin yanzu domin ina jin kunyar sake hada ido da gwaggo da Babana naci amanarsu na tozartasu a idon duniya dalilin da yasa kenan na yanke shawarar barin gari gabadaya.
Gabanta ne ya fad'i da sauri tace."Khalid ba'a kan ka aka fara ba kuma ba za'a 'kare a kanka ba saboda haka ka dawo gida shine kwanciyar hankalina.
"Ummatu kiyi hakuri ki gafarce ni ba zan dawo gida na zauna cikin takaici da damuwa ba ki yafe min kuma kiyi min fatan alkairi a duk inda nake."
Yana gama maganar ya kashe wayar kansa na wani irin sarawa
Ummatu baki a sake take kallon mahaifiyarta Baito tace."Wai me yake faruwa ne."?
Bude baki tayi za tayi magana sai kuma kuka ya kufce mata!
baito hankali a tashe ta dinga tambayarta abunda ya faru Ummatu sai da taci kukunta ta koshi ta fada mata yanda sukayi da Khalid din.
Baito tace."Amma nayi mamakin hakan saboda nasan aikin malam Sammanin kamar yankan wuka haka yake to me yasa wannan karon aikin yayi gardama."
Ummatu tace."Ni babban tashin hankalina ma katifa ta dana siyar gashi yaron nan yana tabbatar min da cewa ba zai dawo gida a wannan lokacin ba
Baito tace"Share hawayen ki ki daina kuka akwai malamai a gari saboda haka yanzu sauran kudin da suka rage a hannunki dasu zamuyi amfani zaki tashi yanzu muje mu nemi inda za'ayi aiki mai zafi akan yaron nan."
Ummatu a sanyaye tace."To shikkenan Baito Allah yasa a dace." Baito ta amsa da cewa "Za'a dace da yardar Allah bari na shirya mu tafi."
Mikewa tayi ta hau shiryawa suna sake tattauna maganar.
Sai daf da magariba suka gama yawace yawacen gurin malaman tun a hanya suka rabu da juna....Ummatu ana kiran sallah ta shigo gidan lokacin Gwaggo na zaune a kan kujera tana alwala sallama tayi Gwaggo ta kalleta kafafunta sunyi fururu! duk tayi firgai-firgai da ita! Gwaggo ta amsa sallamar da fad'in "Rabi daga ina kike haka kinyi fururu dake kamar an haqo ki daga rami."
Ummatu shuru tayi bata tanka mata ba ta bude kofarta ta shige...Gwaggo ta bita da kallo tana girgiza kanta.
Ummatu abubuwan hannunta ta ajiye da sauri ta fito ta shiga kicin ta hura wuta ta dora tukunya ta fito a gurguje tayi alwala azahur la'asar magriba ta had'a a lokaci guda tana idar da sallar ta mike ta dauko kaskon wuta kicin ta shiga ta d'ebo garwashi da yawa tazo ta bude ledojin data shigo dasu wani magani ta dauko daure a leda ta kwance ai kafin kice kwabo ta rikice da atishawa maganin jajawur dashi kamar barkono tana zabga atishawar ta zuba maganin cikin wutar ta mike da saurin gaske ta fito babban tsakar gidan tasa a tsakiya ta tsaya kan maganin tana kiran sunan Khalid.
Gwaggo dake sallah atishawa da majina suka cika mata hanci hawaye kawai take a jigace! ta idar da sallar ni kuwa tunda na leqa tsakar gidan naga Ummatu a tsaye gaban kaskon sai kace soja na koma dakin na kwanta tare da toshe hancina daya cika da majina tsinkakkiya.....Tana idar da sallar ta hau sababi da fad'in "Wace irin jaraba kuma aka shigo mana da ita gida." Zaune na mike ina kokarin hana ta fita ta fizge hannunta da fad'in "Ke sakar min hannu na fita naga jarabar da matar nan take." Fita tayi daga dakin tana surutai....har yanzu Ummatu na tsaye a tsakiyar tsakar gidan da kaskon wuta a gabanta yana hayaki tana kiran sunan Khalid fuskarta tayi gaja-gaja da majina da gumi da hawaye sai nishi take tana sakin atishawa.....Gwaggo da sauri ta 'karasa gurin tasa kafa tayi wurgi da kaskon wutar da fad'in "Rabi wane irin surkulle ne wannan........!
*SADAUKARWA NE GA IYAYE NA BIYU*
*FATIMA MUSA (MOMMY NIJAR)*
*TARE DA*
*USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)*
*(HAJIYA BABBAH)*
*_Ha'kika ina Alfahari daku da irin kaunar da kuke min.🥰🤝🏻💜_*
*33&34*
Ummatu da sauri ta d'aga kaskon dake cike da wutar ta gyarashi haya'kin ya cigaba da tashi a gurin tana me cigaba da kiran sunan Khalid a bayyane .........Gwaggo ta tsorata sosai da sauri ta bar gurin tana toshe hancinta dakin ta dawo ta same ni da tissue ina goge hanci gabad'aya majina ta tsinke min wannan wace irin jaraba ce...Hannuna ta kamo muka fito daga dakin har yanzu Ummatu na tsaye akan maganin tana aiki ita kanta sauri take ta gama kiran sunan Khalid din iya adadin da aka gindaya mata .
Kofar gida muka fita muka tsaitsaya muna mayar da numfashi..Gwaggo ta kalli cikin soron gidan tasa gefen hijabinta ta goge hawayen dake sauka a fuskarta tace."Sa'ida kinga yanda haya'kin nan yake fitowa kuwa."
Soron na le'ke na gani nace."Gwaggo matsa daga gurin ki bashi hanya ya fice idan gidan ya sarara sai mu koma.
Kusa dani ta tsaya tana zazzare ido kafin tace."Sa'ida kiga jaraba mutum da gidansa an koro shi waje kai gaskiya Rabi shaid'aniya ce wallahi tana azabtar damu."
Nace."Gwaggo addua zakiyi mata Allah ya shiryeta." tace."Sa'ida idan da Rabi zata shiryu da tuntuni ta shiryu kullum fa a tafe take to daga yau ta daina fita daga gida domin zan sa Ibrahim ya gindaya mata sharad'ai."
Tana rufe bakinta Kawun ya karyo kwana nace"Alhamdulillahi gashinan ma.'' Ajiyar zuciya ta sauke dukkaninmu muka tsira masa ido har ya karaso gurin.
Hankali a tashe yace."Gwaggo lafiya na ganku da magariba a tsaye a waje."
Mikewa nayi zan fita tace."Ina kuma zakije da ina so muyi wata magana mai muhimmanci.
Nace."Zan duba almajiri ne ya siyo min kayan miya nayi miya dan ba zanci farar taliya da mai ulcer zata tayar min.
Tace."Yawwa to tunda hakane nima na fasa siyan d'anwaken Allah yasa a samu almajirin."
Ameen nace na fita daga dakin....daga cikin soron na tsaya ina le'kawa can na hango almajirai su uku hannu na daga musu gabad'ayansu suka 'karaso inda nake na mikawa daya daga cikinsu dari biyu da fad'in "Dan Allah kayan miya zaku siyo min na duka.''
Da sauri suka ce to suka tafi ni kuma na koma cikin gidan
Tana zaune a inda take na nemi guri na zauna ina kallonta da fad'in " Wace magana za muyi."
Ta dago a nutse tace."Ya jikin naki ina fatan gurin ya daina ciwo.'' nace."Eh alhamdulillahi." Tace."Masha Allah haka ake so."
Dakin yayi shuru na minti biyar kafin tace." Dazu bayan tafiyar ki makaranta Ina sauraran shirin *TAMBAYA MABUDIN ILIMI* wanda Malam *AMINU DAURAWA* yake gabatarwa a tashar freedom redio naji yana amsa wata tambaya da akayi masa akan budurwar da akayi mata fyad'e ko kuma karuwar da ta tuba ta dawo gida domin tayi tsarkakken aure shine yake cewa ba kai tsaye za'a daura aure ba sai mace tayi tsarki uku an tabbatar da cewa babu ciki a tare da ita sai a d'aura auran wannan shine daidai da abinda addinin musulunci ya tanada sai duk jikina yayi sanyi Sa'ida ina so kiyi tsarkakken aure gashi yau saura kwana biyar daurin auranki yanzu ya kike ganin za'ayi me zamu cewa da Alhaji Nura nasan dai shi yanzu ya gama shirye-shiryensa lokaci kawai yake jira yanzu ya kike ganin za'ayi."?
Cikin wani irin yanayi nace."Gwaggo wallahi nima ban san ya za'ayi ba gabad'aya na mance da hakan kinga Amfanin sauraran redio kenan da tuni an daura aure akan kwamacala."
Tace." To Sa'ida ai ita redio tamkar makaranta take domin babu abinda basa koyawa mutane wallahi sauraran redio yafi mutum ya kalli akwatin talabijin mutukar ba tashoshin addinin musulunci mutum zai kalla ba."
Nace."Hakane maganarki Gwaggo yanzu wace shawara za 'a yanke."? Tace." Bari Babanki Iro ya dawo mu tattauna shima nasan hankalinsa ne ya dauke baiyi tunanin hakan ba nasan idan ya dawo yaji abinda yake da akwai dole a nemo mafita."
Ajiyar zuciya na sauke nace"Gwaggo Allah yayi mana maganin masifa.'' ta amsa da "ameen 'yan nan."
To kusan awa guda kenan da aiken da nayi wa almajirai shuru basu dawo ba, Nace"Gwaggo kinga awa guda almajiran nan basu kawo kayan miyan ba.
Tace."Sa'ida Ai almajiran unguwar nan su zama abinda suka zama Allah yasa dai basu gudu da kudin ba domin sau nawa suka gudar min da kudi shiyasa kika ina zuwa nayi uzirina da kaina.
Girgiza kaina nayi nace." Allah ya kyauta to.'' tace"Sai dai fa kiyi hakuri ki bada wani kudin a siyo kayan miyan." Nace."Bani dasu tunda kin san yanzu dai a karshen wata muke ki siyo ai nasan kina da kudi.
Tace."To bari na 'karasa abinda nake sai naje na siyo." Tana rufe baki naji alamar shigowar text wayata daukar wayar nayi ina dubawa, Khalid ne wai dan Allah yana so yayi magana da Gwaggo yanzu zai kira sai na bata wayar. takaici ya sani na kashe wayar gabadaya na ajiyeta.
'Bangaransa kuwa hankalinsa ne ya tashi sosai lokacin daya kira wayar yaji ta a kashe ya kalli Salmanu a raunane yace."Kaga ta kashe wayar gabadaya.'' Salmanu yace."Ka kira ta mahaifinka mana." shiru yayi yana tunani kafin ya yanke hukuncin kiran mahaifin nasa.
Baba Iro yana kasuwa yaga kiran D'an nasa 'kin daga wayar yayi har ta karaci ringing d'inta ta katse. Khalid sai da ya kira sau kusan biyar Kawu Ibrahim bai daga ba. sai ya yanke shawarar kiran ta mahaifiyarsa a lokacin ta dawo daga zauran Malam Sammani suna tattaunawa da mahaifiyarta Baito ganin Khalid din ke kiranta a waya sai farin ciki ya isheta hakika babu abinda za tace da malam sammani gashi tun kafin aje ko'ina aiki yayi kyau Khalid din ya kira wayarta.
Hannu na rawa ta dauki wayar tasa a kunnenta tana kiran sunansa.
Ajiyar zuciya ya sauke yace."Ummatu ku gafarce ni." sai kawai ta fashe da kuka da fadin."Khalid kana ina ne? me yasa ka gudu bayan baka ka aikata ba nasan ni yaro na kamili ne ba zai aikata abinda ake zarginsa ba.
Yace."Ummatu ni na aikata ba wani mahaluki ba wallahi nine." sai hawaye suka 'kwace mata tana rawar baki tace."Khalid kaine fa kace."
Yace."Eh Ummatu tsautsayi da qaddara ne ku gafarce ni." hannu tasa ta sharce gumin fuskarta tace."To yanzu kana ina."?
Yace."Ummatu ina gidansu abokina a halin yanzu domin ina jin kunyar sake hada ido da gwaggo da Babana naci amanarsu na tozartasu a idon duniya dalilin da yasa kenan na yanke shawarar barin gari gabadaya.
Gabanta ne ya fad'i da sauri tace."Khalid ba'a kan ka aka fara ba kuma ba za'a 'kare a kanka ba saboda haka ka dawo gida shine kwanciyar hankalina.
"Ummatu kiyi hakuri ki gafarce ni ba zan dawo gida na zauna cikin takaici da damuwa ba ki yafe min kuma kiyi min fatan alkairi a duk inda nake."
Yana gama maganar ya kashe wayar kansa na wani irin sarawa
Ummatu baki a sake take kallon mahaifiyarta Baito tace."Wai me yake faruwa ne."?
Bude baki tayi za tayi magana sai kuma kuka ya kufce mata!
baito hankali a tashe ta dinga tambayarta abunda ya faru Ummatu sai da taci kukunta ta koshi ta fada mata yanda sukayi da Khalid din.
Baito tace."Amma nayi mamakin hakan saboda nasan aikin malam Sammanin kamar yankan wuka haka yake to me yasa wannan karon aikin yayi gardama."
Ummatu tace."Ni babban tashin hankalina ma katifa ta dana siyar gashi yaron nan yana tabbatar min da cewa ba zai dawo gida a wannan lokacin ba
Baito tace"Share hawayen ki ki daina kuka akwai malamai a gari saboda haka yanzu sauran kudin da suka rage a hannunki dasu zamuyi amfani zaki tashi yanzu muje mu nemi inda za'ayi aiki mai zafi akan yaron nan."
Ummatu a sanyaye tace."To shikkenan Baito Allah yasa a dace." Baito ta amsa da cewa "Za'a dace da yardar Allah bari na shirya mu tafi."
Mikewa tayi ta hau shiryawa suna sake tattauna maganar.
Sai daf da magariba suka gama yawace yawacen gurin malaman tun a hanya suka rabu da juna....Ummatu ana kiran sallah ta shigo gidan lokacin Gwaggo na zaune a kan kujera tana alwala sallama tayi Gwaggo ta kalleta kafafunta sunyi fururu! duk tayi firgai-firgai da ita! Gwaggo ta amsa sallamar da fad'in "Rabi daga ina kike haka kinyi fururu dake kamar an haqo ki daga rami."
Ummatu shuru tayi bata tanka mata ba ta bude kofarta ta shige...Gwaggo ta bita da kallo tana girgiza kanta.
Ummatu abubuwan hannunta ta ajiye da sauri ta fito ta shiga kicin ta hura wuta ta dora tukunya ta fito a gurguje tayi alwala azahur la'asar magriba ta had'a a lokaci guda tana idar da sallar ta mike ta dauko kaskon wuta kicin ta shiga ta d'ebo garwashi da yawa tazo ta bude ledojin data shigo dasu wani magani ta dauko daure a leda ta kwance ai kafin kice kwabo ta rikice da atishawa maganin jajawur dashi kamar barkono tana zabga atishawar ta zuba maganin cikin wutar ta mike da saurin gaske ta fito babban tsakar gidan tasa a tsakiya ta tsaya kan maganin tana kiran sunan Khalid.
Gwaggo dake sallah atishawa da majina suka cika mata hanci hawaye kawai take a jigace! ta idar da sallar ni kuwa tunda na leqa tsakar gidan naga Ummatu a tsaye gaban kaskon sai kace soja na koma dakin na kwanta tare da toshe hancina daya cika da majina tsinkakkiya.....Tana idar da sallar ta hau sababi da fad'in "Wace irin jaraba kuma aka shigo mana da ita gida." Zaune na mike ina kokarin hana ta fita ta fizge hannunta da fad'in "Ke sakar min hannu na fita naga jarabar da matar nan take." Fita tayi daga dakin tana surutai....har yanzu Ummatu na tsaye a tsakiyar tsakar gidan da kaskon wuta a gabanta yana hayaki tana kiran sunan Khalid fuskarta tayi gaja-gaja da majina da gumi da hawaye sai nishi take tana sakin atishawa.....Gwaggo da sauri ta 'karasa gurin tasa kafa tayi wurgi da kaskon wutar da fad'in "Rabi wane irin surkulle ne wannan........!
*SADAUKARWA NE GA IYAYE NA BIYU*
*FATIMA MUSA (MOMMY NIJAR)*
*TARE DA*
*USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)*
*(HAJIYA BABBAH)*
*_Ha'kika ina Alfahari daku da irin kaunar da kuke min.🥰🤝🏻💜_*
*33&34*
Ummatu da sauri ta d'aga kaskon dake cike da wutar ta gyarashi haya'kin ya cigaba da tashi a gurin tana me cigaba da kiran sunan Khalid a bayyane .........Gwaggo ta tsorata sosai da sauri ta bar gurin tana toshe hancinta dakin ta dawo ta same ni da tissue ina goge hanci gabad'aya majina ta tsinke min wannan wace irin jaraba ce...Hannuna ta kamo muka fito daga dakin har yanzu Ummatu na tsaye akan maganin tana aiki ita kanta sauri take ta gama kiran sunan Khalid din iya adadin da aka gindaya mata .
Kofar gida muka fita muka tsaitsaya muna mayar da numfashi..Gwaggo ta kalli cikin soron gidan tasa gefen hijabinta ta goge hawayen dake sauka a fuskarta tace."Sa'ida kinga yanda haya'kin nan yake fitowa kuwa."
Soron na le'ke na gani nace."Gwaggo matsa daga gurin ki bashi hanya ya fice idan gidan ya sarara sai mu koma.
Kusa dani ta tsaya tana zazzare ido kafin tace."Sa'ida kiga jaraba mutum da gidansa an koro shi waje kai gaskiya Rabi shaid'aniya ce wallahi tana azabtar damu."
Nace."Gwaggo addua zakiyi mata Allah ya shiryeta." tace."Sa'ida idan da Rabi zata shiryu da tuntuni ta shiryu kullum fa a tafe take to daga yau ta daina fita daga gida domin zan sa Ibrahim ya gindaya mata sharad'ai."
Tana rufe bakinta Kawun ya karyo kwana nace"Alhamdulillahi gashinan ma.'' Ajiyar zuciya ta sauke dukkaninmu muka tsira masa ido har ya karaso gurin.
Hankali a tashe yace."Gwaggo lafiya na ganku da magariba a tsaye a waje."