Sashe 46
Ga Irinta Nan Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sai da nayi wanka tsaf na shirya jikina na daidaici cewar sun bar daining din sannan na fita falon kai tsaye gurin cin abincin na nufa ba tare dana tanka musu ba.
Ina kokarin zama naji tana fad'in "Sa'ida yau Hajia Aziza tazo ko.''? Nace."Eh tazo." Tace."Wallahi sai da na fita na tuna ashe ban fada mata zani unguwa ba kuma nayi ta kiran wayarta domin na sheda mata wayar ta'ki shiga."
Nace."Eh itama haka tace har nace ta biki gidan biki tace Aa ba zataje ba."
D'an murmushi tayi da fad'in "Hajiya Aziza kenan." cikin zuciyata nace "Gafalallu insha Allahu sai Allah ya tona muku asiri.
Mintina goma sha biyar na kammala cin abincina na mike a nutse na bar gurin. dakina na nufa Yusura tace." Aunty yanzu zasu saka *TARKO KAUNA* Naga zaki shiga daki yau ba zaki kalla ba.'' Ba tare dana juyo ba nace."Yusura yau bacci nake ji na kalli maimaici ranar lahadi.'' Tace."To shikkenan aunty Sai da safe." na amsa da Allah ya tashemu lafiya.
Ina kokarin shiga bargo ya shigo dakin ya tsaya a kaina zaune na mike ina kallonsa yace."Wulakancin naki har akan 'ya'yana zaki gwada.
Nace."Ban fahimci maganarka ba." A hasale yace."Yarinyar nan Yusura tana miki magana sabida kina ji da isa da iko ki gagara kallon inda take shin dame kike takama ne."?
Murmushin takaici nayi nace."Bana takama da kowa sai Allah da ma'aiki'' Da sauri yace."Ki kiyaye b'ata ran d'aya daga cikin iyalina kinji ko baki ji ba."
Nace."Naji yanzu Ita Yusuran ce ta turo ka kazo ka sauke min ashafa ko kuma uwarta ce."? Kallona yayi da fad'in "Zakiyi min rashin kunyar da kika saba ne."
Nace."Ai gaskiya ce sabida nasan wannan hayaniyar da kazo kana yi min ba tunaninka bane turo ka akayi."
Hannu ya daga zai kwada min mari na kauce da sauri ya mari iska.
Yana huci yace."Wai me yasa kika raina ni Sa'ida me kika mayar dani a cikin gidana."
Cike da takaici nace."Alhaji kaine kasa kima da mutuncinka duk suka zube a idona kasan Allah a yanzu dai sai dai kawai na kalleka domin kayi min bazata ban ta'ba zaton zan shigo gidanka nayi irin wannan rayuwar ba."
Yace." Wannan rayuwar kuma ki rubuta ki ajiye yanzu kika fara ni haka tsarina yake a gidana babu wata macan data isa tace min ga yanda zanyi 'karya take.
Dariya ya bani na kalleshi yana tsaye a kaina sai daga murya sama yake nace."Yanzu dai magana ta wuce akan na 'ki zaman falo aka zuga ka kazo kaci min mutunci to naji na dauka nayi laifi kayi hakuri."
Shuru yayi yana sauke ajiyar zuciya, Nace."Ka zauna inaso muyi magana. a watse ya kalleni da fadin"Kin san ba girkin bane ko."? Nace."Eh na sani ai ba wata doguwar magana zamuyi ba.
Zama yayi kusa dani yana kallona. Nace."Kasan me? a ya mutse yace."Sai kin fada." Nace."Ka hana wannan matar zuwa gidan ka ina nufin hajiya Aziza 'kawar aunty Murja."
"A kan wane dalili zan hanata zuwa."? Yayi maganar tare da tsareni da idonsa.
Nace." Ba alkairi ne yake kawo ta gidan ba tana zuwa ta hana mala'ikun rahama shigowa gidanka sabida haka ka hanata zuwa shi yafi alkairi.
"Ba zan hana ta shigowa gidana ba sai naji dalilin ki." ajiyar zuciya na saukw idona akansa nace." *'YAR MADIGO (LESBIAN)* ce."
Wani irin kallo yake min kafin yace."Shine me? dan Aziza tana Lesbian sai kike zargin Matata Murja.''?
Cike da karsashi da kwarin gwiwa nace."Kwarai kuwa dole nayi zarginta saboda tayi abinda zai janyo hakan Hajiya Aziza a sati sai tazo sau uku ko sau hudu sannan idan suka hau sama suka rufe kofa sai yamma suke saukowa."
Shuru yayi kansa a 'kasa na cigaba da cewa''Yau tazo gidan lokacin Aunt Murja ta tafi gidan biki ni kuma ina daki ina bacci ta shigo ta same ni ...........Duk abinda ya faru ta kwashe kaf ta fad'a masa.
Wani irin gumi! ne yake karyo masa ya dinga kallona bakinsa na rawa da alama magana yake so yayi amma tsabar rud'u ya hana shi cewa komai.
Nace."Dan Allah ka fahimci maganata kuma ka yanke hukuncin daya dace wallahi tallahi banyi musu sharri ba.
Da 'kyar ya iya fadin"Sa'ida a gidan nawa ake aikata wannan kafurcin tsayin shekaru ban sani ba.
Ajiyar zuciya na sauke nace."Yau ne Allah yaso kasan abinda yake faruwa saboda haka sai kayi namijin kokari gurin ganin ka kori wannan masifar da ta kunno maka a gida.
Mi'kewa yayi ya kama hanyar fita yana tafiya yana had'a hanya babu shakka al'amarin yayi masifar saka shi cikin rud'u da tashin hankali mai tsanani.
Tana kwance a gado cikin kayan bacci masu fitar da tsaraici ya shiga dakin sama-sama ta amsa sallamarsa domin taji masifar haushin zaman da yayi a dakin Sa'ida.
Ya nemi gefan gado ya zauna yana kallonta a burkice!
Zaune ta mi'ke had'e da ajiye wayar hannunta tace."Lafiya na ganka ka shigo a burkice wani abun ne ya faru."?
Ya kalleta da jajayan idanunsa yace."Murja ashe dama ha'intata kikeyi."? da sauri tace."Wace irin magana ce wannan."? Hannu ya daga mata a kaushashe! yace." Menene tsakanin ki da wannan matar dake zuwa gurunki.?
Gabanta ne ya fad'i baki na rawa tace."Wace mata kake magana."?
Yace."Hajiya Aziza matar da kuka had'u da ita a fece book." Ajiyar zuciya ta sauke tace."Alhaji babu abunda yake tsakanina da Aziza sai mutumci da zumunci."
Yace."Ban yarda da maganarki ba Murja kina gayyato min 'yar iska gida kuna iskanci yaushe kika zama lalatacciya."?
Cikin firgici tace."Wai ya kake magana a baibai ne ka fito fili ka fada min abinda kake nufi dani."
Yace."Sa'ida ta tabbatar min da cewa" Aziza *'YAR MADIGO (LESBIAN)* ce domin a dazu da tazo bakya nan sai ta nemi Sa'idan akan suyi harkar ita kuma ta'ki amince mata."
Wani irin kuka ta fashe dashi tana salati da tafa hannaye tace."Yanzu irin sharrin da yarinyar nan za tayi min kenan."? Yace." Ki fada min gaskiyar magana ba kuka nace kiyi min ba shin kema kina aikatawa ko kuwa.?
Hanci ta shaqa a fusace! ta miqe tsaye da fad'in "Wallahi tunda yarinyar nan ta kai ni karshe sai na hukuntata har ni za tayi wa sharri na lesbian lallai sai na nuna mata kuskuranta.
Kafin yayi wani yunkuri har ta bude kofar dakin ta fita ya mike da saurin gaske ya bi bayanta yana kiran sunanta, da gudu ta sauka k'asa kai tsaye dakin Sa'ida ta durfafa.
Shaf na manta bayan fitarsa ban rufe kofa ta ba na kwanta bacci ya daukeni kawai sai jin shaqa nayi a makogwarona tari ya sarqe ni na bude ido ina kakari! kafin na ankara naji mari mai zafi a kumatuna.
" Ni zakiyi wa k'azafi Sa'ida ashe baki da mutunci da 'ya'yana da mutuncina amma ki zaunar da mijina marufar asirina uban 'ya'yana kice masa ni 'Yar Lesbian ce."
A mutukar galabaice nace."Ki sakar min wuyana." tana kumfar baki tace."Ba zan saki ba sai kin fada min a inda kika gan ni ina lesbian. "
Nace."A cikin gidanki na kama ki a dakin ki kina lesbian sai me."? Ta sake kawo min mari! na rike hannunta da karfin gaske na ture ta na sauko daga gadon ina haki nace."Idan bakya lesbian din meye naki na tayar da hankali."
Tayo kaina tana ihu! nace."Wallahi kika kuskura kika doke ni sai na zubar miki da hakora."Kuka tasa a daidai lokacin daya shigo dakin take fad'in "Amma wannan yarinya kin cuce ni wallahi sai Allah ya sake min gida kuma zan fita na barshi tunda kinfi bukatar haka.
Nace." Idan kin tafi kin bar gidanki da 'ya'yanki kanki kika cuta ba wani ba.
Ta kalleshi tana kuka da fad'in "Alhaji kaga irin abunda nake nuna maka ko? dama nasan sai haka ta faru tunda nasan duk wata mace da zaka aura burinta ta shigo ta rabani da kai shikkenan tunda abin ya kasance a haka ni zan tafi gida domin ba zan zauna ba."
Tana gama maganarta ta bude kofa ta fita, zuwa yayi ya zauna kusa dani yana goge gumi nace."Alhaji kada ka bari ta tafi gidansu kaje ka hanata"
Yace."Sa'ida ki 'kyaleta taje jikina na bani maganarki akwai alamun gaskiya a ciki taje kawai sai nayi binkice."
Jikina yayi sanyi da jin abinda ya fada hakika da nasan haka zata faru da ban fada masa ba domin bana so ta sanadiyar al'amarin auransu ya samu matsala nafi bukatar ta shiryu su cigaba da zama mai tsafta a tsakaninsu.
Aunty Murja kwananta biyu a gidansu mahaifinta ya nemeshi da su tattauna...............Kima da darajar dattijon tasa shi janye kudirinsa akanta domin da yayi niyyar datse igiyar auranta sai kuma dattijon ya bashi tausayi ya hakura amma kafin ta dawo gidan sai da yayi mata gargadi akan cewa babu ita babu hajiya Aziza duk sanda ya sake ganin matar a gidansa to ta tabbatar kwanan auranta dashi ya 'kare."
Tunda ta dawo gidan ta tsiri gaba dani ko na gaisheta bata amsawa ni kuwa da yake ban iya gaba ba ko na fara ajiyewa nake nai mata magana tsakanina da yaran ta babu wata matsala hakanan tsakanina da mijina ma sai godiyar Allah dan yanzu na fahimci halinsa 'bangaran auratayya ma yana kokari yanzu dan bana ta'ba bari ya sauka daga kaina sai na biya bukatata yanzu ya saba da jarabata yana kuma kokari akan hakan.
Ranar Lahadi Khalid yazo min gida wai yazo yayi min sallama zai koma Lego's ni dai tunda ya shigo gidan gabana yake fad'uwa! na kalleshi da fadin."A maimakon ka kira ni a waya kayi min sallama sai kuma kazo min gida kasan dai bani kadai bace ko."?
Yana min wani irin kallo yace."Me kika d'auke ni ne ? bake kadai bace to ina ruwana da kishiyarki ni gurunki nazo muyi sallama ba zuwa nayi na kalli kishiyarki ba.
Ina kokarin zama naji tana fad'in "Sa'ida yau Hajia Aziza tazo ko.''? Nace."Eh tazo." Tace."Wallahi sai da na fita na tuna ashe ban fada mata zani unguwa ba kuma nayi ta kiran wayarta domin na sheda mata wayar ta'ki shiga."
Nace."Eh itama haka tace har nace ta biki gidan biki tace Aa ba zataje ba."
D'an murmushi tayi da fad'in "Hajiya Aziza kenan." cikin zuciyata nace "Gafalallu insha Allahu sai Allah ya tona muku asiri.
Mintina goma sha biyar na kammala cin abincina na mike a nutse na bar gurin. dakina na nufa Yusura tace." Aunty yanzu zasu saka *TARKO KAUNA* Naga zaki shiga daki yau ba zaki kalla ba.'' Ba tare dana juyo ba nace."Yusura yau bacci nake ji na kalli maimaici ranar lahadi.'' Tace."To shikkenan aunty Sai da safe." na amsa da Allah ya tashemu lafiya.
Ina kokarin shiga bargo ya shigo dakin ya tsaya a kaina zaune na mike ina kallonsa yace."Wulakancin naki har akan 'ya'yana zaki gwada.
Nace."Ban fahimci maganarka ba." A hasale yace."Yarinyar nan Yusura tana miki magana sabida kina ji da isa da iko ki gagara kallon inda take shin dame kike takama ne."?
Murmushin takaici nayi nace."Bana takama da kowa sai Allah da ma'aiki'' Da sauri yace."Ki kiyaye b'ata ran d'aya daga cikin iyalina kinji ko baki ji ba."
Nace."Naji yanzu Ita Yusuran ce ta turo ka kazo ka sauke min ashafa ko kuma uwarta ce."? Kallona yayi da fad'in "Zakiyi min rashin kunyar da kika saba ne."
Nace."Ai gaskiya ce sabida nasan wannan hayaniyar da kazo kana yi min ba tunaninka bane turo ka akayi."
Hannu ya daga zai kwada min mari na kauce da sauri ya mari iska.
Yana huci yace."Wai me yasa kika raina ni Sa'ida me kika mayar dani a cikin gidana."
Cike da takaici nace."Alhaji kaine kasa kima da mutuncinka duk suka zube a idona kasan Allah a yanzu dai sai dai kawai na kalleka domin kayi min bazata ban ta'ba zaton zan shigo gidanka nayi irin wannan rayuwar ba."
Yace." Wannan rayuwar kuma ki rubuta ki ajiye yanzu kika fara ni haka tsarina yake a gidana babu wata macan data isa tace min ga yanda zanyi 'karya take.
Dariya ya bani na kalleshi yana tsaye a kaina sai daga murya sama yake nace."Yanzu dai magana ta wuce akan na 'ki zaman falo aka zuga ka kazo kaci min mutunci to naji na dauka nayi laifi kayi hakuri."
Shuru yayi yana sauke ajiyar zuciya, Nace."Ka zauna inaso muyi magana. a watse ya kalleni da fadin"Kin san ba girkin bane ko."? Nace."Eh na sani ai ba wata doguwar magana zamuyi ba.
Zama yayi kusa dani yana kallona. Nace."Kasan me? a ya mutse yace."Sai kin fada." Nace."Ka hana wannan matar zuwa gidan ka ina nufin hajiya Aziza 'kawar aunty Murja."
"A kan wane dalili zan hanata zuwa."? Yayi maganar tare da tsareni da idonsa.
Nace." Ba alkairi ne yake kawo ta gidan ba tana zuwa ta hana mala'ikun rahama shigowa gidanka sabida haka ka hanata zuwa shi yafi alkairi.
"Ba zan hana ta shigowa gidana ba sai naji dalilin ki." ajiyar zuciya na saukw idona akansa nace." *'YAR MADIGO (LESBIAN)* ce."
Wani irin kallo yake min kafin yace."Shine me? dan Aziza tana Lesbian sai kike zargin Matata Murja.''?
Cike da karsashi da kwarin gwiwa nace."Kwarai kuwa dole nayi zarginta saboda tayi abinda zai janyo hakan Hajiya Aziza a sati sai tazo sau uku ko sau hudu sannan idan suka hau sama suka rufe kofa sai yamma suke saukowa."
Shuru yayi kansa a 'kasa na cigaba da cewa''Yau tazo gidan lokacin Aunt Murja ta tafi gidan biki ni kuma ina daki ina bacci ta shigo ta same ni ...........Duk abinda ya faru ta kwashe kaf ta fad'a masa.
Wani irin gumi! ne yake karyo masa ya dinga kallona bakinsa na rawa da alama magana yake so yayi amma tsabar rud'u ya hana shi cewa komai.
Nace."Dan Allah ka fahimci maganata kuma ka yanke hukuncin daya dace wallahi tallahi banyi musu sharri ba.
Da 'kyar ya iya fadin"Sa'ida a gidan nawa ake aikata wannan kafurcin tsayin shekaru ban sani ba.
Ajiyar zuciya na sauke nace."Yau ne Allah yaso kasan abinda yake faruwa saboda haka sai kayi namijin kokari gurin ganin ka kori wannan masifar da ta kunno maka a gida.
Mi'kewa yayi ya kama hanyar fita yana tafiya yana had'a hanya babu shakka al'amarin yayi masifar saka shi cikin rud'u da tashin hankali mai tsanani.
Tana kwance a gado cikin kayan bacci masu fitar da tsaraici ya shiga dakin sama-sama ta amsa sallamarsa domin taji masifar haushin zaman da yayi a dakin Sa'ida.
Ya nemi gefan gado ya zauna yana kallonta a burkice!
Zaune ta mi'ke had'e da ajiye wayar hannunta tace."Lafiya na ganka ka shigo a burkice wani abun ne ya faru."?
Ya kalleta da jajayan idanunsa yace."Murja ashe dama ha'intata kikeyi."? da sauri tace."Wace irin magana ce wannan."? Hannu ya daga mata a kaushashe! yace." Menene tsakanin ki da wannan matar dake zuwa gurunki.?
Gabanta ne ya fad'i baki na rawa tace."Wace mata kake magana."?
Yace."Hajiya Aziza matar da kuka had'u da ita a fece book." Ajiyar zuciya ta sauke tace."Alhaji babu abunda yake tsakanina da Aziza sai mutumci da zumunci."
Yace."Ban yarda da maganarki ba Murja kina gayyato min 'yar iska gida kuna iskanci yaushe kika zama lalatacciya."?
Cikin firgici tace."Wai ya kake magana a baibai ne ka fito fili ka fada min abinda kake nufi dani."
Yace."Sa'ida ta tabbatar min da cewa" Aziza *'YAR MADIGO (LESBIAN)* ce domin a dazu da tazo bakya nan sai ta nemi Sa'idan akan suyi harkar ita kuma ta'ki amince mata."
Wani irin kuka ta fashe dashi tana salati da tafa hannaye tace."Yanzu irin sharrin da yarinyar nan za tayi min kenan."? Yace." Ki fada min gaskiyar magana ba kuka nace kiyi min ba shin kema kina aikatawa ko kuwa.?
Hanci ta shaqa a fusace! ta miqe tsaye da fad'in "Wallahi tunda yarinyar nan ta kai ni karshe sai na hukuntata har ni za tayi wa sharri na lesbian lallai sai na nuna mata kuskuranta.
Kafin yayi wani yunkuri har ta bude kofar dakin ta fita ya mike da saurin gaske ya bi bayanta yana kiran sunanta, da gudu ta sauka k'asa kai tsaye dakin Sa'ida ta durfafa.
Shaf na manta bayan fitarsa ban rufe kofa ta ba na kwanta bacci ya daukeni kawai sai jin shaqa nayi a makogwarona tari ya sarqe ni na bude ido ina kakari! kafin na ankara naji mari mai zafi a kumatuna.
" Ni zakiyi wa k'azafi Sa'ida ashe baki da mutunci da 'ya'yana da mutuncina amma ki zaunar da mijina marufar asirina uban 'ya'yana kice masa ni 'Yar Lesbian ce."
A mutukar galabaice nace."Ki sakar min wuyana." tana kumfar baki tace."Ba zan saki ba sai kin fada min a inda kika gan ni ina lesbian. "
Nace."A cikin gidanki na kama ki a dakin ki kina lesbian sai me."? Ta sake kawo min mari! na rike hannunta da karfin gaske na ture ta na sauko daga gadon ina haki nace."Idan bakya lesbian din meye naki na tayar da hankali."
Tayo kaina tana ihu! nace."Wallahi kika kuskura kika doke ni sai na zubar miki da hakora."Kuka tasa a daidai lokacin daya shigo dakin take fad'in "Amma wannan yarinya kin cuce ni wallahi sai Allah ya sake min gida kuma zan fita na barshi tunda kinfi bukatar haka.
Nace." Idan kin tafi kin bar gidanki da 'ya'yanki kanki kika cuta ba wani ba.
Ta kalleshi tana kuka da fad'in "Alhaji kaga irin abunda nake nuna maka ko? dama nasan sai haka ta faru tunda nasan duk wata mace da zaka aura burinta ta shigo ta rabani da kai shikkenan tunda abin ya kasance a haka ni zan tafi gida domin ba zan zauna ba."
Tana gama maganarta ta bude kofa ta fita, zuwa yayi ya zauna kusa dani yana goge gumi nace."Alhaji kada ka bari ta tafi gidansu kaje ka hanata"
Yace."Sa'ida ki 'kyaleta taje jikina na bani maganarki akwai alamun gaskiya a ciki taje kawai sai nayi binkice."
Jikina yayi sanyi da jin abinda ya fada hakika da nasan haka zata faru da ban fada masa ba domin bana so ta sanadiyar al'amarin auransu ya samu matsala nafi bukatar ta shiryu su cigaba da zama mai tsafta a tsakaninsu.
Aunty Murja kwananta biyu a gidansu mahaifinta ya nemeshi da su tattauna...............Kima da darajar dattijon tasa shi janye kudirinsa akanta domin da yayi niyyar datse igiyar auranta sai kuma dattijon ya bashi tausayi ya hakura amma kafin ta dawo gidan sai da yayi mata gargadi akan cewa babu ita babu hajiya Aziza duk sanda ya sake ganin matar a gidansa to ta tabbatar kwanan auranta dashi ya 'kare."
Tunda ta dawo gidan ta tsiri gaba dani ko na gaisheta bata amsawa ni kuwa da yake ban iya gaba ba ko na fara ajiyewa nake nai mata magana tsakanina da yaran ta babu wata matsala hakanan tsakanina da mijina ma sai godiyar Allah dan yanzu na fahimci halinsa 'bangaran auratayya ma yana kokari yanzu dan bana ta'ba bari ya sauka daga kaina sai na biya bukatata yanzu ya saba da jarabata yana kuma kokari akan hakan.
Ranar Lahadi Khalid yazo min gida wai yazo yayi min sallama zai koma Lego's ni dai tunda ya shigo gidan gabana yake fad'uwa! na kalleshi da fadin."A maimakon ka kira ni a waya kayi min sallama sai kuma kazo min gida kasan dai bani kadai bace ko."?
Yana min wani irin kallo yace."Me kika d'auke ni ne ? bake kadai bace to ina ruwana da kishiyarki ni gurunki nazo muyi sallama ba zuwa nayi na kalli kishiyarki ba.