Sashe 78
Ga Irinta Nan Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Hannunta na rawa ta dauki d'an karamin kofin data shigo dashi dakin tasa masa a bakinsa da fadin."Ga magani na had'a maka kasha zakaji sassauci."
Hannunsa ya d'ora akan nata ya shanye ruwan lemon tsamin tas sai wani irin gumi yake jikinsa na wani irin rawa.
Ya kai kimanin rabin awa a dakin kafin ya samu sassauci yace wanka zaiyi Gwaggo da kanta ta had'a masa ruwan wanka ya shiga yayi ya daura alwala ya nufi massalaci.
Gwaggo kuwa ta kudurci wani abu a zuciyarta tana ganin shine maslaha ga rayuwar jikokin nata.
*****
Bayan sati hudu Khalid yayi tafiya zuwa kasar chadi inda k'ungiyar *Manchester* na kasar suka gayyace shi wasa a babban filin wasan su dake kasar....Tafiyarsa kasar Chadi tasa hankalina ya kwanta na sake a gidan ina sabgogina wanda ada bana iya sakewa ina yi saboda yanda yake takurawa rayuwata.
Ranar wata Alhamis muna zaune nida Gwaggo muna hira tace."Sa'ida ni kuwa me zai hana ki rabu da zawarawan nan dake bibiyar ki."
Nace."Me yasa kika ce haka Gwaggo.''? a nutse tace."Kwanakin baya da muna magana da Babanku Ibrahim akan lamarin auranki sai yake cewa da zaki amince da auran Khalid da yaji dadi yana ganin kamar idan kin auri yaron matsalar ki tazo karshe to nima hankali na yafi kwanciya da ki auri dan uwanki domin kwata-kwata bana sha'awar ki koma gidan Aminu ko Alhaji Nura domin gidan jiya zaki koma.
Shuru nayi na minti biyu kafin nace."Gwaggo yanda yaron nan yake nunawa kamar yafi k'arfi na bana so azo ayi abu rayuka suna 'baci kin san dai Ummatu bata k'aunata ko."
Tace."Sa'ida Rabi bata isa ta hana abinda Allah ya hukunta ba ki kwantar da hankalin ki kuma khalid karya yake yace yafi karfin ki shin ko baki ga yarinyar da zai aura bane? kin fita komai na mata saboda haka ni yanxu amincewarki kawai nake bukata."
Ajiyar zuciya na sauke nace."Shikkenan Gwaggo Allah ya za'ba abinda yafi alkairi." Cike da jin dadi ta amsa da ameeen insha Allahu dake dashi zakuyi farin cikin wannan al'amarin.
Cikin zuciyata na amsa da "Allah yasa haka."
To bayan ya dawo gida da kwana biyu Gwaggo ta kirashi domin ta sheda masa halin da ake ciki..........Shuru yayi bayan ya gama sauraranta tace."Jarumi kayi shuru ko ba zaka aureta ba."?
Babu wata alamar farin ciki a tare dashi yace."Gwaggo don Allah ku bar maganar nan ni bana da ra'ayin auran bazawara a halin yanzu."
Gwaggo taji kamar ya soka mata wuka a makoshi murya na rawa tace."Abinda za kace kenan.''? shuru yayi yana duba wayarsa.
Wulakantaccen kallo nayi masa nace."Khalid ba fa kaine autan maza a duniya ba kada ka dauka rasa mijin aure nayi A'a duk wannan abinda ake ina bin umarnin iyayena ne bani da wata damuwa idan baka aureni ba sai me? akwai dubban mazan da suka fika komai a duniya."
Ba tare da ya kalle ni ba yace."An san da haka me yasa aka zo ana min magiya da 'yar murya kije ki auri maza dubu bai dami Khalidu ba."
Hawayen bakin ciki suka ciko idona nace." Kana cewa ba zaka auri bazawara ba tun farko wane shegen ne ya lalata min rayuwa ."?
Kallona yayi yana huci! yace."Ni kike zagi."? a harzuke! nace."Eh na zage ka ko zaka rama ne."?
Gwaggo ganin al'amarin yayi zafi sai ta shiga tsakani rai a bace tace."Ka tashi ka tafi tunda ba zaka bi umarnina ba babu komai."
Mi'kewa yayi ba tare da wata damuwa ba ya fice daga dakin......Takaici da bakin ciki suka taru sukayi min yawa. kwanciya nayi kasan kafet hawaye masu zafi suka dinga zuba a saman fuskata.
*98*
"Ki daina kuka kina damun kanki komai abinsa sai ya had'aku ku biyu ya aura mutukar yana kaunar zaman lafiyarsa."
Zaune na mike ina kallonta da sauran hawayen a idona nace."Gwaggo don Allah ku rabu da yaron nan tunda baya so babu dole a cikin al'amarin nan insha Allahu Allah zai kawo min miji daidai da rayuwata na aura."
Girgiza kanta tayi tace."Sa'ida insha Allahu baki da miji sai Khalid na gaji da wannan al'amarin shima tsiya ce kawai amma yana sonki yana so ya 'bata mana rai ne saboda haka kada ki damu Khalid ko yana so ko baya so sai ya had'aku ku biyu ya aura."
Ina kokarin magana Kawu ya shigo dakin ya shirya cikin manya kaya da alama fita za'ayi hankalinsa a kaina suka gaisa da Gwaggo
A sanyaye na gaishe na sunkuyar da kaina ina wasa da yatsun hannuna.....Cikin rashin jin dadi yace."Sa'ida ina fatan lafiya naga idonki yayi jawur wani abu ya faru ne."?
Hawaye ne suka zubo min nasa hannu na goge ina girgiza kaina.
Gwaggo tace."Ya zaki girgiza kai bayan akwai dalili." Kallonsa tayi da fadin." Yanzu nan Jarumi ya fita bayan ya gama rashin arziki na zaunar dashi na sheda masa hukuncin da muka yanke kai tsaye yace shi ba zai aureta ba shine abin yayi mata ciwo take kuka."
Kawu Ransa ya 'baci yace."To tunda haka ya za'ba shikkenan itama Jamilan ba zai aureta ba sai yaje ya nemi wata." yana gama maganarsa ya bar gurin cikin bacin rai.
Gwaggo tace."Hakan shine hukunci dama ai ba kowa ne yake zuga shi ba sai uwarsa da 'yan uwanta to itama Jamilan sai dai ta hakura yaje ya nemi auran a wani wajen.''
Ummatu tana share hawaye ta d'aga labulan dakin tace"Gwaggo wallahi ni bani na hana yaron nan auran 'yar uwarsa ba ku daina daukar alhakina.''
Gwaggo tace."To idan bake bace wacece Rabi aini babu abinda zance dake tunda dai bakya so ya yaron ki ya auri Sa'ida to itama Jamila sai ta ha'kura haka shi yafi alkairi."
Hawaye ta share da fad'in "Ni dai kiyi masa magana ya janye maganar yi min kishiya meye laifina a cikin al'amarin da har za'ayi min kishiya."
Gwaggo murmushi tayi tace."Ai ba zan hana abinda Allah ya halasta ba Rabi ke kin kasa tursasa d'anki ni kuma sai kizo ki sani na tauyewa d'ana rayuwa idan mata uku zai aura ba zan hana shi ya more rayuwarsa ba."
Ummatu hankalinta yayi masifar tashi tana kuka ta koma sashenta, zama tayi tana tunanin mafita babu shakka dole ta zauna da yaron akan al'amarin dan tana ji tana gani ba zata bari ayi mata kishiya ba.
Sai can dare ya dawo gidan yana kokarin bude dakinsa ta fito daga daki ya kalleta da mamaki a tare dashi yace."Umma baki bacci ba.'?
Tace."Eh na zauna zaman jiran shigowarka.''
Yace."To Allah yasa lafiya." Ajiyar zuciya ta sauke kafin tace."Khalid babanka duk ya sheda min abinda yake faruwa ashe sun yanke maka hukuncin auran Sa'ida ban sani ba."
Yace."Eh nima dazu Gwaggo ke sheda min sai dai na nuna mata cewa bana ra'ayin hakan."
Tace."Ka aureta na baka Umarnin hakan." Wani sanyi yaji ya sauka a zuciyarsa dama abinda yake so yaji kenan daga gurinta.
Ya nuna kamar baya murna da al'amarin yace."Umma kina ganin babu matsala ba naso keda ita ku dinga samun matsala tunda jininku bai had'u ba."
Tace."Babu matsala mutukar zaka nuna mata cewa ni mai muhimmanci ce to zamu zauna lafiya."
Yace."Umma ba zan iya had'a ki da kowa ba saboda ke mahaifiyata ce babu wata 'ya mace da zan aura ta wulakanta min ke sabida haka ki kwantar da hankalin insha Allah ba zan bari ki wulakanta ba."
Murmushin jin dadi tayi tace."To nagode yaron kirki bari na kawo maka abinci." Yace."To nagode Ummana." kicin ta nufa shi kuma yana murmushin jin dadi ya bud'e dakinsa ya shiga cike da nishadi ya cire kayan jikinsa domin ya watsa ruwa.
Washe gari da safe kafin ma mahaifinsa ya tare shi da maganar shi ya rigashi bayan sun gaisa yake sheda masa da cewa ya amince zai had'asu su biyun ya aura.
Yace." Hakan shine yafi maka alkairi da zaman lafiya saboda haka sai ka fara shirye-shirye domin ba zamu ja dogon lokaci ba.''
Yace."Insha Allahu komai za'ayi komai cikin nutsuwa da kwanciyar hankali." Kawu barin sa yayi a tsugune a gurin ya shige daki......Mikewa yayi ya nufi kofar Gwaggo domin su gaisa.
Kawu ya kalleta da fadin." Kin Umarci Yaron nan da ya amince da bukatarmu ko."? shuru tayi tana kallonsa yace."To ki sani hakan da kikayi ba zai hana ni na 'kara aure ba domin tuntuni mun riga mun gama daidaitawa da matar da zan aura dan haka sai ki shiga nutsuwarki." Ummatu baki a sake take kallonsa har ya gama abinda yake ya fita daga dakin......Jiki a masifar sanyaye ta nemi guri ta kwanta tana sak'awa da kwancewa tunda take bata ta'ba tsammanin Mijinta zai iya yi mata kishiya ba, hawaye masu zafin gaske suka dinga sauka a fuskatarta.
Khalid yana can dakin Gwaggo yana neman magana lokacin daya shiga dakin tana bandaki wayarta ya hango kan gado yaje ya dauka yana mata binkice duk number da ba tayi masa ba sai da ya goge sai tsaki yake ja yana girgiza kai.......Cikin wannan yanayin ta shiga dakin ta sameshi.
Hannu ta mike ba tare da tayi masa magana ba. ya harari hannun tsaki yaja ya cigaba da abinda yake da wayar.
Da karfi ta fizge wayar daga hannunsa ta fad'i gurin dake tayi wawar faduwa a take komai yayi pieces a gurin.
Gwaggo tace."Subahanallahi wai me yake damun ku ne sai kuyi ta fad'a sai kace tsofaffin karnuka a haka zakuyi auran."
Ba tare da yace komai ba ya mike zai fita daga dakin da sauri na wafci wayarsa dake aljihun gaban rigarsa ban tsaya jiran komai ba na buga ta da bango." Gabad'aya ta watse a gurin.
Ido jawur yake kallona "Kin san kudin wayar nan kuwa zaki buga min ita da bango(garu)
Hannu na daga masa da fadin." Kaga ban bukaci sanin kudin wayarka ba kawai ka daina shiga sabga ta meye zaka daukar min waya kana duba min."
Rai a 'bace yace.''Dole nayi bunkice a wayarki saboda nasan baki da gaskiya ina so ki daina hurd'a da kowane namiji mutukar kina bukatar ki zauna lafiya."
"Ko an daura min aure da kai baka isa ka hana ni mu'amula da wanda ya cancanta ba namiji ko mace so saboda haka wannan abin bashi ne mafita ba."
Hannunsa ya d'ora akan nata ya shanye ruwan lemon tsamin tas sai wani irin gumi yake jikinsa na wani irin rawa.
Ya kai kimanin rabin awa a dakin kafin ya samu sassauci yace wanka zaiyi Gwaggo da kanta ta had'a masa ruwan wanka ya shiga yayi ya daura alwala ya nufi massalaci.
Gwaggo kuwa ta kudurci wani abu a zuciyarta tana ganin shine maslaha ga rayuwar jikokin nata.
*****
Bayan sati hudu Khalid yayi tafiya zuwa kasar chadi inda k'ungiyar *Manchester* na kasar suka gayyace shi wasa a babban filin wasan su dake kasar....Tafiyarsa kasar Chadi tasa hankalina ya kwanta na sake a gidan ina sabgogina wanda ada bana iya sakewa ina yi saboda yanda yake takurawa rayuwata.
Ranar wata Alhamis muna zaune nida Gwaggo muna hira tace."Sa'ida ni kuwa me zai hana ki rabu da zawarawan nan dake bibiyar ki."
Nace."Me yasa kika ce haka Gwaggo.''? a nutse tace."Kwanakin baya da muna magana da Babanku Ibrahim akan lamarin auranki sai yake cewa da zaki amince da auran Khalid da yaji dadi yana ganin kamar idan kin auri yaron matsalar ki tazo karshe to nima hankali na yafi kwanciya da ki auri dan uwanki domin kwata-kwata bana sha'awar ki koma gidan Aminu ko Alhaji Nura domin gidan jiya zaki koma.
Shuru nayi na minti biyu kafin nace."Gwaggo yanda yaron nan yake nunawa kamar yafi k'arfi na bana so azo ayi abu rayuka suna 'baci kin san dai Ummatu bata k'aunata ko."
Tace."Sa'ida Rabi bata isa ta hana abinda Allah ya hukunta ba ki kwantar da hankalin ki kuma khalid karya yake yace yafi karfin ki shin ko baki ga yarinyar da zai aura bane? kin fita komai na mata saboda haka ni yanxu amincewarki kawai nake bukata."
Ajiyar zuciya na sauke nace."Shikkenan Gwaggo Allah ya za'ba abinda yafi alkairi." Cike da jin dadi ta amsa da ameeen insha Allahu dake dashi zakuyi farin cikin wannan al'amarin.
Cikin zuciyata na amsa da "Allah yasa haka."
To bayan ya dawo gida da kwana biyu Gwaggo ta kirashi domin ta sheda masa halin da ake ciki..........Shuru yayi bayan ya gama sauraranta tace."Jarumi kayi shuru ko ba zaka aureta ba."?
Babu wata alamar farin ciki a tare dashi yace."Gwaggo don Allah ku bar maganar nan ni bana da ra'ayin auran bazawara a halin yanzu."
Gwaggo taji kamar ya soka mata wuka a makoshi murya na rawa tace."Abinda za kace kenan.''? shuru yayi yana duba wayarsa.
Wulakantaccen kallo nayi masa nace."Khalid ba fa kaine autan maza a duniya ba kada ka dauka rasa mijin aure nayi A'a duk wannan abinda ake ina bin umarnin iyayena ne bani da wata damuwa idan baka aureni ba sai me? akwai dubban mazan da suka fika komai a duniya."
Ba tare da ya kalle ni ba yace."An san da haka me yasa aka zo ana min magiya da 'yar murya kije ki auri maza dubu bai dami Khalidu ba."
Hawayen bakin ciki suka ciko idona nace." Kana cewa ba zaka auri bazawara ba tun farko wane shegen ne ya lalata min rayuwa ."?
Kallona yayi yana huci! yace."Ni kike zagi."? a harzuke! nace."Eh na zage ka ko zaka rama ne."?
Gwaggo ganin al'amarin yayi zafi sai ta shiga tsakani rai a bace tace."Ka tashi ka tafi tunda ba zaka bi umarnina ba babu komai."
Mi'kewa yayi ba tare da wata damuwa ba ya fice daga dakin......Takaici da bakin ciki suka taru sukayi min yawa. kwanciya nayi kasan kafet hawaye masu zafi suka dinga zuba a saman fuskata.
*98*
"Ki daina kuka kina damun kanki komai abinsa sai ya had'aku ku biyu ya aura mutukar yana kaunar zaman lafiyarsa."
Zaune na mike ina kallonta da sauran hawayen a idona nace."Gwaggo don Allah ku rabu da yaron nan tunda baya so babu dole a cikin al'amarin nan insha Allahu Allah zai kawo min miji daidai da rayuwata na aura."
Girgiza kanta tayi tace."Sa'ida insha Allahu baki da miji sai Khalid na gaji da wannan al'amarin shima tsiya ce kawai amma yana sonki yana so ya 'bata mana rai ne saboda haka kada ki damu Khalid ko yana so ko baya so sai ya had'aku ku biyu ya aura."
Ina kokarin magana Kawu ya shigo dakin ya shirya cikin manya kaya da alama fita za'ayi hankalinsa a kaina suka gaisa da Gwaggo
A sanyaye na gaishe na sunkuyar da kaina ina wasa da yatsun hannuna.....Cikin rashin jin dadi yace."Sa'ida ina fatan lafiya naga idonki yayi jawur wani abu ya faru ne."?
Hawaye ne suka zubo min nasa hannu na goge ina girgiza kaina.
Gwaggo tace."Ya zaki girgiza kai bayan akwai dalili." Kallonsa tayi da fadin." Yanzu nan Jarumi ya fita bayan ya gama rashin arziki na zaunar dashi na sheda masa hukuncin da muka yanke kai tsaye yace shi ba zai aureta ba shine abin yayi mata ciwo take kuka."
Kawu Ransa ya 'baci yace."To tunda haka ya za'ba shikkenan itama Jamilan ba zai aureta ba sai yaje ya nemi wata." yana gama maganarsa ya bar gurin cikin bacin rai.
Gwaggo tace."Hakan shine hukunci dama ai ba kowa ne yake zuga shi ba sai uwarsa da 'yan uwanta to itama Jamilan sai dai ta hakura yaje ya nemi auran a wani wajen.''
Ummatu tana share hawaye ta d'aga labulan dakin tace"Gwaggo wallahi ni bani na hana yaron nan auran 'yar uwarsa ba ku daina daukar alhakina.''
Gwaggo tace."To idan bake bace wacece Rabi aini babu abinda zance dake tunda dai bakya so ya yaron ki ya auri Sa'ida to itama Jamila sai ta ha'kura haka shi yafi alkairi."
Hawaye ta share da fad'in "Ni dai kiyi masa magana ya janye maganar yi min kishiya meye laifina a cikin al'amarin da har za'ayi min kishiya."
Gwaggo murmushi tayi tace."Ai ba zan hana abinda Allah ya halasta ba Rabi ke kin kasa tursasa d'anki ni kuma sai kizo ki sani na tauyewa d'ana rayuwa idan mata uku zai aura ba zan hana shi ya more rayuwarsa ba."
Ummatu hankalinta yayi masifar tashi tana kuka ta koma sashenta, zama tayi tana tunanin mafita babu shakka dole ta zauna da yaron akan al'amarin dan tana ji tana gani ba zata bari ayi mata kishiya ba.
Sai can dare ya dawo gidan yana kokarin bude dakinsa ta fito daga daki ya kalleta da mamaki a tare dashi yace."Umma baki bacci ba.'?
Tace."Eh na zauna zaman jiran shigowarka.''
Yace."To Allah yasa lafiya." Ajiyar zuciya ta sauke kafin tace."Khalid babanka duk ya sheda min abinda yake faruwa ashe sun yanke maka hukuncin auran Sa'ida ban sani ba."
Yace."Eh nima dazu Gwaggo ke sheda min sai dai na nuna mata cewa bana ra'ayin hakan."
Tace."Ka aureta na baka Umarnin hakan." Wani sanyi yaji ya sauka a zuciyarsa dama abinda yake so yaji kenan daga gurinta.
Ya nuna kamar baya murna da al'amarin yace."Umma kina ganin babu matsala ba naso keda ita ku dinga samun matsala tunda jininku bai had'u ba."
Tace."Babu matsala mutukar zaka nuna mata cewa ni mai muhimmanci ce to zamu zauna lafiya."
Yace."Umma ba zan iya had'a ki da kowa ba saboda ke mahaifiyata ce babu wata 'ya mace da zan aura ta wulakanta min ke sabida haka ki kwantar da hankalin insha Allah ba zan bari ki wulakanta ba."
Murmushin jin dadi tayi tace."To nagode yaron kirki bari na kawo maka abinci." Yace."To nagode Ummana." kicin ta nufa shi kuma yana murmushin jin dadi ya bud'e dakinsa ya shiga cike da nishadi ya cire kayan jikinsa domin ya watsa ruwa.
Washe gari da safe kafin ma mahaifinsa ya tare shi da maganar shi ya rigashi bayan sun gaisa yake sheda masa da cewa ya amince zai had'asu su biyun ya aura.
Yace." Hakan shine yafi maka alkairi da zaman lafiya saboda haka sai ka fara shirye-shirye domin ba zamu ja dogon lokaci ba.''
Yace."Insha Allahu komai za'ayi komai cikin nutsuwa da kwanciyar hankali." Kawu barin sa yayi a tsugune a gurin ya shige daki......Mikewa yayi ya nufi kofar Gwaggo domin su gaisa.
Kawu ya kalleta da fadin." Kin Umarci Yaron nan da ya amince da bukatarmu ko."? shuru tayi tana kallonsa yace."To ki sani hakan da kikayi ba zai hana ni na 'kara aure ba domin tuntuni mun riga mun gama daidaitawa da matar da zan aura dan haka sai ki shiga nutsuwarki." Ummatu baki a sake take kallonsa har ya gama abinda yake ya fita daga dakin......Jiki a masifar sanyaye ta nemi guri ta kwanta tana sak'awa da kwancewa tunda take bata ta'ba tsammanin Mijinta zai iya yi mata kishiya ba, hawaye masu zafin gaske suka dinga sauka a fuskatarta.
Khalid yana can dakin Gwaggo yana neman magana lokacin daya shiga dakin tana bandaki wayarta ya hango kan gado yaje ya dauka yana mata binkice duk number da ba tayi masa ba sai da ya goge sai tsaki yake ja yana girgiza kai.......Cikin wannan yanayin ta shiga dakin ta sameshi.
Hannu ta mike ba tare da tayi masa magana ba. ya harari hannun tsaki yaja ya cigaba da abinda yake da wayar.
Da karfi ta fizge wayar daga hannunsa ta fad'i gurin dake tayi wawar faduwa a take komai yayi pieces a gurin.
Gwaggo tace."Subahanallahi wai me yake damun ku ne sai kuyi ta fad'a sai kace tsofaffin karnuka a haka zakuyi auran."
Ba tare da yace komai ba ya mike zai fita daga dakin da sauri na wafci wayarsa dake aljihun gaban rigarsa ban tsaya jiran komai ba na buga ta da bango." Gabad'aya ta watse a gurin.
Ido jawur yake kallona "Kin san kudin wayar nan kuwa zaki buga min ita da bango(garu)
Hannu na daga masa da fadin." Kaga ban bukaci sanin kudin wayarka ba kawai ka daina shiga sabga ta meye zaka daukar min waya kana duba min."
Rai a 'bace yace.''Dole nayi bunkice a wayarki saboda nasan baki da gaskiya ina so ki daina hurd'a da kowane namiji mutukar kina bukatar ki zauna lafiya."
"Ko an daura min aure da kai baka isa ka hana ni mu'amula da wanda ya cancanta ba namiji ko mace so saboda haka wannan abin bashi ne mafita ba."