Sashe 81
Ga Irinta Nan Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A nutse yace." Ummatu don Allah ku kwantar da hankalin ku tsakanin Sa'ida Jamila babu wacce tafi wata a gurina duk daya suke tunda dukkaninsu zumunci ne mai karfi a tsakanin mu bayan haka ga babban al'amarin da ya ratsa tsakanin mu to ina ganin a halin yanzu duk wasu surutai da 'kanunan magana basu dace ba babban burina shine Allah ya bani ikon rike jagorancin daya bani inaso ku taya ni da addua akan haka.
Jikinsu ne yayi sanyi Baito tace."Addua kam muna yi sai dai muqara akan wata amma dai duk da haka sai ka jajurce ka zama namijin duniya duba da cewa ita Uwargidan naka uwar mata ce ta fika wayo da dubara sannan ta girme ka ta kuma girmi Jamila dole ne ta wani gefan ta cutar daku shiyasa hankalinmu ya kasa kwanciya.
'Bata rai yayi yace."Baito kada ki sake cewa Sa'ida ta girme ni bana so." Baki ta riqe tana kallonsa tace."To ai ko ba'a fad'a ba ido ba mudu ba yasan kima dama dai don ka kwallafa ranka akanta ne amma ai ba sa'ar auranka bace."
Mi'kewa yayi ya dauki wayoyinsa da key ya fita ya basu guri yaji mugun haushin maganar Kakar tashi a ganinsa yanzu maganar girma da shekaru ta kare tunda shine yake gaba da ita a k'arkashinsa take tilas ya kar'be shekarunta ita ta kar'bi nasa.
Gurin Gwaggo ya nufa ya sameta a bakin murhu tana ta dahuwar kaza a cikin madaidaiciyar tukunya.........Cikin rashin jin dadi yace."Gwaggo duk Gas din gidan nan ba zaki amfani dashi ba sai ki kunna ice duba don Allah sai hayaki ne yake tashi a gidan idanuwanki na ruwa wai shin ma me kike girkawa."
Tace."Ai ka bari mu gaisa kafin ka kalubance ni." Guri ya nema ya zauna ta karkad'e tabarma ta shinfida kusa dashi tana kallonsa.....Murmushin jin dadi tayi tace."Ango mijin Sa'ida da Jamila Jarumi D'an gidan Rabi da Ibarahim Jikan Lawali da Ramatu."
Dariya yasa yana kallonta itama tana dariyar tace."Wallahi jiya da kyar nayi bacci saboda tsabar farin ciki ina fatan kun wayi gari lafiya da kai da iyalin naka."?
Yace."Lafiya lau Alhamdulillhi." Tace."To masha Allah ai naji dadin zuwanka dama ina ta tunanin wanda zai kaiwa Sa'ida dawur kazarta."
Yace."Ai ni nan da kika gani sai can dare zan koma gidan......Tace."Don Allah komai dare kazo ka tafi mata abin ba ita kad'ai zai amfana ba harda kai."
Yace."Gwaggo wace irin kaza ce wannan da za'a dauka idan tana so ita tayi farfesun mana." Tace."Ni dai ba doguwar magana na nema da kai ba kawai kace to."
Yace."To naji ita Jamila ba zaki bata kazar ba." Girgiza kanta tayi tace."Kowa kansa ya sani ita wa yasan irin gyaran da iyayenta sukayi mata." Sai da ta fadi maganar sai ya fahimci inda ta dosa Dariya ya dinga kyalkyalawa yana fad'in."Gaskiya nima ban yarda ba sai kin bani maganin kar'fi ai nima jikan ki ne me yasa ba zaki gyara ni domun mataye na suji ni garau ba."
Mifici tasa tana dukansa da fadin." Tashi ka tafi harkokin ka bana son rashin ta ido ai kai tuntuni nasan da cewar Jarumi ne koda za'a tara maka mata dubu sai ka iya dasu."
Khalid ya dinga kyalkyala dariya yana girgiza k'anshi Yana masifar kaunar kakarshi saboda yanda take kaunarsa da damuwa da al'amuransa yasan babu wani abu da zaiyi mata ya biya ta akan irin abinda take masa na aikairi yanda yake jin Gwaggo a cikin ranshi baya jin iyayensa Gwaggo nada kima da daraja a gurinsa.
Ina cikin bedroom d'ina ina gyare-gyare naji motsi a falo da sauri na ajiye abayar dake hannuna na bude kofar dakin na fita.
Ido hudu mukayi da ita tana tsaye a tsakiyar falon ita da wasu 'yan mata guda biyu da alama dai 'kawayenta ne.......Babu walwala a fuskata nace."Ku zauna mana kun tsaya a tsaye sai kalle-kalle kukeyi ko kun ajiye wani abu ne."?
Wani irin kallo tayi min kafin tace."Kinga mu ba zama ne ya kawo mu ba me zamu zauna muyi miki."?
Tsayuwa na gyara ina kallonsu nace."Okey to me ya kawo ku."? Daya daga cikin k'awayen nata tace."Munzo muyi miki warning ne."?
Da mamaki a tare dani nace."Warning kamar yaya."? Dayar tace."Kema ai kin sani aikin banza aikin wofi mutum da girmansa sai zuciyar yara in banda ma abin d'a namiji mai zai ci dake bazawara ragowar mutun biyu."
Wani irin gumi ne ya shiga tsatstsafowa a jikina kawai na zuba musu ido suna ta surutu da fadin duk maganar da tazo bakinsu.
Jamila tace."Suwaiba ku kyaleta naga kamar jikinta yayi sanyi tayi nadamar abinda ta aikata ku muje kawai da alama bata da abin fad'a.
Juyawa sukayi zasu fita da sauri na janyo rigarta dan har sai da wuyan ya yage wawan! mari na kwad'a mata a kumatu.!
Dafe kumatun tayi tana kallona hawaye kuwa tuni sun wanke mata fuska.
A wulakance na kalleta da fad'in."Wallahi ki shiga hankalin ki dani ni zaki shigowa daki ki zaga harda gayyato wasu shashashan k'awayen ki me suka isa su tare miki."
Suwaiba tayi tsagal tace."Aikuwa mun isa mu tare mata aikin banza kawai mugu......Kafin ta 'karasa ta bata nata marin wanda taga gilmawar taurari a cikinsa.
Murya na rawa tace."Kika mare ni."? a fusace! Nace." Idan baku fice min daga guri ba wayar redio zan dauko naci ubanku shashashan yara marasa tarbiya."
Jamila na kuka take fadin." Za kiga abinda zai faru wallahi sai na fanshe marin da kikayi min muguwa azzalima kawai."
Tsawa! mai razanarwa na buga mata da fadin." Ba zaki rufe min wannan ru'babben bakin naki ba ko."? shuru tayi tana kallona nace." Alkairi zan gani da yardar Allah duk wani sharrin ki dana iyayenki zai koma kanku."
Girgiza kanta tayi cikin kunar zuciya ta kama hanyar fita simi-simi suka rufa mata baya ko wacce jikinta yayi sanyi da abinda nayi musu.....Raina a bace na koma cikin dakina na cigaba da abinda nake.
Kimanin awa guda da faruwar al'amarin ya kira waya ta, ina d'aga wa ya fara masifa " Me Jamila tayi miki zaki mareta ita da 'kawayenta Nifa bana son mugunta da neman fitina."
Sassauta murya nayi nace."Kaga ka tsaya ka saurare ni don Allah bana so ka sake tunzura min zuciya.
A dakile yace." To na saurara sai kiyi min bayanin abinda ya faru."
Ajiyar zuciya na sauke cikin nutsuwa na zayyane masa dukkanin abinda ya faru a tsakanin mu.
"Me yasa ba zaki bari na dawo ki fad'a min ba? me yasa zaki dauki mataki a hannunki? ashe ke kike da kanki baki dana gaba dake ko."?
Raina ne ya 'baci da maganarsa Nace." Khalid kana nufin hukunci na beyi daidai ba kenan."?
'Kwarai kuwa baiyi daidai ba kinyi zalinci saboda kin san kinfi k'arfinta shine zaki zage karfi a kanta ki fasa mata baki da hanci."
Tsaki mai karfi naja nace."Tunda nafi karfinta idan ka dawo gidan sai ka rama mata." kashe waya ta nayi ba tare dana saurari abinda yake fad'a ba.
Be shigo gidan ba sai wajan sha d'aya da rabi na dare lokacin ma ni na jima da yin bacci ya jima a gurin Jamila yana lalla'bata da bata hakuri akan abinda Sa'ida tayi mata sai da ya sata dariya sannan yayi mata sallama ya nufi Side din Uwargidan nashi...
*101*
Motsin shigowarsa dakin ne ya farkar dani na miqe zaune ina kallonsa ya a jiye lodojin dake hannunsa, ba tare da yace min komai ba ya nufi toilet kamar na tashi na bishi domin nasan wanka zaiyi na had'a masa ruwa sai wata zuciyar ta kwa'be ina jin tsoron iskancin yaron domin na lura da cewa idan yaga ina masa rawar jiki yafi wulakanci.
Ina zaune ina tunanin rayuwa ya fito daga bandakin daure da towel da karami a hannunsa yana goge jikinsa.
A nutse nace."Sannu da zuwa." Yana tafiya zuwa mirror ya amsa ba tare da ya kalleni ba.
Komawa nayi na kwanta tare da juya bayana, boxer yasa a jikinsa ya had'a da vest wacce ta matse shi kaina yazo ya tsaya yana min magana cikin gadara da Iko.
Zaune na mike ina kallonsa "Ki tashi ki bani abinci." Cikin jin haushi nace "Ka duba daining da akwai komai."
A fusace! yace."Kina nufin ni zanyi hidima da kaina kenan."
Nace."Kaga Khalid bana neman fitina cikin daran nan don Allah idan za kayi min magana ka daina d'aga min murya kana buga min tsawa ba sai kayi haka ba za'a san kai maigida ne."
"Anyi miki tsawar ko zaki mayar da martani ne."? Cike da mamaki na dinga kallonsa sai wani huci yake yana kumfar baki Nace." Akan na mari Jamila ka tsaya a kaina kake kokarin zagi na."
"Eh akan hakane me yasa ba zaki jira na dawo ba ki fad'a min na dauki hukunci da hannu na ko kuma zaman kanki kike."?
Murmushin takaici nayi da fadin." Naga kaji zafin abin abinda za'ayi yanzu kawai ka rama mata marin sai ka huce haushin ka."
Tsaki mai karfi yaja yace."Wannan shine na farko kuma shine na karshe wallahi mutukar kika sake fitar da hannu kika daki yarinyar nan sai na hukunta ki dake da ita dukkaninku Amanar ku a hannuna take."
Kwanciya kawai nayi na kyaleshi yana surutai "Kin raina min mahaifiya sam bakya ganin kima da mutuncin dangi na kina maganar duk sharrin su zai koma kansu me sukayi miki na sharri da har kike fad'in wannan maganar."?
Kaina ne naji yana wani irin ciwo nace."Don darajar Allah ka matsa daga kaina wannan masifar taka ta haddasa min ciwon kai Khalid bana son damuwa naji na amsa laifina shikkenan ko."?
Gurin ya bari yana cigaba da k'ananun maganganu cikin zuciyata nace." Tunda Allah ya riga ya had'a ni zama da mutum mara hakuri dole na dauki kaddara.
Can cikin bacci na na jishi a naniqe a jikina yana kokarin cire min rigar bacci.
Haushi ya turnuke ni Khalid bai da kunya ko kad'an ya gama cin mutuncin na amma yazo yana lalube ni.
Hannunsa na d'auke na matsa can karshen gado.....Janyo ni yayi ya matse a kirjinsa yana wani irin nishi........"Auntyna kiyi min taimako irin na jiya kinji ko."
Shuru nayi masa ina jinsa yana magana kasa-kasa sai kokarin cire min riga yake ina hana shi.
Jikinsu ne yayi sanyi Baito tace."Addua kam muna yi sai dai muqara akan wata amma dai duk da haka sai ka jajurce ka zama namijin duniya duba da cewa ita Uwargidan naka uwar mata ce ta fika wayo da dubara sannan ta girme ka ta kuma girmi Jamila dole ne ta wani gefan ta cutar daku shiyasa hankalinmu ya kasa kwanciya.
'Bata rai yayi yace."Baito kada ki sake cewa Sa'ida ta girme ni bana so." Baki ta riqe tana kallonsa tace."To ai ko ba'a fad'a ba ido ba mudu ba yasan kima dama dai don ka kwallafa ranka akanta ne amma ai ba sa'ar auranka bace."
Mi'kewa yayi ya dauki wayoyinsa da key ya fita ya basu guri yaji mugun haushin maganar Kakar tashi a ganinsa yanzu maganar girma da shekaru ta kare tunda shine yake gaba da ita a k'arkashinsa take tilas ya kar'be shekarunta ita ta kar'bi nasa.
Gurin Gwaggo ya nufa ya sameta a bakin murhu tana ta dahuwar kaza a cikin madaidaiciyar tukunya.........Cikin rashin jin dadi yace."Gwaggo duk Gas din gidan nan ba zaki amfani dashi ba sai ki kunna ice duba don Allah sai hayaki ne yake tashi a gidan idanuwanki na ruwa wai shin ma me kike girkawa."
Tace."Ai ka bari mu gaisa kafin ka kalubance ni." Guri ya nema ya zauna ta karkad'e tabarma ta shinfida kusa dashi tana kallonsa.....Murmushin jin dadi tayi tace."Ango mijin Sa'ida da Jamila Jarumi D'an gidan Rabi da Ibarahim Jikan Lawali da Ramatu."
Dariya yasa yana kallonta itama tana dariyar tace."Wallahi jiya da kyar nayi bacci saboda tsabar farin ciki ina fatan kun wayi gari lafiya da kai da iyalin naka."?
Yace."Lafiya lau Alhamdulillhi." Tace."To masha Allah ai naji dadin zuwanka dama ina ta tunanin wanda zai kaiwa Sa'ida dawur kazarta."
Yace."Ai ni nan da kika gani sai can dare zan koma gidan......Tace."Don Allah komai dare kazo ka tafi mata abin ba ita kad'ai zai amfana ba harda kai."
Yace."Gwaggo wace irin kaza ce wannan da za'a dauka idan tana so ita tayi farfesun mana." Tace."Ni dai ba doguwar magana na nema da kai ba kawai kace to."
Yace."To naji ita Jamila ba zaki bata kazar ba." Girgiza kanta tayi tace."Kowa kansa ya sani ita wa yasan irin gyaran da iyayenta sukayi mata." Sai da ta fadi maganar sai ya fahimci inda ta dosa Dariya ya dinga kyalkyalawa yana fad'in."Gaskiya nima ban yarda ba sai kin bani maganin kar'fi ai nima jikan ki ne me yasa ba zaki gyara ni domun mataye na suji ni garau ba."
Mifici tasa tana dukansa da fadin." Tashi ka tafi harkokin ka bana son rashin ta ido ai kai tuntuni nasan da cewar Jarumi ne koda za'a tara maka mata dubu sai ka iya dasu."
Khalid ya dinga kyalkyala dariya yana girgiza k'anshi Yana masifar kaunar kakarshi saboda yanda take kaunarsa da damuwa da al'amuransa yasan babu wani abu da zaiyi mata ya biya ta akan irin abinda take masa na aikairi yanda yake jin Gwaggo a cikin ranshi baya jin iyayensa Gwaggo nada kima da daraja a gurinsa.
Ina cikin bedroom d'ina ina gyare-gyare naji motsi a falo da sauri na ajiye abayar dake hannuna na bude kofar dakin na fita.
Ido hudu mukayi da ita tana tsaye a tsakiyar falon ita da wasu 'yan mata guda biyu da alama dai 'kawayenta ne.......Babu walwala a fuskata nace."Ku zauna mana kun tsaya a tsaye sai kalle-kalle kukeyi ko kun ajiye wani abu ne."?
Wani irin kallo tayi min kafin tace."Kinga mu ba zama ne ya kawo mu ba me zamu zauna muyi miki."?
Tsayuwa na gyara ina kallonsu nace."Okey to me ya kawo ku."? Daya daga cikin k'awayen nata tace."Munzo muyi miki warning ne."?
Da mamaki a tare dani nace."Warning kamar yaya."? Dayar tace."Kema ai kin sani aikin banza aikin wofi mutum da girmansa sai zuciyar yara in banda ma abin d'a namiji mai zai ci dake bazawara ragowar mutun biyu."
Wani irin gumi ne ya shiga tsatstsafowa a jikina kawai na zuba musu ido suna ta surutu da fadin duk maganar da tazo bakinsu.
Jamila tace."Suwaiba ku kyaleta naga kamar jikinta yayi sanyi tayi nadamar abinda ta aikata ku muje kawai da alama bata da abin fad'a.
Juyawa sukayi zasu fita da sauri na janyo rigarta dan har sai da wuyan ya yage wawan! mari na kwad'a mata a kumatu.!
Dafe kumatun tayi tana kallona hawaye kuwa tuni sun wanke mata fuska.
A wulakance na kalleta da fad'in."Wallahi ki shiga hankalin ki dani ni zaki shigowa daki ki zaga harda gayyato wasu shashashan k'awayen ki me suka isa su tare miki."
Suwaiba tayi tsagal tace."Aikuwa mun isa mu tare mata aikin banza kawai mugu......Kafin ta 'karasa ta bata nata marin wanda taga gilmawar taurari a cikinsa.
Murya na rawa tace."Kika mare ni."? a fusace! Nace." Idan baku fice min daga guri ba wayar redio zan dauko naci ubanku shashashan yara marasa tarbiya."
Jamila na kuka take fadin." Za kiga abinda zai faru wallahi sai na fanshe marin da kikayi min muguwa azzalima kawai."
Tsawa! mai razanarwa na buga mata da fadin." Ba zaki rufe min wannan ru'babben bakin naki ba ko."? shuru tayi tana kallona nace." Alkairi zan gani da yardar Allah duk wani sharrin ki dana iyayenki zai koma kanku."
Girgiza kanta tayi cikin kunar zuciya ta kama hanyar fita simi-simi suka rufa mata baya ko wacce jikinta yayi sanyi da abinda nayi musu.....Raina a bace na koma cikin dakina na cigaba da abinda nake.
Kimanin awa guda da faruwar al'amarin ya kira waya ta, ina d'aga wa ya fara masifa " Me Jamila tayi miki zaki mareta ita da 'kawayenta Nifa bana son mugunta da neman fitina."
Sassauta murya nayi nace."Kaga ka tsaya ka saurare ni don Allah bana so ka sake tunzura min zuciya.
A dakile yace." To na saurara sai kiyi min bayanin abinda ya faru."
Ajiyar zuciya na sauke cikin nutsuwa na zayyane masa dukkanin abinda ya faru a tsakanin mu.
"Me yasa ba zaki bari na dawo ki fad'a min ba? me yasa zaki dauki mataki a hannunki? ashe ke kike da kanki baki dana gaba dake ko."?
Raina ne ya 'baci da maganarsa Nace." Khalid kana nufin hukunci na beyi daidai ba kenan."?
'Kwarai kuwa baiyi daidai ba kinyi zalinci saboda kin san kinfi k'arfinta shine zaki zage karfi a kanta ki fasa mata baki da hanci."
Tsaki mai karfi naja nace."Tunda nafi karfinta idan ka dawo gidan sai ka rama mata." kashe waya ta nayi ba tare dana saurari abinda yake fad'a ba.
Be shigo gidan ba sai wajan sha d'aya da rabi na dare lokacin ma ni na jima da yin bacci ya jima a gurin Jamila yana lalla'bata da bata hakuri akan abinda Sa'ida tayi mata sai da ya sata dariya sannan yayi mata sallama ya nufi Side din Uwargidan nashi...
*101*
Motsin shigowarsa dakin ne ya farkar dani na miqe zaune ina kallonsa ya a jiye lodojin dake hannunsa, ba tare da yace min komai ba ya nufi toilet kamar na tashi na bishi domin nasan wanka zaiyi na had'a masa ruwa sai wata zuciyar ta kwa'be ina jin tsoron iskancin yaron domin na lura da cewa idan yaga ina masa rawar jiki yafi wulakanci.
Ina zaune ina tunanin rayuwa ya fito daga bandakin daure da towel da karami a hannunsa yana goge jikinsa.
A nutse nace."Sannu da zuwa." Yana tafiya zuwa mirror ya amsa ba tare da ya kalleni ba.
Komawa nayi na kwanta tare da juya bayana, boxer yasa a jikinsa ya had'a da vest wacce ta matse shi kaina yazo ya tsaya yana min magana cikin gadara da Iko.
Zaune na mike ina kallonsa "Ki tashi ki bani abinci." Cikin jin haushi nace "Ka duba daining da akwai komai."
A fusace! yace."Kina nufin ni zanyi hidima da kaina kenan."
Nace."Kaga Khalid bana neman fitina cikin daran nan don Allah idan za kayi min magana ka daina d'aga min murya kana buga min tsawa ba sai kayi haka ba za'a san kai maigida ne."
"Anyi miki tsawar ko zaki mayar da martani ne."? Cike da mamaki na dinga kallonsa sai wani huci yake yana kumfar baki Nace." Akan na mari Jamila ka tsaya a kaina kake kokarin zagi na."
"Eh akan hakane me yasa ba zaki jira na dawo ba ki fad'a min na dauki hukunci da hannu na ko kuma zaman kanki kike."?
Murmushin takaici nayi da fadin." Naga kaji zafin abin abinda za'ayi yanzu kawai ka rama mata marin sai ka huce haushin ka."
Tsaki mai karfi yaja yace."Wannan shine na farko kuma shine na karshe wallahi mutukar kika sake fitar da hannu kika daki yarinyar nan sai na hukunta ki dake da ita dukkaninku Amanar ku a hannuna take."
Kwanciya kawai nayi na kyaleshi yana surutai "Kin raina min mahaifiya sam bakya ganin kima da mutuncin dangi na kina maganar duk sharrin su zai koma kansu me sukayi miki na sharri da har kike fad'in wannan maganar."?
Kaina ne naji yana wani irin ciwo nace."Don darajar Allah ka matsa daga kaina wannan masifar taka ta haddasa min ciwon kai Khalid bana son damuwa naji na amsa laifina shikkenan ko."?
Gurin ya bari yana cigaba da k'ananun maganganu cikin zuciyata nace." Tunda Allah ya riga ya had'a ni zama da mutum mara hakuri dole na dauki kaddara.
Can cikin bacci na na jishi a naniqe a jikina yana kokarin cire min rigar bacci.
Haushi ya turnuke ni Khalid bai da kunya ko kad'an ya gama cin mutuncin na amma yazo yana lalube ni.
Hannunsa na d'auke na matsa can karshen gado.....Janyo ni yayi ya matse a kirjinsa yana wani irin nishi........"Auntyna kiyi min taimako irin na jiya kinji ko."
Shuru nayi masa ina jinsa yana magana kasa-kasa sai kokarin cire min riga yake ina hana shi.