← Book details Ga Irinta Nan Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 33 OF 90

Sashe 33

Ga Irinta Nan Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Nace"Gwaggo ki samu nutsuwa dan Allah in sha Allahu Khalid na raye cikin koshin lafiya."

"Kayya! Sa'ida bana tsammanin yaron nan nada rai.'' nace" Bari gari ya waye sai a sake kiran wayar tashi."

Tace."to shikkenan." tagumi! ta zabga har yanzu hawaye take cikin zuciyata nace ko wane irin so da kauna take masa.....Nace"Gwaggo yau ba zaki kunna redio ba."?

Kanta ta girgiza min na dauki redion na kunna mata na ajiye mata kusa da ita.

Dauka tayi tana kokarin kashewa tace."Sa'ida rabu dani nayi salati a zuciyata yau bana sha'awar jin redio nafi bukatar na samu nutsuwar zuciya nayi wa yaron nan addua.

Nace"Hakane Allah ya kare shi." ta amsa da ameeen ya rabbi.'' Mikewa nayi na fita tsakar gida domin d'ora ruwan wanka, sai naji motsin fitowarta na jiyo ina kallonta naga tana sa takalmanta da kudi a hannunta.

Nace"Ina kuma zakije da sassafe haka'' Tace."Zanje gidan Marka mai waina na siya domin nayi wa almajirai sadaka."

Shuru nai ina kallonta har ta fita daga gidan na girgiza kaina tare da cigaba da abinda nake.

Har nayi wanka na fito nasa kaya na Gwaggo bata dawo gidan ba, na zauna cikin damuwa na dauki mai ina shafawa a jikina Kawu Iro ya daga labulan dakin, da sauri na gaisheshi ya amsa cikin kulawa yana fad'in "Gwaggo tana bandaki ne."?

Nace." Aa ta d'an jima da fita wai taje gidan Marka siyo wainar gero."

Yana kokarin magana ta shigo gidan. Kawu Iro Kallo guda yayi wa mahaifiyar tasa jikinsa ya mutu ganin yanda ta zabge idunuwanta sunyi fululu.

Yace."Gwaggo lafiya me yake faruwa."? Hawaye suka 'kwace mata tace."Ibrahim babu lafiya domin kuwa Jiya a zaune na kwana tunda nayi mummunan mafarki da yaron nan Khalid na kasa rintsawa.

Yace."Gwaggo dan Allah ki cire damuwar Khalid daga cikin ranki kada ki janyo wa kanki ciwo mai tsanani.

Tace."Ibrahim idan kaga na cire Khalid a raina to mutuwa nayi amma ba zan ta'ba daina damuwa dashi ba.''

Tana gama maganarta ta wuce gurin Ummatu.

Ummatu na tsaka da dama kunu ta ganta ta shigo kicin din, gabanta ya fadi! tunda suke a gidan sai ta irga iya adadin shigowarta gurinta bai fi uku ko hudu ba Allah dai yasa ba wata masifar bace.

"Gwaggo ina kwana."? tafada babu cikakkiyar sakewa.

Gwaggo cikin kulawa ta amsa da fadin" Rabi gurin ki nazo.'' Ummatu ta saki ludayin da take dama kunu dashi tana kallonta .

Gwaggo ta 'kas'kantar da kanta da fad'in "Dan Allah Rabi'atu ki gafarci yaron nan kiyi hakuri ki masa addua Akan Allah ya sassauta masa domin jiya ni nasan mummunan halin dana ganshi a mafarkina.

Ummatu jikinta yayi sanyi tace." Gwaggo dama ai ni ban 'kullaci Khalid ba tunda dama ban yarda da zargin da kuke masa ba.

Tace."To hakane to amma dan Allah ki dage dayi masa addua saboda bakin uwa albarka gare shi ki daina zuwa kina asarar kudin ki a banza addua zaki masa da kyakykyawan fata."

Ummatu tace."To shikkenan Gwaggo insha Allahu zan cigaba dayi masa addua.

Tace."Bari na tsaya na tafi da kunun tunda naga kin gama damawa." Ummatu tace."Aa Gwaggo kije kawai zan kawo muku." Gwaggo 'kin tafiya tayi har sai da Ummatu ta zuba musu kunun a jug ta zuba musu awara mai yawa a silba Gwaggo ta dinga shi mata albarka kamar basu ta'ba samun sa'bani da juna ba Ummatu ta dinga mamakin al'amarin domin tunda suke da Gwaggon bata ta'ba kwantar mata da kai irin yau ba gashi har da ya sanya mata albarka gaskiya dole al'amarin ya bata mamaki.

'Dakin ta shigo ta same ni na gama shiryawa tace."Sa'ida ga kunu nan da zafin sa ki zauna kisha kafin ki tafi.''

Da mamaki! a tare dani nake kallonta kafin nace."Yau da kanki kika kar'bo kunun."? Tace."Eh gani nayi ta gama damawa shiyasa na tsaya na tawo dashi.

Shuru nayi na samu cup na tsiyayi kad'an a warar ma uku na dauka na zauna ina kur'ba, tace"Ki sake kiran wayar tasa mana.

Ba tare dana ce komai ba na dauki wayar na shiga duba number tashi....Kamar dazu wayar ta katse ta'ki shiga.

Nace."Gwaggo sai dai kiyi hakuri fa domin wayar nan ta'ki shiga.kallona take nace." Dan Allah ki daina wannan kukan Gwaggo mutuwa dai ake Jin tsoro idan Kwanan sa ne ya 'kare Allah ya jikansa.

Tace."Sa'ida amma baki da tausayi da imani yanzu sai kiso Khalid ya mutu a wani guri ai idan ma lokacinsa ne yazo nafi bukatar ya mutu a gabana hankali na sai yafi kwanciya idan naga gawarsa.

Nace."Yanzu ma idan mutuwar yayi kina zaune labari zai same ki kuma za'a kawo miki gawar sa har gida.

Ta dinga kuka tana watsa min harara, dariya na kunshe a gurguje na gama abinda nake nayi mata sallama uffan ba tace min ba har na fita daga gidan.

Sai da gari ya waye tukkuna suka samu damar komawa cikin motar kowa ya zauna a gurin zamansa jikinsu duk yayi sanyi da irin 'barnar da 'yan fashi sukayi musu Khalid baiji takaici sosai ba saboda yasan ya tsira da sim card dinsa da 'yan tufafinsa amma duk guzurin kudin da Sukayi shi da Salmanu 'Yan fashin nan sun hargitsa musu kaya sun kwashe a yanzu ko sun sauka a garin na legos sai Sunyi fafutuka tukkuna.

Motar tayi shuru kowa na sake-sake a cikin ransa yayin da direben ke ta sharara guda akan kwalta, tun kafin su karasa inda matar take kwance a gefen titi Mijin nata yake ihu! da fadin"Innalillahi wa'ina ilaihi raji'un gatacan a kwance sun kasheta.''

Direban suna karasawa inda take ya fara kokarin parking ko kafin ya 'karasa mutumin ya fit ya fito a take ya gangara k'asan wani rami mai Mugun zurfi! gaske.

Hankalin su Khalid ya tashi mutuka hakika tunda yake bai ta'ba ganin masifa da tashin hankali irin na yau ba wannan mugun ramin da mutumin ya fad'a ciki ai sai dai wani kuma, wasu suka nufi inda matar take kwance wasu kuma Sukayi dafifi! a bakin ramin da mutumin ke ciki sai salati suke suna tunanin ita ina zasu taimakeshi.

Khalid yayi masifar tsorata da ganin matar da babu rai a tare da ita har ta fara kumbura ga jini duk ya bushe a jikinta kud'aje da 'kwarika sai bin jikinta sukeyi.......Yarinyar ta na gani uwarta sai ta tsandara ihu!! ta shiga tsakanin mutanan tana so taje inda take...Khalid yayi gaggawar daukarta yana rarrashin ta hawayen tausayi na nema ya kufce masa..

Da yake sun shiga cikin gari yasa basu sha wata wahala ba mazauna gurin suka kawo musu dauki 'yan agaji suka shiga cikin ramin suka fito da mutumin a mace duk ya karkarye, da yawa daga cikin mutanan gurin sai da suka tsorata da wannan tashin hankali masu rauni a ciki suka dinga faduwa suna suma wasu kuwa gefe suke nema su zauna suyi ta share hawaye suna kad'aita Allah shi d'aya.

Khalid wata irin nadama mai tsanani ta rufe shi ya dinga jin kamar ya juya ya koma gida ya nemi gafarar iyayensa da wacce ya zalin ta yanzu idan da 'karar kwana da tuni shima ya zama tarihi ya mutu da fushin iyaye a tare dashi.

Jakar mutumin aka duba akayi sa'ar samun wallet dinsa nan Suka shiga binkicen in da yake a jikin IDcard d'insa aka samu cikakken address dinsa da inda yake aiki. Mutumin dai dan kano ne kuma yana aiki asibitin Koroda dake karkashin gomnati. ba tare da 'bata lokaci ba jami'an tsaron dake gurin suka shiga aikinsu Gawarwakin aka d'aure suka sa a mota suka dauki hanya Khalid ya dinga jin kamar ya tsayar dasu ya bisu ya koma gida suna tsaye a gurin har motar Police din ta 'bacewa ganinsu kafin su koma cikin motar ko wanne da mataccan jiki motar tayi tsit! shima direban duk da ya saba ganin tashin hankali irin wannan amma gaskiya wannan karon ya firgita mutuka jiki a mace ya shiga ya zauna ya kunna motar suka bar gurin...
*SADAUKARWA NE GA IYAYE NA GUDA BIYU*

*FATIMA MUSA (MOMY NIJAR)*
*TARE DA*
*USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)*

_*Ina kaunar ku iyayena ina kuma alfahari da irin kaunar da kuke nuna min💜🥰*_

*37&38*
Khalid da Salmanu sun sha matukar wahala kafin wani bayerabe ya tausaya musu ya basu gurin kwana a jikin gidansa, tunda suka sauka a garin suke buge-buge a kasuwanni domin su samu abinda zasu ci idan dare yayi su shiga 'kar'kashin gada su kwanta asuba nayi suke futowa daga karkashin gadar suyi sallah su shiga buge-buge kamar yanda suka saba Akande beyerabe ne kullum yana ganinsu a kasuwa suna bulayi da daukar dako sai ya tausaya musu ya dinga jansu a jikinsa yana nuna musu gurin da zasu shiga su samu aiki cikin ikon Allah kuwa suka kutsa cikin kasuwar su shiga cikin kanikawa masu gyaran abubuwan hawa suka fara taimaka musu da yake duk yawanci masu aiki a gurin 'yan jahar kano ne shiyasa suka saki jikinsu dasu suka basu gurin zama suna nuna musu yanda zasuyi sati hudu sun zama 'yan gari domin gyaran mota kona babur babu wanda basu iya ba.
Idan sun tashi daga aiki sai su nufi shagon da suke kwana wanda yake jikin gidan Akande, watansu biyu a legos suka siyi waya Khalid yasa Sim card dinsa a wayar shi kuwa Salmanu sai da ya siyi wani akai masa rigistar Allah yasa yana da number wayar mahaifiyarsa saboda haka kai tsaye ita ya fara kira.

Khalid kuwa babu wanda yayi tunanin kira sai aunty shi domin kullum da ita yake kwana a cikin ransa zuciyarsa na fada masa cewa ta riga tayi auranta fa sai dai ka hakura duk sanda zuciyarsa tayi masa wannan tunin yini yake cikin damuwa da bakin kishi.

Muna tare da Hauwwa a gidanta mai lalle nayi min na biki kiran wayar tashi ya shigo waya ta a lokacin da naga sunansa yana yawo a fuskar waya ta sai da na zabura! mai lallen tayi saurin rike kafata nace."Dan saurara na amsa waya.

Kafata ta saki na kalli Hauwwa a sanyaye nace."Khalid ne."? Baki ta bude da sauri tace."Ikon Allah dama yana raye a duniya.?

Hannu na daga mata nasa wayar a kunnena.

sanyayyar ajiyar zuciyarsa naji a kunnena kafin naji sautin muryarsa yana kiran sunana.
Chapter 33 · 0% Book details