Sashe 42
Ga Irinta Nan Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bude baki nayi zanyi magana sai kuma kuka ya kufce min nasa hannu na gumtse bakina hawaye na shatata! jikinsa na wani irin rawa janyo ni jikinsa sosai ya rik'e ni yana kokarin goge min hawayen fuskata...Gwaggo tace."Khalid sakar mata jiki kada kasa mu shiga fushin ubangiji kayi maza!maza ka sakar mata jiki."
Da karfi take maganar tana kokarin mikewa tsaye!
Kasa'ke yayi yana kallonta hakan ya bani damar mi'kewa daga kusa dashi naje na samu wani gurin na zauna ina goge fuskata.
Yace."Gwaggo wace irin magana ce wannan."?
Girgiza kanta ta shiga yi tace."Khalid da naso ka zauna kaci abinci ka samu nutsuwa in yaso sai na zaunar da kai na fada maka abinda yake faruwa amma yanzu tunda hakan be samu ba dole na fada maka halin da ake ciki.....A yanzu dai Sa'ida tana da aure kuma ba kowa take aure ba face Alhaji Nura wannan dalilin yasa kaga hankalina ya tashi a lokacin daka ri'keta a jikinka."
Wani irin jiri ya dinga yi a zaune kansa ya dinga juyawa gabadaya ya nemi yawu ya rasa a bakinsa auntynsa tana da aure amma ta yaudare shi a waya tace ya dawo gida zata aureshi shin meye manufarta nayin wasa da hankalinsa.
Mi'kewa tsaye yayi jikinsa na wani irin rawa ya dumfari inda take zaune!.....tsorata nayi da ganin yanda ya tunkaro ni na mi'ke da saurin gaske Gwaggo na kokarin tare masa hanya da sauri ya kauce mata wuyana ya sha'ko ya had'a ni da bango (garu) ya matse ni sosai! ido jajawur! yace."Ni zaki yaudara ko."? Gwaggo hankalinta a tashe tazo tana kokarin janyeshi tana fadin."Haba Jarumi ka sassautawa zuciyarka mana." hannu ya daga mata a fusace! yace."Gwaggo ki 'kyaleni na kashe wannan mara imanin gwara na aika da ita barzahu tun kafin ta aika dani." Yana gama maganarsa ya sake matse wuya na da jikin bangon."
Gwaggo ta fashe da kuka hankali a tashe! ta fita daga dakin............Khalid dai da gaske so yake ya kasheni dan yanda ya matse min wuya gabadaya ya hana ni fitar da numfashi, sai kawai na rintse idanuwana zafafan hawaye suka shiga kwaranyo wa a saman fuskata.
*49&50*
Hawayen dake sharara a saman fuskata bai sanya shi ya sassauta matsar da yayi wa wuyana ba, yana wani irin huci da zufa! yace."Ni zaki yi wa haka ko? me yasa kin san an daura miki aure da wani zaki yaudare ni! kin mayar dani shakatafe sabida kina ganin ina sonki ko to wallahi ki rubuta ki ajiye sai na hana ki jin dadin rayuwa yanda kika hautsina min lissafi kema sai na hautsina naki sai na hana ki zaman aure da kowane mahaluki." Yana maganar yana matse ni a jikin bango had'e da bubbuga kaina yanda jikinsa yake rawa sai ka dauka tsumin 'yan bori yasha hannu nasa akan nasa ina k'okarin cire hannunsa ya sake shaqe ni da kyar nace."Kashe ni kake so kayi ko."?
Ido jawur! yace."Meye amfanin mayaudariya kashe ki zanyi dan baki da wani amfani." ya 'karasa maganar yana sake ma'kure ni a jikin bango(Garu) Gwaggo da Ummatu suka shigo dakin hankalinsu a tashe.
Ganin yanda nayi wujiga-wujiga a hannunsa ya tsorata su Ummatu tazo tana janyeshi had'e da bashi baki ya sake ni! kansa ya sunkuyar k'asa tare da sassauta matsar da yayi min amma bai sake ni gabadaya ba.
Gwaggo tazo ta rike hannunsa a sanyaye tace."Haba Jarumi ka zama mai hakuri da yarda da kaddara mana me yasa zaka aikata haka ka duba kaga yanda duk ka galabaitar da ita kayi hakuri ka saketa komai kaga yana faruwa to dama can haka Allah ya shirya."
Ya kalleta da jajayen idanunsa yace."Gwaggo wato har dake za'a hada baki a yaudare ni ko? me yasa kin san tayi aure baki fada min ba bayan kullum muna waya dake."
Kallona tayi tana so tayi magana sai ta kasa nace."Me yasa zakiyi shuru Gwaggo ki fada masa cewa nice na tsara haka in yaso sai ya dauko wuka ya soka min a ma'koshi."
Raina a 'bace nake magana.
Matse wuya na ya sakeyi ya tsira min rikitattun idanunsa, da 'kyar nace."Khalid ka kashe ni mana mai ka tsaya jira ne." Shuru yayi bai ce komai ba ya dai zuba min idanunsa da nake hango ruwan hawaye a cikinsu.
Ummatu tazo ta cire hannunsa daga wuyana ai banyi wata-wata ba na fitar da hannu a zafafe zan kai masa mari!
Hannun ya rike ya murd'e da mugun karfi na saki ihu! ya yarfar min da hannuna yana huci! ya matsa daga gurin.
Tsugunawa nayi a gurin hawaye masu zafi na zubo min hannuna kawai nake dubawa kamar wacce tayi targade sabida zafi.
Gabad'ayansu kansa suka rufu suna bashi baki babu wacce tabi ta kaina. raina ya 'baci sosai na kalli gefe na kwalbar cocar colar da Gwaggo kesa maganin sauro a kai na dauka a fusace na kai masa jifa da ita. cikin zafin nama ya kauce yana kallona.
Murya na rawa nace."Wallahi sai kasan wanda kayi wa wannan iskanci Khalid sai na fad'awa Kawu yayi min tsakani da kai shashasha mara hankali kawai."
Gwaggo a fusace! tace."Wato ba zaki daina zaginsa ba ko.''
Nima a fusace! Nace." Gwaggo abinda yafi zagi zanyi masa mutukar bai fita daga dakin nan ba."
Tace." ba zai fita ba din sai dai ke ki fita dama ai rashin hakurin ki ne yasa mijin naki ya koro ki gida.""
Cikin takaici da mugun bakin ciki nace."Haka zaki ce ko."? Da sauri tace."Eh mana ai gaskiya ce ya za'ayi ki yaudari yaro bayan kin san ba auransa za kiyi ba shiyasa lokacin da kika zo da maganar hankalina bai kwanta da ita ba saboda nasan halin Khalid da zafin zuciya.
Nace."A lokacin da nazo da maganar gabad'ayan ku kuna neman hanyar da zaku bi kuga ya dawo gida kun rasa me yasa dana kawo shawarar hakan kuka amince sai yanzu kuma ki goya masa baya to bari kaji da kai da Gwaggo a yanzu koda aurena zai mutu ba zan aureka ba kaje can ka nemi daidai da kai." na 'karashe maganar idona a tsaye a kansa.
Gwaggo tace."To dama me zaiyi dake kuma ai shi sabuwar budurwa zai aura mai jini ajika.
Kallonta nayi zuciyata na ingiza ni akan na tashi na hada kayana na bar gidan wata zuciyar tace ki zauna dai har Kawu ya dawo ya yanke hukunci.
Ummatu tace."Ke Sa'ida magana ta mutu dan kyautawa baki kyauta ba kai kuma Khalid ka shiga hankalinka ka gane samu da rashi duk na Allah ne.
Yace."Ummatu wallahi hakkina ba zai bar wannan mayaudariyar ba ta cuce ni."
Nace."Kai har kana da bakin wata magana akaina ko.''? Gwaggo da sauri tace."Magana dai a barta ni bana son wani tashin tashina."
Girgixa kaina nayi cikin tsantsar takaici na kalleshi nace."Hakki ko."?
Kallona yake babu kiftawa nace."To ina rokon Allah ya gaggauta bi maka hakkinka a kaina idan kuma ni nake da hakki Allah ya gaggauta bi min akanka.''
Ina k'are magana ta na fita tsakar gida na zauna dandaryar 'kasa tunanin mafita kawai nake.
Gwaggo da Ummatu da 'kyar suka rarrasheshi ya tsakuri abinci kadan yace ya koshi! mikewa yayi ya fita ya barsu a dakin suna tattaunawa.
Bayansa nabi da kallo a lokacin da yake kokarin fita daga gidan, daidai bakin kofa ya yanke jiki ya fadi.
Gabana yayi wani irin fad'uwa! "Gwaggo." da karfi na kwala mata kira."
Tare suka fito ita da Ummatu na nuna musu inda yake kwance tamkar mara rai.
Gwaggo salati ta rafka hankali a tashe ta kamfato ruwa ta kuza masa a jikinsa, tsayuwa sukayi kansa suna kuka Gwaggo fadi take "Sa'ida kinga masifar da kika janyo mana ko zaki kasheshi ki huta ai.
Daki na shiga na dauko waya ta hannuna sai rawa yake na marasa wanda zan kira a wayar.
Ummatu ta tsuguna kusa dashi tana masa firfita hade da kiran sunansa.
Idonsa ya bude a jigace yake kokarin tashi zaune kansa na wani irin sarawa hakika al'amarin yayi masifar firgitashi da sashi cikin tashin hankali .
Gwaggo hannunsa ta rike sai sannu take masa tana yi masa firfita da mahuci.
Kawu ne ya shigo gidan hannunsa rike da ledoji ganinsu sun masa rumfa da mafici a hannu yasa ya tsaya yana tambayar abinda ke faruwa.
Gwaggo hawaye ta share tace."Faduwa yayi ya suma bayan ya samu labarin auran Sa'ida yanzu yanzu ya farfado.
Kawu bece komai ba ya tsallakesu ya shige ciki
Kallona yayi cikin kulawa nace."Kawu Sannu da zuwa." yana sake nazari na yace."Sa'ida kiyi hakuri da rayuwa kinji ko." hawaye suka zubo min hannu nasa na goge nace."To Kawu insha Allah. Har yayi nufin wuce wa gurinsu sai ya tsaya da fad'in "Har yanzu dai Alhaji Nura beyi magana ba ni kuma bana so na tunkareshi da maganar sabida kada yaga kamar wani abu dole dai zamu cigaba da sauraransa daga nan zuwa gobe idan beyi magana ba to zan samu Alhaji Shamsu da maganar muji hukuncin da zai yanke.
A raunane nace." To shikkenan Kawu."
Gurinsu ya shige ba tare daya waiwayi su Gwaggo ba haushin Khalid din ya shafe su ya lura wani lokacin mahaifiyar tasa ce take d'aurewa yaron gindi yake iskancin da yake so.
Nima mi'kewa nayi na shiga daki na bar su a gurfane a gabansa suna rarrashinsa mussaman Gwaggo da duk ta fita daga hayyacinta, shima abinda ya gani kenan yasa ya sassautawa zuciyarsa ya daure ya mike tsaye, Gwaggo tace ka shiga dakinka ka kwanta ka huta kaji ko Khalid dan Allah dan Annabi ka cire Sa'ida daga cikin ranka idan ka mutu mune mukayi asara ba wani ba.
Kansa kawai ya daga mata ya bar gurin kallo suka bishi dashi suna jimanta abinda ya faru.
To sai da na bari Kawu ya ci abinci ya nutsu tukkuna na shiga gurin na same shi a kashingid'e akan dadduma yana hutawa.
Gaishe shi na sakeyi ya amsa cike da kulawa da fadin "Sa'ida akwai magana a tare dake ko."?
Nace." Eh Kawu nazo ne akan inaso kayi min tsakani da Khalid ya fita daga harkata tunda dai ni ba sa'arsa bace Kawu wai kamar ni Khalid zai shaqewa ma'kogwaro kuma su Gwaggo suna gani sun kasa daukar mataki."
Da karfi take maganar tana kokarin mikewa tsaye!
Kasa'ke yayi yana kallonta hakan ya bani damar mi'kewa daga kusa dashi naje na samu wani gurin na zauna ina goge fuskata.
Yace."Gwaggo wace irin magana ce wannan."?
Girgiza kanta ta shiga yi tace."Khalid da naso ka zauna kaci abinci ka samu nutsuwa in yaso sai na zaunar da kai na fada maka abinda yake faruwa amma yanzu tunda hakan be samu ba dole na fada maka halin da ake ciki.....A yanzu dai Sa'ida tana da aure kuma ba kowa take aure ba face Alhaji Nura wannan dalilin yasa kaga hankalina ya tashi a lokacin daka ri'keta a jikinka."
Wani irin jiri ya dinga yi a zaune kansa ya dinga juyawa gabadaya ya nemi yawu ya rasa a bakinsa auntynsa tana da aure amma ta yaudare shi a waya tace ya dawo gida zata aureshi shin meye manufarta nayin wasa da hankalinsa.
Mi'kewa tsaye yayi jikinsa na wani irin rawa ya dumfari inda take zaune!.....tsorata nayi da ganin yanda ya tunkaro ni na mi'ke da saurin gaske Gwaggo na kokarin tare masa hanya da sauri ya kauce mata wuyana ya sha'ko ya had'a ni da bango (garu) ya matse ni sosai! ido jajawur! yace."Ni zaki yaudara ko."? Gwaggo hankalinta a tashe tazo tana kokarin janyeshi tana fadin."Haba Jarumi ka sassautawa zuciyarka mana." hannu ya daga mata a fusace! yace."Gwaggo ki 'kyaleni na kashe wannan mara imanin gwara na aika da ita barzahu tun kafin ta aika dani." Yana gama maganarsa ya sake matse wuya na da jikin bangon."
Gwaggo ta fashe da kuka hankali a tashe! ta fita daga dakin............Khalid dai da gaske so yake ya kasheni dan yanda ya matse min wuya gabadaya ya hana ni fitar da numfashi, sai kawai na rintse idanuwana zafafan hawaye suka shiga kwaranyo wa a saman fuskata.
*49&50*
Hawayen dake sharara a saman fuskata bai sanya shi ya sassauta matsar da yayi wa wuyana ba, yana wani irin huci da zufa! yace."Ni zaki yi wa haka ko? me yasa kin san an daura miki aure da wani zaki yaudare ni! kin mayar dani shakatafe sabida kina ganin ina sonki ko to wallahi ki rubuta ki ajiye sai na hana ki jin dadin rayuwa yanda kika hautsina min lissafi kema sai na hautsina naki sai na hana ki zaman aure da kowane mahaluki." Yana maganar yana matse ni a jikin bango had'e da bubbuga kaina yanda jikinsa yake rawa sai ka dauka tsumin 'yan bori yasha hannu nasa akan nasa ina k'okarin cire hannunsa ya sake shaqe ni da kyar nace."Kashe ni kake so kayi ko."?
Ido jawur! yace."Meye amfanin mayaudariya kashe ki zanyi dan baki da wani amfani." ya 'karasa maganar yana sake ma'kure ni a jikin bango(Garu) Gwaggo da Ummatu suka shigo dakin hankalinsu a tashe.
Ganin yanda nayi wujiga-wujiga a hannunsa ya tsorata su Ummatu tazo tana janyeshi had'e da bashi baki ya sake ni! kansa ya sunkuyar k'asa tare da sassauta matsar da yayi min amma bai sake ni gabadaya ba.
Gwaggo tazo ta rike hannunsa a sanyaye tace."Haba Jarumi ka zama mai hakuri da yarda da kaddara mana me yasa zaka aikata haka ka duba kaga yanda duk ka galabaitar da ita kayi hakuri ka saketa komai kaga yana faruwa to dama can haka Allah ya shirya."
Ya kalleta da jajayen idanunsa yace."Gwaggo wato har dake za'a hada baki a yaudare ni ko? me yasa kin san tayi aure baki fada min ba bayan kullum muna waya dake."
Kallona tayi tana so tayi magana sai ta kasa nace."Me yasa zakiyi shuru Gwaggo ki fada masa cewa nice na tsara haka in yaso sai ya dauko wuka ya soka min a ma'koshi."
Raina a 'bace nake magana.
Matse wuya na ya sakeyi ya tsira min rikitattun idanunsa, da 'kyar nace."Khalid ka kashe ni mana mai ka tsaya jira ne." Shuru yayi bai ce komai ba ya dai zuba min idanunsa da nake hango ruwan hawaye a cikinsu.
Ummatu tazo ta cire hannunsa daga wuyana ai banyi wata-wata ba na fitar da hannu a zafafe zan kai masa mari!
Hannun ya rike ya murd'e da mugun karfi na saki ihu! ya yarfar min da hannuna yana huci! ya matsa daga gurin.
Tsugunawa nayi a gurin hawaye masu zafi na zubo min hannuna kawai nake dubawa kamar wacce tayi targade sabida zafi.
Gabad'ayansu kansa suka rufu suna bashi baki babu wacce tabi ta kaina. raina ya 'baci sosai na kalli gefe na kwalbar cocar colar da Gwaggo kesa maganin sauro a kai na dauka a fusace na kai masa jifa da ita. cikin zafin nama ya kauce yana kallona.
Murya na rawa nace."Wallahi sai kasan wanda kayi wa wannan iskanci Khalid sai na fad'awa Kawu yayi min tsakani da kai shashasha mara hankali kawai."
Gwaggo a fusace! tace."Wato ba zaki daina zaginsa ba ko.''
Nima a fusace! Nace." Gwaggo abinda yafi zagi zanyi masa mutukar bai fita daga dakin nan ba."
Tace." ba zai fita ba din sai dai ke ki fita dama ai rashin hakurin ki ne yasa mijin naki ya koro ki gida.""
Cikin takaici da mugun bakin ciki nace."Haka zaki ce ko."? Da sauri tace."Eh mana ai gaskiya ce ya za'ayi ki yaudari yaro bayan kin san ba auransa za kiyi ba shiyasa lokacin da kika zo da maganar hankalina bai kwanta da ita ba saboda nasan halin Khalid da zafin zuciya.
Nace."A lokacin da nazo da maganar gabad'ayan ku kuna neman hanyar da zaku bi kuga ya dawo gida kun rasa me yasa dana kawo shawarar hakan kuka amince sai yanzu kuma ki goya masa baya to bari kaji da kai da Gwaggo a yanzu koda aurena zai mutu ba zan aureka ba kaje can ka nemi daidai da kai." na 'karashe maganar idona a tsaye a kansa.
Gwaggo tace."To dama me zaiyi dake kuma ai shi sabuwar budurwa zai aura mai jini ajika.
Kallonta nayi zuciyata na ingiza ni akan na tashi na hada kayana na bar gidan wata zuciyar tace ki zauna dai har Kawu ya dawo ya yanke hukunci.
Ummatu tace."Ke Sa'ida magana ta mutu dan kyautawa baki kyauta ba kai kuma Khalid ka shiga hankalinka ka gane samu da rashi duk na Allah ne.
Yace."Ummatu wallahi hakkina ba zai bar wannan mayaudariyar ba ta cuce ni."
Nace."Kai har kana da bakin wata magana akaina ko.''? Gwaggo da sauri tace."Magana dai a barta ni bana son wani tashin tashina."
Girgixa kaina nayi cikin tsantsar takaici na kalleshi nace."Hakki ko."?
Kallona yake babu kiftawa nace."To ina rokon Allah ya gaggauta bi maka hakkinka a kaina idan kuma ni nake da hakki Allah ya gaggauta bi min akanka.''
Ina k'are magana ta na fita tsakar gida na zauna dandaryar 'kasa tunanin mafita kawai nake.
Gwaggo da Ummatu da 'kyar suka rarrasheshi ya tsakuri abinci kadan yace ya koshi! mikewa yayi ya fita ya barsu a dakin suna tattaunawa.
Bayansa nabi da kallo a lokacin da yake kokarin fita daga gidan, daidai bakin kofa ya yanke jiki ya fadi.
Gabana yayi wani irin fad'uwa! "Gwaggo." da karfi na kwala mata kira."
Tare suka fito ita da Ummatu na nuna musu inda yake kwance tamkar mara rai.
Gwaggo salati ta rafka hankali a tashe ta kamfato ruwa ta kuza masa a jikinsa, tsayuwa sukayi kansa suna kuka Gwaggo fadi take "Sa'ida kinga masifar da kika janyo mana ko zaki kasheshi ki huta ai.
Daki na shiga na dauko waya ta hannuna sai rawa yake na marasa wanda zan kira a wayar.
Ummatu ta tsuguna kusa dashi tana masa firfita hade da kiran sunansa.
Idonsa ya bude a jigace yake kokarin tashi zaune kansa na wani irin sarawa hakika al'amarin yayi masifar firgitashi da sashi cikin tashin hankali .
Gwaggo hannunsa ta rike sai sannu take masa tana yi masa firfita da mahuci.
Kawu ne ya shigo gidan hannunsa rike da ledoji ganinsu sun masa rumfa da mafici a hannu yasa ya tsaya yana tambayar abinda ke faruwa.
Gwaggo hawaye ta share tace."Faduwa yayi ya suma bayan ya samu labarin auran Sa'ida yanzu yanzu ya farfado.
Kawu bece komai ba ya tsallakesu ya shige ciki
Kallona yayi cikin kulawa nace."Kawu Sannu da zuwa." yana sake nazari na yace."Sa'ida kiyi hakuri da rayuwa kinji ko." hawaye suka zubo min hannu nasa na goge nace."To Kawu insha Allah. Har yayi nufin wuce wa gurinsu sai ya tsaya da fad'in "Har yanzu dai Alhaji Nura beyi magana ba ni kuma bana so na tunkareshi da maganar sabida kada yaga kamar wani abu dole dai zamu cigaba da sauraransa daga nan zuwa gobe idan beyi magana ba to zan samu Alhaji Shamsu da maganar muji hukuncin da zai yanke.
A raunane nace." To shikkenan Kawu."
Gurinsu ya shige ba tare daya waiwayi su Gwaggo ba haushin Khalid din ya shafe su ya lura wani lokacin mahaifiyar tasa ce take d'aurewa yaron gindi yake iskancin da yake so.
Nima mi'kewa nayi na shiga daki na bar su a gurfane a gabansa suna rarrashinsa mussaman Gwaggo da duk ta fita daga hayyacinta, shima abinda ya gani kenan yasa ya sassautawa zuciyarsa ya daure ya mike tsaye, Gwaggo tace ka shiga dakinka ka kwanta ka huta kaji ko Khalid dan Allah dan Annabi ka cire Sa'ida daga cikin ranka idan ka mutu mune mukayi asara ba wani ba.
Kansa kawai ya daga mata ya bar gurin kallo suka bishi dashi suna jimanta abinda ya faru.
To sai da na bari Kawu ya ci abinci ya nutsu tukkuna na shiga gurin na same shi a kashingid'e akan dadduma yana hutawa.
Gaishe shi na sakeyi ya amsa cike da kulawa da fadin "Sa'ida akwai magana a tare dake ko."?
Nace." Eh Kawu nazo ne akan inaso kayi min tsakani da Khalid ya fita daga harkata tunda dai ni ba sa'arsa bace Kawu wai kamar ni Khalid zai shaqewa ma'kogwaro kuma su Gwaggo suna gani sun kasa daukar mataki."