Sashe 17
Ga Irinta Nan Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Uwale tace."To shikkenan ai babu damuwa sai kinzo din." Sallama sukayi da juna...Uwale na kokarin fita daga gidan Khalid ya shigo da kyar ya gaisheta yana dauke kansa ya shige gidan.
Gwaggo na ganinsa shi kadai fuskarsa kuma babu annuri sai tasha jinin jikinta.....Ya zaune kusa da ita yana matse gumin goshinta a sanyaye tace."Jarumi ya ake ciki ne ina Sa'idar.''?
Nannauyar ajiyar zuciya ya sauke kafin yace."Gwaggo lokacin da muka isa gidan Alhajin ya fita sai na yanke shawarar kiran wayarta Gwaggo nayi nayi ta daga ta'ki haka na hakura na kyaleta.
Tace."Yanzu dai baku samu nasarar daukota ba." Kansa kawai ya daga mata ya lumshe idonsa damuwa ce mai tsanani take damunsa.
Gwaggo shuru tayi na minti biyu kafin tace."Idan anjima da yamma zanje gidan ayi wacce za'ayi."
Idonsa ya bude da sauri yace."Kada kije musu gida ki bari Baba yace zai koma da daddare insha Allahu komai zaizo da sauki amma ni bana so kije gidan kiyi wani abu suji haushinki ko kuma daga baya kiyi nadama kiyi hakuri abi komai a hankali."
Shuru tayi ba dan maganarsa ta gamsar da ita ba, yace." kin san gobe ni zan koma skull ko."? Girgiza kanta tayi tace."Bani da labari aini na dauka ka gama karatun ganin wannan karan ka dade a gida."
Yace."Yajin aiki malamai suka tafi karatu kuma da yardar Allah na kusa kammalawa ki cigaba dayi min addua idan na gama na samu aiki."
Tace."Insha Allahu zan cigaba dayi maka addua."
Mikewa yake kokarin yi tace."Zaka ci abinci ko."? kallonta yayi kafin yace."Idan yanzu kika girka zanci." Tace."Sai dai na dauki taliya d'aya a cikin kayan abincin Sa'ida nayi maka dafaduka da daddawa irin wacce kakeso."
Girgiza kansa yayi yace."Kada ki ta'ba mata kayan abinci bari nai wanka na fita na siyo sai kiyi min." Tace."Khalid kada ka 'batar da kudinka zasuyi maka amfani a makaranta ka bari a d'auka tunda da akwai."
Yace."Gwaggo bana bukata na fad'a miki ki kyaleni naci aljihuna bana fatan wata mace ta ciyar dani." Tace."To shikkenan bari naje na siyo kayan miyar da zanyi maka girkin."
Yace."Ki zauna ki huta duk zan had'o komai da zaki bukata gurin girkin." Shuru tayi tana kallonsa har ya shige gurinsu....Ta sauke ajiyar zuciya cikin ranta take masa fatan alkairi.
Tsaf tayi masa jallop din taliya irin ta mutanan da taji daddawa da manja da kifi sosai yaji dadin abincin ya dinga ci yana santi ita kuma sai dariya take masa dama haka take so ya sake ya cika cikinsa da abinci......Bayan ya kammala cin abincin a nutse ya kalleta da fad'in "Gwaggo ni zan fita nayi sallama da abokaina dan gobe da wuri nake so na tafi."
Tace."To shikkenan Jarumi sai ka dawo." Khalid yasa takalmansa ya fice daga gidan ita kuma ta juye ruwan zafin dake kan wuta ta surka ta shiga bandaki tayi wanka a gurguje ta shirya jikinta cikin atamfa (nicam) riga da zani da mayafi ta daura dankwalin (disco) a kanta pose dinta da dan mukkuli ta dauka ta fito ta kulle dakin takalmanta na dan'ko tasa a 'kafafunta ta fita daga gidan......Bakin titi ta fita tana addua akan Allah yasa kada ta hadu da Khalid din cikin ikon Allah kuwa har ta shiga adaidaita sahu bata ganshi ba.
Har bakin gate din gidan Alhaji Shamsu aka ajiyeta ta fito tana gyara lullu'bin mayafin atamfar dake jikinta, Pose din ta bude ta dauko dari biyu ta mika masa ya kar'ba tare da dauko hamsin ya bata a matsayin canjin ta.. karba tayi da sauri tasa a cikin jakarta tana masa godiya yaja babur dinsa yayi gaba.
Gate din gidan ta nufa ta bubbuga maigadin ya bude ganin kamar yasan fuskarta yasa ya gaisheta tace."Ina fata ka sheda ni ko."? Maigadin yace."Eh na sheda ki Gwaggo bisimillah shigo mana."
Gwaggo ta shiga gidan tana hamdala a cikin zuciyarta...............Gyaran kayan miya mukeyi da Asabe kawai naji sallamarta nai saurin daga kaina ina kallon bakin kofa. Ido muka had'a da ita tace."Babu shakka Sa'ida wato ke kina nan hankalin ki a kwance kin bar mu cikin damuwa ko."?
Bagarar da maganarta nayi nace."Gwaggo sannu da zuwa ki shigo mana." Tace."Ai ko baki fad'a ba." Asabe na murmushi ta gaisheta ta amsa tana bin gurin da kallo sai ta'be baki take.
Sanin halinta yasa nayi saurin mi'kewa da fad'in "Shigo mana." Ba tare da tace komai ba ta biyo bayana...Ummah kawai sai ganin mu tayi a tare.
Da sauri tace."Gwaggo kece kike tafe da yamma haka."?
Tana kokarin cire takalmanta domin shiga falon tace."Aikuwa dai nice nake tafe ko dai ba'a maraba dani."?
Ummah Habiba tace."Aa Gwaggo ana maraba dake shigo ga guri ki zauna." Ta shiga ta zauna kan kujera tana gyara yafan mayafinta.
Cikin mutunci da girmawa Ummah ta gaisheta ta amsa babu cikakkiyar walwala a tare da ita.
Nace."Gwaggo sannu da hanya." tayi saurin fad'in "Ai bazan amsa gaisuwarki ba Sa'ida tunda kin nuna mana iyakarmu."
Nace."Gwaggo wace irin magana ce wannan."? Fashawa tayi da kuka tace."Wato Sa'ida saboda Ibrahim bashi da kudi baya baki shayi da biredi baya siyo kayan miya da nama shine kika tattaro kayan ki kika gudo gidan mijin mahaifiyarki to komai talaucin mu mune gatanki sabida haka 'kafata k'afarki zamu koma gida dan ba zan zauna ayi min 'karfa-'karfa ba."
Cikin aljabi da mamaki nake kallonta lallai Gwaggo ta iya sauya lamari wato tanan ta 'bullo kenan."
Umma Habiba tace."Haba Gwaggo banji dad'in wannan magana ba wallahi Sa'ida bata da gata sai ku kuma duk rashi da taulacin Kawunta bai gaza da ita ba yana iyakacin bakin kokarinsa akanta to me zai sanya kiyi wannan maganar."
Shuru tayi bata tanka ba.Umma Habiba ta cigaba da cewa" Sa'ida tazo gidan nan jiya da daddare cikin damuwa da tashin hankali ta sheda min irin cin mutuncin da Ummatu take mata wannan dalilin yasa nace ta zauna ta huta idan ta samu nutsuwa sai ta koma."
Gwaggo tace."Eh hakane abinda tazo ta fad'a miki Ummatu taci mutuncin ta amma kuma Kawunta Ibrahim ya dauki mataki dan yanzu zancan da nake miki Rabi tana gidansu kuma yace ba zata dawo ba sai Sa'ida ta dawo saboda haka idan ke 'yar halak ce sai ki had'a kayanki mu tafi gida idan kuma kikayi sanadiyar raba auran Ibrahim da matarsa to zaki shiga bakin duniya."
Sa'ida da mahaifiyarta jikinsu yayi sanyi! Gwaggo ganin duk jikinsu ya mutu sai taji dadin hakan ta cigaba da zuzuta al'amarin.....Ummah Habiba tace."To shikkenan Gwaggo magana ta 'kare Sa'ida zata biki amma sai mun jira Maigidan ya dawo."
Gwaggo wani irin kallo ta watsa mata a fusace tace.....
*GA IRINTA NAN!!!🙆🏼♀️*
_(LOVE STORY🌺)_
*NA*
_BINTU UMAR ABBALE🍒_
*MANAZARTA WRITES ASSO🖊️📚*
*MUTANAN NIJAR IDAN KUNA BUKATAR BIYAN KUDIN LITTAFIN GA NUMBER DA ZAKU NEMA......22790899076*
*SADAUKAWA NE GA IYAYE BIYU*
*FATIMA MUSA (MOMMY NIJAR)*
*TARE DA*
*USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)*
*(HAJIYA BABBAH)*
_*Hakika ina alfahari dadu Iyayena🤝🏻🥰*_
*16&17*
*'KARSHEN FREE PEGE*
"Wane irin sai maigidan ya dawo kuma Habiba kina nufin zanyi ta zama a gidan nan har sai mijinki ya dawo ya bada umarni."? ta'karashe maganar tana hararar ta.
Umma Habiba taji rashin dadin maganar Gwaggon amma sai ta daure ko a fuska bata nuna ba tace."Gwaggo abinda nake nufi kenan a bari ya dawo a bashi hakkinsa a matsayinsa na mijina tunda tamkar uba yake a gurinta saboda haka dan Allah kiyi hakuri kada ki dauki maganata da wata manufa ta daban."
Ta'be bakinta tayi tace."Saboda kawai nice sarkin zargi sai na dauki maganarki da wata manufa shikkenan ai tunda kince haka sai na zauna na jira shi ya dawo na dai fad'a miki 'kafata 'kafar Sa'ida dan ba zan yarda da raina da lafiyata jinina yayi agolanci a wani guri ba."
Cikin takaici nace."Wai Gwaggo wace irin magana ce wannan kike yi dan Allah kiyi shuru haka ki daina d'aga mirya da tada jijiyar wuya magana ta 'kare zan koma gidan ko dan saboda Ummatu ta dawo d'akinta."
Shuru tayi min ba tanka ba. Umma ta sauke ajiyar zuciya da fad'in "Ai maigidan ma yana kan hanya shida na yamma suke dawowa daga kasuwa."
Tace."To Allah ya kawo su lafiya." Umma Habiba ta amsa da "ameen tare da mi'kewa domin fita daga falon Gwaggo ta dakatar da ita, da fadin " Nace ko kina da goro ki bani wallahi garin sauri na manta nawa a gida." Tace."Gwaggo ni bana cin goro amma bari na tambayar miki Hajia Hansatu.'' tana nufin uwargidansu. tace."To nagode Habiba ina jira wallahi sha'awar cinsa ce ta taso min a yanzu idan ma babu a gurinta ga kudina a siyo min."
Umma Habiba tace."Ba za'a rasa ba insha Allahu bari na tambayar miki ita." Fita tayi daga dakin da sauri.
Nace."Gwaggo ba zaki daina cin goro ba ko."? Kallona tayi cikin kulawa tace."Sa'ida ai ina jin sai ranar da numfashi ya bar gangar jikina zan hakura da goro ya zame min masifa ni kaina so nake na daina amma na kasa."
Nace."Abu ne da kuka sanyawa ranku wanda kuke ganin idan baku ci ba wata matsalar zata iya faruwa daku kuma ba haka bane da zaku yi sati guda baku ci ba babu abinda zai same ku sai ma lafiya da kuzari da zakuyi amma dan jaraba kuyi ta cin abinda zai cutar daku."
Shuru tayi bata ce komai ba. nasan duk surutan da zanyi akan al'amarin ba zata d'auka ba cin goro ya zame mata jinin jikinta.
Gwaggo na ganinsa shi kadai fuskarsa kuma babu annuri sai tasha jinin jikinta.....Ya zaune kusa da ita yana matse gumin goshinta a sanyaye tace."Jarumi ya ake ciki ne ina Sa'idar.''?
Nannauyar ajiyar zuciya ya sauke kafin yace."Gwaggo lokacin da muka isa gidan Alhajin ya fita sai na yanke shawarar kiran wayarta Gwaggo nayi nayi ta daga ta'ki haka na hakura na kyaleta.
Tace."Yanzu dai baku samu nasarar daukota ba." Kansa kawai ya daga mata ya lumshe idonsa damuwa ce mai tsanani take damunsa.
Gwaggo shuru tayi na minti biyu kafin tace."Idan anjima da yamma zanje gidan ayi wacce za'ayi."
Idonsa ya bude da sauri yace."Kada kije musu gida ki bari Baba yace zai koma da daddare insha Allahu komai zaizo da sauki amma ni bana so kije gidan kiyi wani abu suji haushinki ko kuma daga baya kiyi nadama kiyi hakuri abi komai a hankali."
Shuru tayi ba dan maganarsa ta gamsar da ita ba, yace." kin san gobe ni zan koma skull ko."? Girgiza kanta tayi tace."Bani da labari aini na dauka ka gama karatun ganin wannan karan ka dade a gida."
Yace."Yajin aiki malamai suka tafi karatu kuma da yardar Allah na kusa kammalawa ki cigaba dayi min addua idan na gama na samu aiki."
Tace."Insha Allahu zan cigaba dayi maka addua."
Mikewa yake kokarin yi tace."Zaka ci abinci ko."? kallonta yayi kafin yace."Idan yanzu kika girka zanci." Tace."Sai dai na dauki taliya d'aya a cikin kayan abincin Sa'ida nayi maka dafaduka da daddawa irin wacce kakeso."
Girgiza kansa yayi yace."Kada ki ta'ba mata kayan abinci bari nai wanka na fita na siyo sai kiyi min." Tace."Khalid kada ka 'batar da kudinka zasuyi maka amfani a makaranta ka bari a d'auka tunda da akwai."
Yace."Gwaggo bana bukata na fad'a miki ki kyaleni naci aljihuna bana fatan wata mace ta ciyar dani." Tace."To shikkenan bari naje na siyo kayan miyar da zanyi maka girkin."
Yace."Ki zauna ki huta duk zan had'o komai da zaki bukata gurin girkin." Shuru tayi tana kallonsa har ya shige gurinsu....Ta sauke ajiyar zuciya cikin ranta take masa fatan alkairi.
Tsaf tayi masa jallop din taliya irin ta mutanan da taji daddawa da manja da kifi sosai yaji dadin abincin ya dinga ci yana santi ita kuma sai dariya take masa dama haka take so ya sake ya cika cikinsa da abinci......Bayan ya kammala cin abincin a nutse ya kalleta da fad'in "Gwaggo ni zan fita nayi sallama da abokaina dan gobe da wuri nake so na tafi."
Tace."To shikkenan Jarumi sai ka dawo." Khalid yasa takalmansa ya fice daga gidan ita kuma ta juye ruwan zafin dake kan wuta ta surka ta shiga bandaki tayi wanka a gurguje ta shirya jikinta cikin atamfa (nicam) riga da zani da mayafi ta daura dankwalin (disco) a kanta pose dinta da dan mukkuli ta dauka ta fito ta kulle dakin takalmanta na dan'ko tasa a 'kafafunta ta fita daga gidan......Bakin titi ta fita tana addua akan Allah yasa kada ta hadu da Khalid din cikin ikon Allah kuwa har ta shiga adaidaita sahu bata ganshi ba.
Har bakin gate din gidan Alhaji Shamsu aka ajiyeta ta fito tana gyara lullu'bin mayafin atamfar dake jikinta, Pose din ta bude ta dauko dari biyu ta mika masa ya kar'ba tare da dauko hamsin ya bata a matsayin canjin ta.. karba tayi da sauri tasa a cikin jakarta tana masa godiya yaja babur dinsa yayi gaba.
Gate din gidan ta nufa ta bubbuga maigadin ya bude ganin kamar yasan fuskarta yasa ya gaisheta tace."Ina fata ka sheda ni ko."? Maigadin yace."Eh na sheda ki Gwaggo bisimillah shigo mana."
Gwaggo ta shiga gidan tana hamdala a cikin zuciyarta...............Gyaran kayan miya mukeyi da Asabe kawai naji sallamarta nai saurin daga kaina ina kallon bakin kofa. Ido muka had'a da ita tace."Babu shakka Sa'ida wato ke kina nan hankalin ki a kwance kin bar mu cikin damuwa ko."?
Bagarar da maganarta nayi nace."Gwaggo sannu da zuwa ki shigo mana." Tace."Ai ko baki fad'a ba." Asabe na murmushi ta gaisheta ta amsa tana bin gurin da kallo sai ta'be baki take.
Sanin halinta yasa nayi saurin mi'kewa da fad'in "Shigo mana." Ba tare da tace komai ba ta biyo bayana...Ummah kawai sai ganin mu tayi a tare.
Da sauri tace."Gwaggo kece kike tafe da yamma haka."?
Tana kokarin cire takalmanta domin shiga falon tace."Aikuwa dai nice nake tafe ko dai ba'a maraba dani."?
Ummah Habiba tace."Aa Gwaggo ana maraba dake shigo ga guri ki zauna." Ta shiga ta zauna kan kujera tana gyara yafan mayafinta.
Cikin mutunci da girmawa Ummah ta gaisheta ta amsa babu cikakkiyar walwala a tare da ita.
Nace."Gwaggo sannu da hanya." tayi saurin fad'in "Ai bazan amsa gaisuwarki ba Sa'ida tunda kin nuna mana iyakarmu."
Nace."Gwaggo wace irin magana ce wannan."? Fashawa tayi da kuka tace."Wato Sa'ida saboda Ibrahim bashi da kudi baya baki shayi da biredi baya siyo kayan miya da nama shine kika tattaro kayan ki kika gudo gidan mijin mahaifiyarki to komai talaucin mu mune gatanki sabida haka 'kafata k'afarki zamu koma gida dan ba zan zauna ayi min 'karfa-'karfa ba."
Cikin aljabi da mamaki nake kallonta lallai Gwaggo ta iya sauya lamari wato tanan ta 'bullo kenan."
Umma Habiba tace."Haba Gwaggo banji dad'in wannan magana ba wallahi Sa'ida bata da gata sai ku kuma duk rashi da taulacin Kawunta bai gaza da ita ba yana iyakacin bakin kokarinsa akanta to me zai sanya kiyi wannan maganar."
Shuru tayi bata tanka ba.Umma Habiba ta cigaba da cewa" Sa'ida tazo gidan nan jiya da daddare cikin damuwa da tashin hankali ta sheda min irin cin mutuncin da Ummatu take mata wannan dalilin yasa nace ta zauna ta huta idan ta samu nutsuwa sai ta koma."
Gwaggo tace."Eh hakane abinda tazo ta fad'a miki Ummatu taci mutuncin ta amma kuma Kawunta Ibrahim ya dauki mataki dan yanzu zancan da nake miki Rabi tana gidansu kuma yace ba zata dawo ba sai Sa'ida ta dawo saboda haka idan ke 'yar halak ce sai ki had'a kayanki mu tafi gida idan kuma kikayi sanadiyar raba auran Ibrahim da matarsa to zaki shiga bakin duniya."
Sa'ida da mahaifiyarta jikinsu yayi sanyi! Gwaggo ganin duk jikinsu ya mutu sai taji dadin hakan ta cigaba da zuzuta al'amarin.....Ummah Habiba tace."To shikkenan Gwaggo magana ta 'kare Sa'ida zata biki amma sai mun jira Maigidan ya dawo."
Gwaggo wani irin kallo ta watsa mata a fusace tace.....
*GA IRINTA NAN!!!🙆🏼♀️*
_(LOVE STORY🌺)_
*NA*
_BINTU UMAR ABBALE🍒_
*MANAZARTA WRITES ASSO🖊️📚*
*MUTANAN NIJAR IDAN KUNA BUKATAR BIYAN KUDIN LITTAFIN GA NUMBER DA ZAKU NEMA......22790899076*
*SADAUKAWA NE GA IYAYE BIYU*
*FATIMA MUSA (MOMMY NIJAR)*
*TARE DA*
*USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)*
*(HAJIYA BABBAH)*
_*Hakika ina alfahari dadu Iyayena🤝🏻🥰*_
*16&17*
*'KARSHEN FREE PEGE*
"Wane irin sai maigidan ya dawo kuma Habiba kina nufin zanyi ta zama a gidan nan har sai mijinki ya dawo ya bada umarni."? ta'karashe maganar tana hararar ta.
Umma Habiba taji rashin dadin maganar Gwaggon amma sai ta daure ko a fuska bata nuna ba tace."Gwaggo abinda nake nufi kenan a bari ya dawo a bashi hakkinsa a matsayinsa na mijina tunda tamkar uba yake a gurinta saboda haka dan Allah kiyi hakuri kada ki dauki maganata da wata manufa ta daban."
Ta'be bakinta tayi tace."Saboda kawai nice sarkin zargi sai na dauki maganarki da wata manufa shikkenan ai tunda kince haka sai na zauna na jira shi ya dawo na dai fad'a miki 'kafata 'kafar Sa'ida dan ba zan yarda da raina da lafiyata jinina yayi agolanci a wani guri ba."
Cikin takaici nace."Wai Gwaggo wace irin magana ce wannan kike yi dan Allah kiyi shuru haka ki daina d'aga mirya da tada jijiyar wuya magana ta 'kare zan koma gidan ko dan saboda Ummatu ta dawo d'akinta."
Shuru tayi min ba tanka ba. Umma ta sauke ajiyar zuciya da fad'in "Ai maigidan ma yana kan hanya shida na yamma suke dawowa daga kasuwa."
Tace."To Allah ya kawo su lafiya." Umma Habiba ta amsa da "ameen tare da mi'kewa domin fita daga falon Gwaggo ta dakatar da ita, da fadin " Nace ko kina da goro ki bani wallahi garin sauri na manta nawa a gida." Tace."Gwaggo ni bana cin goro amma bari na tambayar miki Hajia Hansatu.'' tana nufin uwargidansu. tace."To nagode Habiba ina jira wallahi sha'awar cinsa ce ta taso min a yanzu idan ma babu a gurinta ga kudina a siyo min."
Umma Habiba tace."Ba za'a rasa ba insha Allahu bari na tambayar miki ita." Fita tayi daga dakin da sauri.
Nace."Gwaggo ba zaki daina cin goro ba ko."? Kallona tayi cikin kulawa tace."Sa'ida ai ina jin sai ranar da numfashi ya bar gangar jikina zan hakura da goro ya zame min masifa ni kaina so nake na daina amma na kasa."
Nace."Abu ne da kuka sanyawa ranku wanda kuke ganin idan baku ci ba wata matsalar zata iya faruwa daku kuma ba haka bane da zaku yi sati guda baku ci ba babu abinda zai same ku sai ma lafiya da kuzari da zakuyi amma dan jaraba kuyi ta cin abinda zai cutar daku."
Shuru tayi bata ce komai ba. nasan duk surutan da zanyi akan al'amarin ba zata d'auka ba cin goro ya zame mata jinin jikinta.