Sashe 70
Ga Irinta Nan Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
****
Tun ranar da mukayi sa'insa dashi bai 'kara yi min magana ba Na lura Yaya Aminu d'an gaba ne ban san me yasa ba laifi kadan sai yayi fushi yayi kwana da kwanaki bai kula ni ba, to wannan karon na gaji kullum cikin tashin hankali babu kwanciyar hankali ta aure sai bacin rai da damuwa ina ganin tun kafin dare yayi min na yanke wa kaina hukunci............Da yake tunda mukayi haka dashi ya sanja lokacin dawowa gida sai can dare yake shigowa kuma kafin na tashi ya fita yau dai na zauna a falo dole ya dawo akan idona domin ba zan kwanta ba sai naji matsayina a gurinsa.
Sai goma da arba'in da biyar ya shigo gidan Ganina a zaune a falo yasa yayi kici kici da fuska ya kauda kansa hade da kama hanyar dakinsa......."Yaya Aminu sannu da zuwa." Ko kallona beyi ba ya cigaba da kokarin bude d'akinsa.
Sai da na bari ya shiga dakin tukkuna na mike nabi bayansa.
Yana kokarin cire rigarsa na tsaya a gabansa fuskata a mugun hade......Rai a bace yace."Lafiya zaki zo ki sani a gaba."? Tsaki naja nace."Ina so naji matsayi na ne? ina so nasan zaman me nake a gidanka."
Shuru yayi min ya cire rigar tare da ratse ni zai wuce da sauri na tari gabansa na bude baki kenan zanyi magana ya gaura min mari!
Dafe kunci na nayi ina kallonsa idanuwa sunyi jajawur! Yace."Baki san haushin ki nake ji ba ko."? Jikina na kyarma nace."Kana jin haushina kamar yanda nake jin haushinka wallahi na tsanake bana kaunar kallon wannan bakar fuskar taka."
Murmushi yayi yace."Duk na gane akan abinda yasa kike min rashin kunya kina so ki tunzura zuciya na sake ki ko."? shuru nayi ina kallonsa ya cigaba da cewa."To ba zan sake ki ba sai kin wahala a hannuna tunda ke baki da mutunci."
Hawaye na share nace."Komai abinka idan zamana ya kare da kai dole ka sake ni ai ba'a dole na gaji da zama da kai babu lafiya gashi baka san mutunci ba."
Ture ni yayi na fadi a gurin ya shige toliet din yana fadin."Hukunci saki a hannuna yake zanga wanda ya isa ya sani na sake ki."
Cikin mutuwar jiki na mike na fita daga dakin......Gefan gado na zauna ina kuka na dauki waya ta number Umma Habiba na nemo gabadaya na manta da dare burina kawai na samu wanda zai rarrashe ni Yaya Aminu so yake yasa zuciyata tayi bundiga."
Umma Habiba na kokarin kashe wayarta taga kira gabanta na faduwa ta daga........."Innalillahi wa'ina ilahi raji'un! wannan kalmar ta fad'a hankali a tashe tace."Sa'ida ya isa ki daina kuka haka kiyi shuru kiyi min bayanin abinda ya faru shin fada kukayi da mijin naki."?
Cikin shaqewar murya tace."Umma na gaji da wannan masifar na gaji wallahi So nake ku raba ni da wannan wahala Yaya Aminu yana azabtar dani zuciyata daf take data buga saboda abubuwan da take had'iya."
Alhaji Shamsu ya miqa hannunsa da fadin."Bani wayar." Jiki a mace ta mika masa wayar yasa a kunnensa a nutse yace."Sa'ida yi shuru kinji ko ki daina kuka haka ya isa duk naji k'orafin ki kuma duk abinda kika ce Aminu yayi miki ba zanyi musu ba domin ba'a shaidar mutumin yau wannan auran dama ni tuntuni ya fice min daga raina saboda wannan gagarimar matsalar ba zan zama mara adalci ba insha Allahu ni zan tsaya miki akan hakkin ki Aminu zai sake ki kamar yanda kika bukata Allah yasa haka shi yafi alkairi."
Jikina ne kuma yayi sanyi sai tausayin mutumin ya lullu'be ni a sanyaye nace."Alhaji wallahi ba laifi na bane nayi dukkanin bakin kokari na al'amarin yaci tura Yaya Aminu yaki fahimtata kullum babu nutsuwa da kwanciyar hankali shiyasa kawai na yanke wannan shawarar domin ina ganin kamar itace maslaha."
Yace."Kwarai kuwa Wannan shine Maslaha kuma kinyi tunani mai kyau Sa'ida ba zaki kashe kan ki akan bukatar wani ba tabbas kinyi hakuri kuma kinyi namijin kokari akan al'amarin auranki duk wanda zai budi baki ya fadi laifin ki to yaso kansa domin ita gaskiya duk inda take sai ta tona kanta saboda haka kada ki damu kinji ko gobe da safe kizo gida da kayan ki." A sanyaye nace."Tom shikkenan Alhaji nagode sosai Allah yasa haka shi yafi alkairi" Cike da kulawa ya amsa da "Ameeen ya Allah." Kwanciyar rigingine nayi ina kallon rufin dakin......."Yanzu idan na rabu da auran Yaya Aminu wane irin namiji zan aura? Shin Sa'ida anya kuwa zaki samu nasarar auran wanda zuciyarki take hasashe."? Zuciyata ce take min wannan zancan.....Idona na rintse gabana ya shiga bugawa! kawai sai na tsinci kaina da addua akan Allah yasa Khalid ya dawo da soyayyarsa a gare ni........
[5/14, 11:48 AM] NAFEE Alwasa: *SADAUKARWA NE GA IYAYE NA BIYU*
*FATIMA MUSA (MOMMY NIJAR)*
*TARE DA*
*USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)*
*(HAJIYA BABBAH)*
*_Ha'kika ina Alfahari daku da irin kaunar da kuke min.🥰🤝🏻💜_*
*92*
Da wannan tunanin bacci mai nauyi ya d'auke ni da asubah sai da na fara wanka tukkuna na dauro alwala na fito na tayar da sallah bayan na idar na jima ina rokon Allah ya kawo min mafita a rayuwa amma a zahirin gaskiya auran Yaya Aminu ya fice min daga raina. jikina na shirya na nemi guri na kwanta ina jiran gari ya waye sosai na fita daga gidan.
Waya ta dake kan bedside na dauka na kunna time na duba shida da rabi na safe, ajiyar zuciya na sauke ina jin wani irin zazzafan feelings na taso min wani irin so nake wa yaron bana tunanin zan iya auran wani idan bashi din ba tunda yanzu na gane cewa shine daidai rayuwa ta, na jima ina shawarwari da zuciyata kafin na yanke shawarar kiran wayar shi muryarshi kawai nake so naji ko zan samu sassaucin abinda ke damuna a zuciyata......Number shi ta kasar waje bata shiga sai na kira number shi ta Asali cikin ikon Allah kuwa tana fara ringing ya daga.
Ajiyar zuciya na sauke hade da kiran sunansa. cikin alamun bacci ya amsa da wacece."? saboda bacci ne a idonsa sam be duba wayar ba.
Gabana na faduwa nace."Khalid nice fa.'' Jin muryarta yasa ya bude idonsa tare da gyara kwanciyarsa a kasalance yace."Aunty Sa'ida kin tashi lafiya."? Cikin kasala nace."Lafiya Khalid bacci kake na tashe ka ko."? k'aramar ajiyar zuciya ya sauke yace."Eh wallahi tunda nayi sallar asubah na kwanta baccin ya dauke ni kiran wayar ki ya tashe ni." Cikin taushin murya nace."Kayi hakuri don Allah." Murmushi ya saki yace."Auntyna ai ke bakya laifi ina fata dai lafiya ko."? shuru nayi ina dawurwura.
Yace."Kinyi shuru Aunty Sa'ida ke nake saurare." Cikin mutuwar jiki nace."Khalid na kasa nutsuwa saboda tunaninka yaushe zaka dawo gida ne."?
Jim yayi na minti biyu yace."Gobe ko jibi zan zo gida insha Allahu kada ku damu ina cikin koshin lafiya da nasarori masu yawa."
Nace."Alhamdulillah dama haka ake so ai duk na samu labarin irin daukakar da ka samu Khalid na taya ka murna ina rokon Allah ya tsare gabanka da bayanka." Ya amsa da ameeen Auntyna nagode sosai."
Shiru mukayi kowa yana sake-sake a zuciyarsa......Murya kasa-kasa yace."Aunty ya labarin maigidan ki ina fata dai komai yayi normal."
Murmushin takaici nayi nace."Yana nan Khalid ai mun rabu da juna." Kawai na tsinci kaina da fada masa haka.
Yace."Ai gwara hakan yafi amfani tunda zaman da kike a gidansa na cutar da kai ne Allah ya za'ba miki abinda yafi alkairi."
Cikin jin dadin maganarsa na amsa da "Ameeen ya Allah nagode k'anina.'' Yace." Yanzu kina ina hotoro ko gidan Gwaggo."? Nace." Ina can hotoro amma dai zan dawo gidan Gwaggo idan an kwana biyu." Yace."To shikkenan idan na sauka a gari zan kira wayarki." Cikin farin ciki nace."To shikkenan Allah ya kawo ka lafiya.'' Ya amsa da ameeen ya Allah ." Kashe wayarsa yayi ya barni da tawa a hannu sai murmushin jin dadi nake a zuciyata nace da alama ba zan sha wahala da yaron ba tunda har yanzu akwai kaunata a cikin zuciyarsa.........Kaina na dago sai muka hada ido dashi yana tsaye a bakin kofar shigowa fuskarsa a mugun 'bace! Gabana na faduwa na mike zaune ina kallonsa, cikin wani irin taku ya karaso inda nake sai na sunkuyar da kaina kasa ina addua a cikin zuciyata ha'ki'kanin gaskiya Yaya Aminu ya zame min mijin jaraba bala'in tsoron masifarsa nake.
"Da wane namiji kike waya."? maganarsa ta daki kunnena. kai a sunkuye nace.''Khalid ne."? Waye Khalid.''? ya fada cikin sigar zargi Dauriya na aro na kalleshi da fadin." Yaya Aminu Khalid din ne baka sani ba."? A zafafe ya daga min hannu da fad'in."Kada ki mayar dani shashasha mana kina waya da wani d'an iskan kice Khalid ne.'' Nace."To ai sai ka duba wayar ka gani ni bana munafurci mutukar nasan nayi abu to zan fad'a." Wayar hannuna ya fizge yana dubawa yake fadin."Na lura dake baki da mutunci da sanin ya kamata ba to zan sanya ido sosai a kanki domin ba zan lamunci ki zubar min da mutunci ba."
Murmushin takaici nayi nace."Wane irin mutunci kuma? Yaya Aminu ai kai zaka siyawa kanka mutunci ni wallahi daidai da 'kwayar zarrah bana ganin mutuncin ka." Ido ya tsira min nasan mamakin maganata yake dauke kaina nayi ina sake tamke fuskata 'kwafa yayi cikin bacin rai yace."Saboda kin kasa samun abinda kike so daga guri na shine kike bibiyar mazan waje ko.'' ? Da sauri na kalleshi idanuwa na sun tara ruwa nace."Sharrin da za kayi min kenan."? Cikin sigar rashin mutunci yace." Ke baki isa ayi miki sharri ba gaskiya ce wannan kada kiyi tsammanin ban san dalilin da yasa tsohon mijinki ya sake ki ba kada kuma kiyi tunanin cewa ba san irin iskancin da kike da maza a gurin aikin ki ba nasan komai nayi binkice sosai a kanki kafin na amince a d'aura min aure dake wannan dalilin ne yasa naqi mayar da hankali gurin shan magani domin kuwa banga amfanin had'a zuria dake ba.''
Wasu irin hawaye ne suka kwace min kallonsa kawai nake bakina na rawa na kasa magana tsabar mamaki da al'ajabi.
Tun ranar da mukayi sa'insa dashi bai 'kara yi min magana ba Na lura Yaya Aminu d'an gaba ne ban san me yasa ba laifi kadan sai yayi fushi yayi kwana da kwanaki bai kula ni ba, to wannan karon na gaji kullum cikin tashin hankali babu kwanciyar hankali ta aure sai bacin rai da damuwa ina ganin tun kafin dare yayi min na yanke wa kaina hukunci............Da yake tunda mukayi haka dashi ya sanja lokacin dawowa gida sai can dare yake shigowa kuma kafin na tashi ya fita yau dai na zauna a falo dole ya dawo akan idona domin ba zan kwanta ba sai naji matsayina a gurinsa.
Sai goma da arba'in da biyar ya shigo gidan Ganina a zaune a falo yasa yayi kici kici da fuska ya kauda kansa hade da kama hanyar dakinsa......."Yaya Aminu sannu da zuwa." Ko kallona beyi ba ya cigaba da kokarin bude d'akinsa.
Sai da na bari ya shiga dakin tukkuna na mike nabi bayansa.
Yana kokarin cire rigarsa na tsaya a gabansa fuskata a mugun hade......Rai a bace yace."Lafiya zaki zo ki sani a gaba."? Tsaki naja nace."Ina so naji matsayi na ne? ina so nasan zaman me nake a gidanka."
Shuru yayi min ya cire rigar tare da ratse ni zai wuce da sauri na tari gabansa na bude baki kenan zanyi magana ya gaura min mari!
Dafe kunci na nayi ina kallonsa idanuwa sunyi jajawur! Yace."Baki san haushin ki nake ji ba ko."? Jikina na kyarma nace."Kana jin haushina kamar yanda nake jin haushinka wallahi na tsanake bana kaunar kallon wannan bakar fuskar taka."
Murmushi yayi yace."Duk na gane akan abinda yasa kike min rashin kunya kina so ki tunzura zuciya na sake ki ko."? shuru nayi ina kallonsa ya cigaba da cewa."To ba zan sake ki ba sai kin wahala a hannuna tunda ke baki da mutunci."
Hawaye na share nace."Komai abinka idan zamana ya kare da kai dole ka sake ni ai ba'a dole na gaji da zama da kai babu lafiya gashi baka san mutunci ba."
Ture ni yayi na fadi a gurin ya shige toliet din yana fadin."Hukunci saki a hannuna yake zanga wanda ya isa ya sani na sake ki."
Cikin mutuwar jiki na mike na fita daga dakin......Gefan gado na zauna ina kuka na dauki waya ta number Umma Habiba na nemo gabadaya na manta da dare burina kawai na samu wanda zai rarrashe ni Yaya Aminu so yake yasa zuciyata tayi bundiga."
Umma Habiba na kokarin kashe wayarta taga kira gabanta na faduwa ta daga........."Innalillahi wa'ina ilahi raji'un! wannan kalmar ta fad'a hankali a tashe tace."Sa'ida ya isa ki daina kuka haka kiyi shuru kiyi min bayanin abinda ya faru shin fada kukayi da mijin naki."?
Cikin shaqewar murya tace."Umma na gaji da wannan masifar na gaji wallahi So nake ku raba ni da wannan wahala Yaya Aminu yana azabtar dani zuciyata daf take data buga saboda abubuwan da take had'iya."
Alhaji Shamsu ya miqa hannunsa da fadin."Bani wayar." Jiki a mace ta mika masa wayar yasa a kunnensa a nutse yace."Sa'ida yi shuru kinji ko ki daina kuka haka ya isa duk naji k'orafin ki kuma duk abinda kika ce Aminu yayi miki ba zanyi musu ba domin ba'a shaidar mutumin yau wannan auran dama ni tuntuni ya fice min daga raina saboda wannan gagarimar matsalar ba zan zama mara adalci ba insha Allahu ni zan tsaya miki akan hakkin ki Aminu zai sake ki kamar yanda kika bukata Allah yasa haka shi yafi alkairi."
Jikina ne kuma yayi sanyi sai tausayin mutumin ya lullu'be ni a sanyaye nace."Alhaji wallahi ba laifi na bane nayi dukkanin bakin kokari na al'amarin yaci tura Yaya Aminu yaki fahimtata kullum babu nutsuwa da kwanciyar hankali shiyasa kawai na yanke wannan shawarar domin ina ganin kamar itace maslaha."
Yace."Kwarai kuwa Wannan shine Maslaha kuma kinyi tunani mai kyau Sa'ida ba zaki kashe kan ki akan bukatar wani ba tabbas kinyi hakuri kuma kinyi namijin kokari akan al'amarin auranki duk wanda zai budi baki ya fadi laifin ki to yaso kansa domin ita gaskiya duk inda take sai ta tona kanta saboda haka kada ki damu kinji ko gobe da safe kizo gida da kayan ki." A sanyaye nace."Tom shikkenan Alhaji nagode sosai Allah yasa haka shi yafi alkairi" Cike da kulawa ya amsa da "Ameeen ya Allah." Kwanciyar rigingine nayi ina kallon rufin dakin......."Yanzu idan na rabu da auran Yaya Aminu wane irin namiji zan aura? Shin Sa'ida anya kuwa zaki samu nasarar auran wanda zuciyarki take hasashe."? Zuciyata ce take min wannan zancan.....Idona na rintse gabana ya shiga bugawa! kawai sai na tsinci kaina da addua akan Allah yasa Khalid ya dawo da soyayyarsa a gare ni........
[5/14, 11:48 AM] NAFEE Alwasa: *SADAUKARWA NE GA IYAYE NA BIYU*
*FATIMA MUSA (MOMMY NIJAR)*
*TARE DA*
*USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)*
*(HAJIYA BABBAH)*
*_Ha'kika ina Alfahari daku da irin kaunar da kuke min.🥰🤝🏻💜_*
*92*
Da wannan tunanin bacci mai nauyi ya d'auke ni da asubah sai da na fara wanka tukkuna na dauro alwala na fito na tayar da sallah bayan na idar na jima ina rokon Allah ya kawo min mafita a rayuwa amma a zahirin gaskiya auran Yaya Aminu ya fice min daga raina. jikina na shirya na nemi guri na kwanta ina jiran gari ya waye sosai na fita daga gidan.
Waya ta dake kan bedside na dauka na kunna time na duba shida da rabi na safe, ajiyar zuciya na sauke ina jin wani irin zazzafan feelings na taso min wani irin so nake wa yaron bana tunanin zan iya auran wani idan bashi din ba tunda yanzu na gane cewa shine daidai rayuwa ta, na jima ina shawarwari da zuciyata kafin na yanke shawarar kiran wayar shi muryarshi kawai nake so naji ko zan samu sassaucin abinda ke damuna a zuciyata......Number shi ta kasar waje bata shiga sai na kira number shi ta Asali cikin ikon Allah kuwa tana fara ringing ya daga.
Ajiyar zuciya na sauke hade da kiran sunansa. cikin alamun bacci ya amsa da wacece."? saboda bacci ne a idonsa sam be duba wayar ba.
Gabana na faduwa nace."Khalid nice fa.'' Jin muryarta yasa ya bude idonsa tare da gyara kwanciyarsa a kasalance yace."Aunty Sa'ida kin tashi lafiya."? Cikin kasala nace."Lafiya Khalid bacci kake na tashe ka ko."? k'aramar ajiyar zuciya ya sauke yace."Eh wallahi tunda nayi sallar asubah na kwanta baccin ya dauke ni kiran wayar ki ya tashe ni." Cikin taushin murya nace."Kayi hakuri don Allah." Murmushi ya saki yace."Auntyna ai ke bakya laifi ina fata dai lafiya ko."? shuru nayi ina dawurwura.
Yace."Kinyi shuru Aunty Sa'ida ke nake saurare." Cikin mutuwar jiki nace."Khalid na kasa nutsuwa saboda tunaninka yaushe zaka dawo gida ne."?
Jim yayi na minti biyu yace."Gobe ko jibi zan zo gida insha Allahu kada ku damu ina cikin koshin lafiya da nasarori masu yawa."
Nace."Alhamdulillah dama haka ake so ai duk na samu labarin irin daukakar da ka samu Khalid na taya ka murna ina rokon Allah ya tsare gabanka da bayanka." Ya amsa da ameeen Auntyna nagode sosai."
Shiru mukayi kowa yana sake-sake a zuciyarsa......Murya kasa-kasa yace."Aunty ya labarin maigidan ki ina fata dai komai yayi normal."
Murmushin takaici nayi nace."Yana nan Khalid ai mun rabu da juna." Kawai na tsinci kaina da fada masa haka.
Yace."Ai gwara hakan yafi amfani tunda zaman da kike a gidansa na cutar da kai ne Allah ya za'ba miki abinda yafi alkairi."
Cikin jin dadin maganarsa na amsa da "Ameeen ya Allah nagode k'anina.'' Yace." Yanzu kina ina hotoro ko gidan Gwaggo."? Nace." Ina can hotoro amma dai zan dawo gidan Gwaggo idan an kwana biyu." Yace."To shikkenan idan na sauka a gari zan kira wayarki." Cikin farin ciki nace."To shikkenan Allah ya kawo ka lafiya.'' Ya amsa da ameeen ya Allah ." Kashe wayarsa yayi ya barni da tawa a hannu sai murmushin jin dadi nake a zuciyata nace da alama ba zan sha wahala da yaron ba tunda har yanzu akwai kaunata a cikin zuciyarsa.........Kaina na dago sai muka hada ido dashi yana tsaye a bakin kofar shigowa fuskarsa a mugun 'bace! Gabana na faduwa na mike zaune ina kallonsa, cikin wani irin taku ya karaso inda nake sai na sunkuyar da kaina kasa ina addua a cikin zuciyata ha'ki'kanin gaskiya Yaya Aminu ya zame min mijin jaraba bala'in tsoron masifarsa nake.
"Da wane namiji kike waya."? maganarsa ta daki kunnena. kai a sunkuye nace.''Khalid ne."? Waye Khalid.''? ya fada cikin sigar zargi Dauriya na aro na kalleshi da fadin." Yaya Aminu Khalid din ne baka sani ba."? A zafafe ya daga min hannu da fad'in."Kada ki mayar dani shashasha mana kina waya da wani d'an iskan kice Khalid ne.'' Nace."To ai sai ka duba wayar ka gani ni bana munafurci mutukar nasan nayi abu to zan fad'a." Wayar hannuna ya fizge yana dubawa yake fadin."Na lura dake baki da mutunci da sanin ya kamata ba to zan sanya ido sosai a kanki domin ba zan lamunci ki zubar min da mutunci ba."
Murmushin takaici nayi nace."Wane irin mutunci kuma? Yaya Aminu ai kai zaka siyawa kanka mutunci ni wallahi daidai da 'kwayar zarrah bana ganin mutuncin ka." Ido ya tsira min nasan mamakin maganata yake dauke kaina nayi ina sake tamke fuskata 'kwafa yayi cikin bacin rai yace."Saboda kin kasa samun abinda kike so daga guri na shine kike bibiyar mazan waje ko.'' ? Da sauri na kalleshi idanuwa na sun tara ruwa nace."Sharrin da za kayi min kenan."? Cikin sigar rashin mutunci yace." Ke baki isa ayi miki sharri ba gaskiya ce wannan kada kiyi tsammanin ban san dalilin da yasa tsohon mijinki ya sake ki ba kada kuma kiyi tunanin cewa ba san irin iskancin da kike da maza a gurin aikin ki ba nasan komai nayi binkice sosai a kanki kafin na amince a d'aura min aure dake wannan dalilin ne yasa naqi mayar da hankali gurin shan magani domin kuwa banga amfanin had'a zuria dake ba.''
Wasu irin hawaye ne suka kwace min kallonsa kawai nake bakina na rawa na kasa magana tsabar mamaki da al'ajabi.