Sashe 75
Ga Irinta Nan Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Muryarta naji tana fad'in "Ai kasan halinta ba'a bata shawara ta dauka ni ai cewa tayi dani Aminu ne ashe bashi bane Alhaji Nura to idan gidansa take so ta koma sai ta d'aura niyya."
Yana kokarin magana na kasara gurin. tsaki yaja da sauri ya bar gurin yana wani irin huci! Kallo na bishi dashi ina mamakin sa.
Magana take kokarin yi na daga mata hannu da fadin."Gwaggo don Allah bar maganar nan raina a 'bace yake a halin yanzu."
Da sauri tace."Ai dole kiyi bacin rai tunda ke ba zaki dinga fad'ar gaskiya ba.
Murya na rawa nace."Wai ke Gwaggo dan Allah duk abinda Khalid yayi daidai ne a gurin ki kina jifa yana kirana da shashasha mara hankali sa'ar sa ce ni kome."?
Shuru tayi min nace."To idan baki masa magana ba wallahi ransa zai 'baci dan ba zan kyaleshi ba.'' Tace." Ai gaskiya ya fad'a me kike kufalaci a gurin Alhaji Nura bayan kin san irin zaman da kikayi dashi a baya."
Nace." Ni dai kawai addua zaki min bana son k'ananun magana ki nema min alkairi a gurin Allah."
Tace."To Allah ya za'ba miki abinda yafi alkairi.'' amsawa nayi da ameeen Na shiga d'akin raina duk a 'bace Gwaggo duk cika bakinta akan Yaron na banza ne zaiyi mata laifi ta gama surutai da cin alwashi a kansa amma daga zarar yazo shikkenan sai ta manta. tayi tai masa rawar jiki tamkar wanda ya sammace ta.
Khalid da asubar fari ya fita motsa jiki can filin wasa na Sharad'a Har muka gama shirye-shiryen mu muka had'a tsaraba muka tafi k'auyen D'ambatta bai dawo gidan ba......Ummatu kuwa yini tayi cikin walwala da farin ciki danginta suka cika gidan suna d'orawa da saukewa.
Sosai ranshi ya 'baci da ya dawo ya tarar da basa nan wayarsa ya dauko ya lalubi number ta ya shiga gurin kira.
Ina kallon kiran nashi naqu d'aga wa domin yayi masifar bani haushi jiya da daddare ya kira ya kai sau hudu ban daga ba ya hakura da kiran. Kwanciya na gyara kan gadon bunun Baba Ladidi ina jiyo hirarsu a tsakar gidan Gwaggo ta samu 'yan uwa sai fara'a da farin ciki takeyi su kuma sun ke waye ta kowanne da kwanon abincinsa suna farin ciki da zuwanta garin nasu na gado.
"Sa'ida wai Gwaggo tace ki fito kici abinci." muryar Jikar Baba Ladadi naji a kunnena.
Ba tare dana tashi zaune ba nace."Kice gani nan zuwa.'' Yarinyar ta juya da sauri ta fita.
Zaune na mike ina gyara dankwalina ya sake kiran wayar......Dauka nayi a hasale nace."Wai menene."? Ajiyar zuciya ya sauke yace."Ki had'ani da Gwaggo za muyi magana."
"Okey." abinda nace kenan na kashe wayar gabadaya na ajiyeta. fita nayi tsakar gidan na samesu suna hira sai raha suke a tsakaninsu.
A takaice dai sai da waya ta tayi kwana hudu a kashe sannan na kunna ina sane nayi masa haka saboda na kuntukawa zuciyarsa.
Text messages d'insa ne suka shigo har uku ko wanne sai da na bud'e na karanta dukkaninsu ba'kar magana ce dan zagi na ne kawai beyi ba ya kira ni da shashasha ya kai sau nawa har da fadin Ban san inda yake min ciwo ba. tsabar bakin ciki da takaici ya sani zubar da hawaye.....nasa hannu na goge da fadin.'"Yaron nan ya gama raina min hankali Allah ka cire min jarabar sonsa a zuciyata.
Aikin gidan ake gadan-gadan domin k'wararrun ma'aikata ya d'auko suka ruguje gidan abinka da tsohon gini irin nada sosai aka samu fili ba tare da 'bata lokaci ba ma'aikata suka fitar da Foundation na zamani aka shiga aikin gidan babu kama hannun yaro........ cikin sati biyu anyi an gama sai abinda ba'a rasa ba gida yayi kyau mutuka ya haske layin Khalid ya kashe kudi sosai gurin aikin gidan Kofar Gwaggo daban Kofar Ummatu daban komai iri daya ya sa musu set na gado da kujeru da sauran abubuwan bukata Ummatu ta dawo amarya gwaggo ma haka. Ummatu ta dinga jin haushin hakan 'yan uwanta na zugata dan kakarsa Baito kishin Gwaggo take sosai ta turkeshi da masifa akan lallai itama sai ya gyara mata gidanta ya sanja mata kayan daki.'' Yace."Shikkenan ta bari idan an kwana biyu zaiyi mata. Hankalinta ne ya kwanta jin abinda yace.
Muna can bamu san abinda ke faruwa ba domin tuntuni ya daina kiran waya ta tunda ba dauka nake ba, kwanan mu ashirin da biyar muka fara shirye-shiryen tafiya.
Tsarabar da mutan kauyen suka had'a mana har taso tayi yawa nace."Baba Ladidi a wace mota zaku kaimu gida da wannan uban kayan." Tace."Ai ba za'a rasa a kori kura ba yanzu idan na fita zan shiga gidan Dije mijinta a kori kura yake ja sai ta fada masa cewa gobe zai dauki kaya ya kai birni.'' Gwaggo tace."To hakan yayi Allah ya kaimu goben." Ta amsa da ameeen ya Allah.
Da daddare ina shirye-shiryen kwanciya ya kira wayar cikin mamaki na dauka ina dubawa ina so naji muryarsa amma kuma ina gudun ya 'bata min rai da ba'kar maganarsa.
Daga wayar nayi a nutse nayi sallama. ya amsa a cunkushe da fad'in." Yaushe zaku dawo gida.''? "Gobe idan Allah ya kaimu." Yace."Okey to kada ku biyo motar haya zan zo na dauke ku domin nima inaso na gaisa da dangi na kuma nuna musu matar da zan aura.''
Nace."Okey to sai kazo din." da sauri na kashe wayar gabana na wani irin fad'uwa! Zai zo ya nuna musu matar da zai aura lallai Khalid wato yana so ya kuntukawa rayuwata tunda ya gane inda na dosa a kansa.
Da kyar bacci ya dauke ni na tashi sukuku don da kyar ma na karya nayi wanka na kimtsa jikina jama'ar garin sai shigowa sallama sukeyi.......Gwaggo kuwa sai share hawaye take sam bata so ta tafi ta bar 'yan uwanta.
Kiran wayarsa ya tabbatar min da cewa ya shigo garin....da kyar nace."Idan ka tambayi gidan Malam mai doki kazo gidan ai babu wuyar kwatance." Yana kokarin magana na datse wayar ina jan tsaki!
Ransa ya 'baci da abinda tayi masa ya ajiye wayar ya cigaba da tafiya da motar a hankali a hankali yana taka busassun kararen ice.
Jamila dake gefensa a zaune tace." Ya Khalid baka ta'ba zuwa bane naji kana tambayar kwatancen gidan."?
Ba tare da ya kalleta ba yace."Tun ina yaro k'arami rabo na da garin kinga kuwa dole kaina ya juye.''
Tace."Eh gaskiya ne kuma amma garin ya burgeni wallahi idan mukayi aure zamu dinga zuwa akai akai muna shan iska." Murmushi kawai yayi ya cigaba da juya sitiyarin motar.
Da kyar suka samu gidan yara yaran k'auyen suka cika bakin motar suna shafawa.
Gwaggo da kanta ta fito domin tar'bar sa sai dai ganinsa tare da Jamila yasa fara'ar fuskarta tayi rauni kadaran kadahan ta amsa gaisuwarta ta jagorance su shiga cikin gidan.
Tsakar gidan akayi musu shimfid'a jama'a maza da mata suka shiga turereniyar zuwa gaisuwa........Ya fito da kudi ya dinda basu yana Jin dadin yanda suke masa addua da fatan alkairi.
Duk abinda ke faruwa ina daki a kwance ina jinsu inaso na fito domin nayi tozali dashi ina jin takaicin na had'a idona da yarinyar.
Baba Larai ta kalli Jamila da fadin" Wato shine kika biyo shi saboda kada na riqeshi na hanashi tafiya ko to komai dai abinki nice Uwargidansa domin itama Gwaggon baya na take bi saboda haka duk ado da kwalliyar ki baki kama kafafuna ba."
Jamila ta dinga Dariya tana 'boye fuskarta ina jinsa yana tare mata da fadin." Ni me zanyi daku duk kun tsufa mussaman ke Baba Ladidi jikin ki duk jijiya da kai duk furfura babu abinda zaki burgeni dashi." Baba Ladidi ta riqe baki tana fadin."Wato wulakanci zakayi min kenan to ai da tsohuwar zuma ake magani kuma dame matar taka tafi ni itama ai bata da wani kumarin kirki dubeta kamar ka busheta tafad'i."
Gwaggo ta ta'be baki da fad'in "Aikuwa haka yaji ya gani sai yaje yayi ta fama watakila kuma a gaba za tayi qiba." Jamila shuru tayi jikinta duk yayi sanyi gabadaya taji wani irin tsanar Gwaggo a cikin ranta.
Sai da zamu tafi tukkuna na fito daga d'akin Uffan bance musu ba na kama hanyar fita Baba Ladidi tace.''Ke kuma ta bizaro babu sallama kinyi gaba na lura da akwai abinda ke damunki domin tun jiya kike nukufurci."
Kallonta nayi da fadin."Baba Ladidi sau dubu kike so nayi miki sallama ne.'' Tace."Ai wannan salamar daban take da sauran wacce mukayi." Nace."To shikkenan mu zamu tafi sai an kwana biyu." Tace."To Allah ya sadamu da alkairi muna jiran tsammani Allah ya kawo miki miji nagari muzo musha biki."
A zucci na amsa da ameeen nayi saurin ficewa daga gidan....
*96*
Jikin motar suka same ni a jingine kauda kaina nayi har suka karaso gurin 'yan uwa da abokanan arziki sun kewaye motar sai bankwana suke mana Gwaggo sai hawaye take sharewa Baba Ladidi na taya ta nace."Dan Allah sallamar ta isa haka Gwaggo shigo mota mu tafi idan kuma baki gaji da zama a garin ba sai ki koma ki zauna mu dai tafiya zamuyi." Baba Ladidi tace."Rufe min baki ja'ira kawai dama ai ke na lura kamar dole akayi miki kika zauna damu komai abinki garin Dambatta shine tushen ki."
Yanda take masifa tana tada jijiyar wuya abin ya bani dariya gaban motar na bude na zauna da fadin."To ni dai na shiga mota Allah ya kaddara saduwarmu." Jamila tayi kicin-kicin da fuska ganin na zauna mata a mazauni ni kuwa ina sane nayi hakan domin da ita dashi dik neman rigima nake dasu.
Gwaggo da kyar 'yan uwa suka barta ta shiga motar Shi kuma ya tsaya yana sallamarsu sosai yayi musu rabon kudi tamkar wanda bai san ciwonsa ba.
Kokarin bude motar yake ya ganta a tsaye tasha kunu yace."Jamila shiga mota mu tafi mana."
A marairace tace."Yaya Khalid ai ta zauna min a mazaunina."
Cikin motar ya duba ya ga yanda na wani 'kame a zaune kaina na dauke ina sake cin magani......Wani irin kwarjini tayi masa ya kalleta da fadin."Ki bata guri ta zauna mana."
Ko kallonsa banyi ba, Gwaggo tace."Jarumi wai tsayuwar me kukeyi ne kai da ita."?
Yana kokarin magana na kasara gurin. tsaki yaja da sauri ya bar gurin yana wani irin huci! Kallo na bishi dashi ina mamakin sa.
Magana take kokarin yi na daga mata hannu da fadin."Gwaggo don Allah bar maganar nan raina a 'bace yake a halin yanzu."
Da sauri tace."Ai dole kiyi bacin rai tunda ke ba zaki dinga fad'ar gaskiya ba.
Murya na rawa nace."Wai ke Gwaggo dan Allah duk abinda Khalid yayi daidai ne a gurin ki kina jifa yana kirana da shashasha mara hankali sa'ar sa ce ni kome."?
Shuru tayi min nace."To idan baki masa magana ba wallahi ransa zai 'baci dan ba zan kyaleshi ba.'' Tace." Ai gaskiya ya fad'a me kike kufalaci a gurin Alhaji Nura bayan kin san irin zaman da kikayi dashi a baya."
Nace." Ni dai kawai addua zaki min bana son k'ananun magana ki nema min alkairi a gurin Allah."
Tace."To Allah ya za'ba miki abinda yafi alkairi.'' amsawa nayi da ameeen Na shiga d'akin raina duk a 'bace Gwaggo duk cika bakinta akan Yaron na banza ne zaiyi mata laifi ta gama surutai da cin alwashi a kansa amma daga zarar yazo shikkenan sai ta manta. tayi tai masa rawar jiki tamkar wanda ya sammace ta.
Khalid da asubar fari ya fita motsa jiki can filin wasa na Sharad'a Har muka gama shirye-shiryen mu muka had'a tsaraba muka tafi k'auyen D'ambatta bai dawo gidan ba......Ummatu kuwa yini tayi cikin walwala da farin ciki danginta suka cika gidan suna d'orawa da saukewa.
Sosai ranshi ya 'baci da ya dawo ya tarar da basa nan wayarsa ya dauko ya lalubi number ta ya shiga gurin kira.
Ina kallon kiran nashi naqu d'aga wa domin yayi masifar bani haushi jiya da daddare ya kira ya kai sau hudu ban daga ba ya hakura da kiran. Kwanciya na gyara kan gadon bunun Baba Ladidi ina jiyo hirarsu a tsakar gidan Gwaggo ta samu 'yan uwa sai fara'a da farin ciki takeyi su kuma sun ke waye ta kowanne da kwanon abincinsa suna farin ciki da zuwanta garin nasu na gado.
"Sa'ida wai Gwaggo tace ki fito kici abinci." muryar Jikar Baba Ladadi naji a kunnena.
Ba tare dana tashi zaune ba nace."Kice gani nan zuwa.'' Yarinyar ta juya da sauri ta fita.
Zaune na mike ina gyara dankwalina ya sake kiran wayar......Dauka nayi a hasale nace."Wai menene."? Ajiyar zuciya ya sauke yace."Ki had'ani da Gwaggo za muyi magana."
"Okey." abinda nace kenan na kashe wayar gabadaya na ajiyeta. fita nayi tsakar gidan na samesu suna hira sai raha suke a tsakaninsu.
A takaice dai sai da waya ta tayi kwana hudu a kashe sannan na kunna ina sane nayi masa haka saboda na kuntukawa zuciyarsa.
Text messages d'insa ne suka shigo har uku ko wanne sai da na bud'e na karanta dukkaninsu ba'kar magana ce dan zagi na ne kawai beyi ba ya kira ni da shashasha ya kai sau nawa har da fadin Ban san inda yake min ciwo ba. tsabar bakin ciki da takaici ya sani zubar da hawaye.....nasa hannu na goge da fadin.'"Yaron nan ya gama raina min hankali Allah ka cire min jarabar sonsa a zuciyata.
Aikin gidan ake gadan-gadan domin k'wararrun ma'aikata ya d'auko suka ruguje gidan abinka da tsohon gini irin nada sosai aka samu fili ba tare da 'bata lokaci ba ma'aikata suka fitar da Foundation na zamani aka shiga aikin gidan babu kama hannun yaro........ cikin sati biyu anyi an gama sai abinda ba'a rasa ba gida yayi kyau mutuka ya haske layin Khalid ya kashe kudi sosai gurin aikin gidan Kofar Gwaggo daban Kofar Ummatu daban komai iri daya ya sa musu set na gado da kujeru da sauran abubuwan bukata Ummatu ta dawo amarya gwaggo ma haka. Ummatu ta dinga jin haushin hakan 'yan uwanta na zugata dan kakarsa Baito kishin Gwaggo take sosai ta turkeshi da masifa akan lallai itama sai ya gyara mata gidanta ya sanja mata kayan daki.'' Yace."Shikkenan ta bari idan an kwana biyu zaiyi mata. Hankalinta ne ya kwanta jin abinda yace.
Muna can bamu san abinda ke faruwa ba domin tuntuni ya daina kiran waya ta tunda ba dauka nake ba, kwanan mu ashirin da biyar muka fara shirye-shiryen tafiya.
Tsarabar da mutan kauyen suka had'a mana har taso tayi yawa nace."Baba Ladidi a wace mota zaku kaimu gida da wannan uban kayan." Tace."Ai ba za'a rasa a kori kura ba yanzu idan na fita zan shiga gidan Dije mijinta a kori kura yake ja sai ta fada masa cewa gobe zai dauki kaya ya kai birni.'' Gwaggo tace."To hakan yayi Allah ya kaimu goben." Ta amsa da ameeen ya Allah.
Da daddare ina shirye-shiryen kwanciya ya kira wayar cikin mamaki na dauka ina dubawa ina so naji muryarsa amma kuma ina gudun ya 'bata min rai da ba'kar maganarsa.
Daga wayar nayi a nutse nayi sallama. ya amsa a cunkushe da fad'in." Yaushe zaku dawo gida.''? "Gobe idan Allah ya kaimu." Yace."Okey to kada ku biyo motar haya zan zo na dauke ku domin nima inaso na gaisa da dangi na kuma nuna musu matar da zan aura.''
Nace."Okey to sai kazo din." da sauri na kashe wayar gabana na wani irin fad'uwa! Zai zo ya nuna musu matar da zai aura lallai Khalid wato yana so ya kuntukawa rayuwata tunda ya gane inda na dosa a kansa.
Da kyar bacci ya dauke ni na tashi sukuku don da kyar ma na karya nayi wanka na kimtsa jikina jama'ar garin sai shigowa sallama sukeyi.......Gwaggo kuwa sai share hawaye take sam bata so ta tafi ta bar 'yan uwanta.
Kiran wayarsa ya tabbatar min da cewa ya shigo garin....da kyar nace."Idan ka tambayi gidan Malam mai doki kazo gidan ai babu wuyar kwatance." Yana kokarin magana na datse wayar ina jan tsaki!
Ransa ya 'baci da abinda tayi masa ya ajiye wayar ya cigaba da tafiya da motar a hankali a hankali yana taka busassun kararen ice.
Jamila dake gefensa a zaune tace." Ya Khalid baka ta'ba zuwa bane naji kana tambayar kwatancen gidan."?
Ba tare da ya kalleta ba yace."Tun ina yaro k'arami rabo na da garin kinga kuwa dole kaina ya juye.''
Tace."Eh gaskiya ne kuma amma garin ya burgeni wallahi idan mukayi aure zamu dinga zuwa akai akai muna shan iska." Murmushi kawai yayi ya cigaba da juya sitiyarin motar.
Da kyar suka samu gidan yara yaran k'auyen suka cika bakin motar suna shafawa.
Gwaggo da kanta ta fito domin tar'bar sa sai dai ganinsa tare da Jamila yasa fara'ar fuskarta tayi rauni kadaran kadahan ta amsa gaisuwarta ta jagorance su shiga cikin gidan.
Tsakar gidan akayi musu shimfid'a jama'a maza da mata suka shiga turereniyar zuwa gaisuwa........Ya fito da kudi ya dinda basu yana Jin dadin yanda suke masa addua da fatan alkairi.
Duk abinda ke faruwa ina daki a kwance ina jinsu inaso na fito domin nayi tozali dashi ina jin takaicin na had'a idona da yarinyar.
Baba Larai ta kalli Jamila da fadin" Wato shine kika biyo shi saboda kada na riqeshi na hanashi tafiya ko to komai dai abinki nice Uwargidansa domin itama Gwaggon baya na take bi saboda haka duk ado da kwalliyar ki baki kama kafafuna ba."
Jamila ta dinga Dariya tana 'boye fuskarta ina jinsa yana tare mata da fadin." Ni me zanyi daku duk kun tsufa mussaman ke Baba Ladidi jikin ki duk jijiya da kai duk furfura babu abinda zaki burgeni dashi." Baba Ladidi ta riqe baki tana fadin."Wato wulakanci zakayi min kenan to ai da tsohuwar zuma ake magani kuma dame matar taka tafi ni itama ai bata da wani kumarin kirki dubeta kamar ka busheta tafad'i."
Gwaggo ta ta'be baki da fad'in "Aikuwa haka yaji ya gani sai yaje yayi ta fama watakila kuma a gaba za tayi qiba." Jamila shuru tayi jikinta duk yayi sanyi gabadaya taji wani irin tsanar Gwaggo a cikin ranta.
Sai da zamu tafi tukkuna na fito daga d'akin Uffan bance musu ba na kama hanyar fita Baba Ladidi tace.''Ke kuma ta bizaro babu sallama kinyi gaba na lura da akwai abinda ke damunki domin tun jiya kike nukufurci."
Kallonta nayi da fadin."Baba Ladidi sau dubu kike so nayi miki sallama ne.'' Tace."Ai wannan salamar daban take da sauran wacce mukayi." Nace."To shikkenan mu zamu tafi sai an kwana biyu." Tace."To Allah ya sadamu da alkairi muna jiran tsammani Allah ya kawo miki miji nagari muzo musha biki."
A zucci na amsa da ameeen nayi saurin ficewa daga gidan....
*96*
Jikin motar suka same ni a jingine kauda kaina nayi har suka karaso gurin 'yan uwa da abokanan arziki sun kewaye motar sai bankwana suke mana Gwaggo sai hawaye take sharewa Baba Ladidi na taya ta nace."Dan Allah sallamar ta isa haka Gwaggo shigo mota mu tafi idan kuma baki gaji da zama a garin ba sai ki koma ki zauna mu dai tafiya zamuyi." Baba Ladidi tace."Rufe min baki ja'ira kawai dama ai ke na lura kamar dole akayi miki kika zauna damu komai abinki garin Dambatta shine tushen ki."
Yanda take masifa tana tada jijiyar wuya abin ya bani dariya gaban motar na bude na zauna da fadin."To ni dai na shiga mota Allah ya kaddara saduwarmu." Jamila tayi kicin-kicin da fuska ganin na zauna mata a mazauni ni kuwa ina sane nayi hakan domin da ita dashi dik neman rigima nake dasu.
Gwaggo da kyar 'yan uwa suka barta ta shiga motar Shi kuma ya tsaya yana sallamarsu sosai yayi musu rabon kudi tamkar wanda bai san ciwonsa ba.
Kokarin bude motar yake ya ganta a tsaye tasha kunu yace."Jamila shiga mota mu tafi mana."
A marairace tace."Yaya Khalid ai ta zauna min a mazaunina."
Cikin motar ya duba ya ga yanda na wani 'kame a zaune kaina na dauke ina sake cin magani......Wani irin kwarjini tayi masa ya kalleta da fadin."Ki bata guri ta zauna mana."
Ko kallonsa banyi ba, Gwaggo tace."Jarumi wai tsayuwar me kukeyi ne kai da ita."?