Sashe 58
Ga Irinta Nan Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tace."Humm! Khalid dole nayi surutu wannan wane irin gantalallan aure ne da za'a d'aura shi babu ango a kusa wato kudi ya fi mutunci ko? duk wanda yaga haka zaice dama kudinsa muka gani muka bashi auran 'yarmu."
Yace."Nifa ban fahimce ki."? A nutse ta warware masa abinda yake faruwa....Yace."To ai ba laifi bane don anyi daurin aure babu ango a kusa sau tari hakan na faruwa kuma hakan ba yana nufin cewa aure bai d'auru ba aure ya dauru mutukar an d'aura shi akan tsari da shedu da kuma waliyyai sabida haka don Allah ki daina wannan surutan."
Gwaggo shuru tayi tana kallonsa mamaki dan'kare a zuciyarta tace."Khalid kai kake fadar wannan maganar kanka tsaye yaushe Allah yasa maka dangana haka."?
Murmushi yayi yace." Tuntuni Allah yasa min dangana Gwaggo ai na barwa Allah komai na hakura da Aunty Sa'ida tunda ba alkari ce a tare dani ba."
Zaune na mike ina kallonsa sam banji dadin maganarsa ba. kallona yayi na second guda ya dauke kansa agogon hannunsa ya duba da fadin."Ni zan dan fita gurin abokaina." Tace."To shikkenan sai ka dawo." Ba tare da yace komai ba ya bar gurin.
Kaina na sunkuyar kasa ina mamakin sadudar yaron ikon Allah lokaci guda yayi sanyi ya mikawa Allah lamarin duk tsananin kishi irin na Khalid wai shine yake musabaha da wanda zan aura hakika al'amarin ya bani mamaki mutuka.
To kamar yanda ango ya tsara al'amarin hakane ya kasance kwanasa biyu da tafiya kasar india aka daura auran kuma a ranar na tare a dan'kareran gidana dake Unguwar Jambulo gida gari guda komai na more rayuwa akwai a gidan Yaya Aminu jin dadi dai na duniya na sameshi sai dai fatan zaman lafiya Layuza da Karima 'kannansa su aka turo domin su taya ni zama kafin ya dawo naji dadin zuwansu sosai dama mun saba dasu tunda ina ziyaryar gidansu sa'i da lokaci, bamu da fargabar komai gidan tunda akwai matakan tsaro a gidan sosai akwai securities masu dagi da karninuka a Estate d'in.
*72&73*
A ranar da Gwaggo tazo gidan sai da ta kusa bani kunya gabansu Layuza sai wasu irin maganganu takeyi akan gidan da kuma maigidan sai da nayi mata jan ido tukkuna tayi shuru da bakinta tana yin sallar azuhur tace ita tafiya za tayi abubuwan kwad'ayi na had'a mata masu yawa nasa direba ya dauketa ya kaita har gida, Gwaggo koda ta koma gidan kasa shuru tayi da bakinta da Kawu Iro ya shigo ta tare shi da maganar wai anya kuwa A harkar kasuwanci Yaya Aminu ya tsaya baya yakan kai wannan uwar dukiya daka gani bata Allah da Annabi bace." Kawu Iro zaunar da ita yayi ya dinga yi mata nasiha gami da kawo mata misalai Allah yakan arzita bawansa da dukiyar da bai san iya adadinta ba saboda haka ta kwantar da hankalinta duk wani binkice yayi ya kuma tabbatar da cewa mutumin a harkar kasuwanci ya tsaya." Gwaggo dai shuru tayi da bakinta tana jajanta al'amarin.
Gwaggo kullum za tayi girkin ta da nama taci ta koshi ta ajiyewa mutumin nata idan ya dawo tace masa yazo yaci abinci kai tsaye yake ce mata ba zai ci ba ya gwammace yaci garau-garau din da mahaifiyarsa tayi ko kuma yaci aljihunsa.....Gwaggo tayi tai masa naci shi kuwa yace."Ba zai ci ba dole take hakuri ta kira almajirai ta raba musu sadaka.
"Khalid kwata-kwata fa ni ban amince maka da wannan tafiyar ba, kai harkar ball din ma gabadaya bana sonka da ita ka hakura ka zauna a gida ka fara kasuwanci shine yafi alkairi a tattare da kai.
Cikin wani irin yanayi na damuwa yake kallon mahaifin nasa yace." Baba kayi hakuri ka lamunce min tafiyar nan akwai nasara a cikinta.
Kawu Iro yace."Ai dama duk hanyar shaid'anci zaka samu nasara a tare da ita hanyar Allah da Annabi kuwa kun dinga kawo suka a cikinta to ni dai na gama magana mutukar ni na haifeka ban lamunce maka tafiya wata america ba.
Kawu Iro na gama maganarsa ya bar gurin.....Ya jima a tsugune a gurin yana sa'kawa da kwancewa kafin ya mike kai tsaye gurin Gwaggo ya nufa domin kuwa yana ganin itace kadai zata iya tursasa mahaifinsa ya barshi ya tafi inda yake muradi.
Tana zaune da kwanon farfesun kaji a gabanta gefe ga lemo nan irin na kwali farfesun take sha hankali a kwance Gwaggo har wani qiba tayi saboda ka'bakin arzikin da Sa'ida take kawo mata duk bayan kwana uku ko hud'u......Dakin ya shiga ya zauna yana kallonsa....Sai ta tura masa kwanon farfesun da fadin."Gashinan ko kayi sha'awa."
Girgiza kansa yayi yace."Bana bukata." Kwanon farfesun ta janye ta cigaba dasha tana tauna tsokar data dahu luguf.
Yace."Gwaggo Alfarma nake nema a gurun ki." Tace."Ai dama tinda naga ka shigo dakina ka zauna nasan da walakin goro a miya.
Sajensa ya shafa yace."Eh wallahi Gwaggo ke kadai ce zaki umarci Kawu Yayi abinda kike so."
Tace."Eh kwarai kuwa ai mahaifinka yana da biyayya duk abinda nace inaso to shima yana so.
Yace." Yawwa Gwaggo dan Allah kice masa ya barni na koma gurin sana'ata."
Tace."To akan me dama zaice ba zaka koma ba."? Yace."Kin san kwanaki nayi miki magana kancewa zamuje america muyi wasa to tafiyar ce ta taso dan tun satin da ya wuce oganmu yake kiran waya ta na bashi hakuri kancewa insha Allahu ya tsammaci zuwa na a cikin satin nan to kuma yanzu da nake shedawa Kawun maganar yake cewa shi bai amince ba.
Tana sud'e hannunta tace."Khalid wace irin ball ce har sai anje america mai zai hana ka ka cigaba da buga abarka a cikin 'kasar ka nima wallahi sam bana sonka da wannan harkar.
Yace."Gwaggo kada kice haka mana zuwa na america matakin nasara ne domin kuwa zanje mu fafata da manya manyan 'yan ball wanda suka shahara sukayi suna duniya tasan dasu."
Hararasa tayi tace."Kai kuma shahara kake nema da makiya Allah da Annabi kenan."? Girgiza kansa yayi da sauri yace."Aa Gwaggo ai ba kafurai ne kawai ba harda musulmai a ciki kowa yana kokarin ya nuna bajintarsa ne."
Shuru tayi masa ya matsa kusa da ita gami da rike hannunta yana rarrashinta. Tace."Shikkenan ka kwantar da hankalin ka zan sameshi muyi magana Allah ya za'ba maka abinda yafi alkairi."
Cike da farin ciki ya amsa da ameeen Uwargidana." Harararsa tayi tace."Ina uwargidanka amma ka daina cin abincina ko da yake ai nasan uwarka ce take zuga ka." Cikin kulawa ya kalleta da fadin."Gwaggo babu ruwan Ummatu ni ne dai ba zanci wani abu da ya shafi aunty Sa'ida ba kin san haka tsarina yake ba tun yau ba.
Tace."In banda abinka kuma wane kishi za kayi bayan komai ya wuce kake cutar kanka." Yace."Kinga Gwaggo dan Allah a bar maganar duk nau'in abincin da nake so naci ina da kudin siya ba sai kin tursasa ni naci abincin ki ba.
Tace."To ai shikkenan tunda haka ka za'ba, mi'kewa yayi yana kallon agogon hannunsa yace."Ni zan fita gurin abokaina." Tace."To sai ka dawo." Fitowa yayi tare da sa takalmansa ya fita daga gidan.
Kullum ta Allah Yaya Aminu yakan kira waya ta sau biyu ko uku mu jima muna hira dashi al'amarin ya dinga bani mamaki ganin gabadaya baya nuna wani d'oki da zumud'in irin na angwaye idan ya kira waya ta hirar kasuwancinsa kawai yake min babu wata kalma mai dadi irin to so da nuna cewa ina bukatar ki abin ya dinga bani mamaki yana sani a cikin damuwa! a gaskiyar magana lamarin yana min ciwo sabida ni na kasance mace mai son soyayya inaso naga namiji na kula dani da nuna min so......Amma Yaya Aminu sam babu wannan a tare dashi shidai harkokinsa yasa a gaba.
Yau asabar Allah yayi nufin dawowarsa sosai nayi gayu cikin shaddan galila taji uban stone work nayi ado da gold wuya da hannu sai zuba kamshin tururuka nakeyi ni kaina dana tsaya gaban mirror sai da nayi mamakin uban kyawun da nayi......Amma abin mamaki wanda akayi kwalliyar dominsa bai wani kula sosai ba dan bayan na bashi abinci yaci dakinsa ya bude ya shiga ya kwanta, sai nayi tunanin binsa dakin koda na ta'ba kofar sai naji a kulle. jiki a sabule na bar gurin zama nayi kujerar falo abin duniya ya dame ni, ga Layuza da Karima sun tafi sai ya kasance ni kadai a gidan dana gaji da zaman falo mikewa nayi na shige dakina na kwanta kawai sai hawaye suka 'balle min wannan wane irin ango ne mara kula. sosai naci kuka na na koshi bacci ya dauke ni.
Sai daf da la'asar na tashi a gurguje nayi wanka na fito daure da alwala sai dana kimtsa jikina tukkuna na tsaya kan dadduma na tayar da sallah.
Ina sallama ya shigo dakin daga kai nayi ina kallonsa kamshin turaransa duk ya cika dakin a shirye yake da alama futa zaiyi.....zama yayi gefan gado har na shafa addua na juyo muka hada ido dashi, murmushi yayi min da fadin"Amarya." ya'ke kawai nayi naje na zauna kusa dashi tare da gaishe shi, ya amsa cikin kulawa ido ya tsira min kafin yace."Naga idanuwanki sunyi jawur ina fata ba wata matsala bace."
Daurewa nayi nace."Babu komai bacci nayi shiyasa idon ya sanja." Yace."Okey to ya kike ya zaman kadaici." Mirmushi kawai nayi ban tanka masa ba.
Ya kalli agogon hannunsa da fadin."Ni zanje babban gida mu gaisa dasu." Nace."To ka gashe min dasu." Mikewa yayi yana fadin."Insha Allahu zasuji sa'kon ki.
Bayansa nabi da kallo har ya bude dakin ya fita.....Jingina baya na nayi jikin gadon na shiga tunanin rayuwa.
Sai kusan tara da rabi ya shigo gidan, gani na a zaune a falo ya bashi mamaki yace."Baki bacci ba."? A nutse na mike da fadin."Eh na tsaya ka dawo ne." Murmushi yayi na kar'bi wayoyinsa ina masa barka da zuwa.
Amsawa yayi ya rike hannuna muka nufi dakinsa.
Yace."Nifa ban fahimce ki."? A nutse ta warware masa abinda yake faruwa....Yace."To ai ba laifi bane don anyi daurin aure babu ango a kusa sau tari hakan na faruwa kuma hakan ba yana nufin cewa aure bai d'auru ba aure ya dauru mutukar an d'aura shi akan tsari da shedu da kuma waliyyai sabida haka don Allah ki daina wannan surutan."
Gwaggo shuru tayi tana kallonsa mamaki dan'kare a zuciyarta tace."Khalid kai kake fadar wannan maganar kanka tsaye yaushe Allah yasa maka dangana haka."?
Murmushi yayi yace." Tuntuni Allah yasa min dangana Gwaggo ai na barwa Allah komai na hakura da Aunty Sa'ida tunda ba alkari ce a tare dani ba."
Zaune na mike ina kallonsa sam banji dadin maganarsa ba. kallona yayi na second guda ya dauke kansa agogon hannunsa ya duba da fadin."Ni zan dan fita gurin abokaina." Tace."To shikkenan sai ka dawo." Ba tare da yace komai ba ya bar gurin.
Kaina na sunkuyar kasa ina mamakin sadudar yaron ikon Allah lokaci guda yayi sanyi ya mikawa Allah lamarin duk tsananin kishi irin na Khalid wai shine yake musabaha da wanda zan aura hakika al'amarin ya bani mamaki mutuka.
To kamar yanda ango ya tsara al'amarin hakane ya kasance kwanasa biyu da tafiya kasar india aka daura auran kuma a ranar na tare a dan'kareran gidana dake Unguwar Jambulo gida gari guda komai na more rayuwa akwai a gidan Yaya Aminu jin dadi dai na duniya na sameshi sai dai fatan zaman lafiya Layuza da Karima 'kannansa su aka turo domin su taya ni zama kafin ya dawo naji dadin zuwansu sosai dama mun saba dasu tunda ina ziyaryar gidansu sa'i da lokaci, bamu da fargabar komai gidan tunda akwai matakan tsaro a gidan sosai akwai securities masu dagi da karninuka a Estate d'in.
*72&73*
A ranar da Gwaggo tazo gidan sai da ta kusa bani kunya gabansu Layuza sai wasu irin maganganu takeyi akan gidan da kuma maigidan sai da nayi mata jan ido tukkuna tayi shuru da bakinta tana yin sallar azuhur tace ita tafiya za tayi abubuwan kwad'ayi na had'a mata masu yawa nasa direba ya dauketa ya kaita har gida, Gwaggo koda ta koma gidan kasa shuru tayi da bakinta da Kawu Iro ya shigo ta tare shi da maganar wai anya kuwa A harkar kasuwanci Yaya Aminu ya tsaya baya yakan kai wannan uwar dukiya daka gani bata Allah da Annabi bace." Kawu Iro zaunar da ita yayi ya dinga yi mata nasiha gami da kawo mata misalai Allah yakan arzita bawansa da dukiyar da bai san iya adadinta ba saboda haka ta kwantar da hankalinta duk wani binkice yayi ya kuma tabbatar da cewa mutumin a harkar kasuwanci ya tsaya." Gwaggo dai shuru tayi da bakinta tana jajanta al'amarin.
Gwaggo kullum za tayi girkin ta da nama taci ta koshi ta ajiyewa mutumin nata idan ya dawo tace masa yazo yaci abinci kai tsaye yake ce mata ba zai ci ba ya gwammace yaci garau-garau din da mahaifiyarsa tayi ko kuma yaci aljihunsa.....Gwaggo tayi tai masa naci shi kuwa yace."Ba zai ci ba dole take hakuri ta kira almajirai ta raba musu sadaka.
"Khalid kwata-kwata fa ni ban amince maka da wannan tafiyar ba, kai harkar ball din ma gabadaya bana sonka da ita ka hakura ka zauna a gida ka fara kasuwanci shine yafi alkairi a tattare da kai.
Cikin wani irin yanayi na damuwa yake kallon mahaifin nasa yace." Baba kayi hakuri ka lamunce min tafiyar nan akwai nasara a cikinta.
Kawu Iro yace."Ai dama duk hanyar shaid'anci zaka samu nasara a tare da ita hanyar Allah da Annabi kuwa kun dinga kawo suka a cikinta to ni dai na gama magana mutukar ni na haifeka ban lamunce maka tafiya wata america ba.
Kawu Iro na gama maganarsa ya bar gurin.....Ya jima a tsugune a gurin yana sa'kawa da kwancewa kafin ya mike kai tsaye gurin Gwaggo ya nufa domin kuwa yana ganin itace kadai zata iya tursasa mahaifinsa ya barshi ya tafi inda yake muradi.
Tana zaune da kwanon farfesun kaji a gabanta gefe ga lemo nan irin na kwali farfesun take sha hankali a kwance Gwaggo har wani qiba tayi saboda ka'bakin arzikin da Sa'ida take kawo mata duk bayan kwana uku ko hud'u......Dakin ya shiga ya zauna yana kallonsa....Sai ta tura masa kwanon farfesun da fadin."Gashinan ko kayi sha'awa."
Girgiza kansa yayi yace."Bana bukata." Kwanon farfesun ta janye ta cigaba dasha tana tauna tsokar data dahu luguf.
Yace."Gwaggo Alfarma nake nema a gurun ki." Tace."Ai dama tinda naga ka shigo dakina ka zauna nasan da walakin goro a miya.
Sajensa ya shafa yace."Eh wallahi Gwaggo ke kadai ce zaki umarci Kawu Yayi abinda kike so."
Tace."Eh kwarai kuwa ai mahaifinka yana da biyayya duk abinda nace inaso to shima yana so.
Yace." Yawwa Gwaggo dan Allah kice masa ya barni na koma gurin sana'ata."
Tace."To akan me dama zaice ba zaka koma ba."? Yace."Kin san kwanaki nayi miki magana kancewa zamuje america muyi wasa to tafiyar ce ta taso dan tun satin da ya wuce oganmu yake kiran waya ta na bashi hakuri kancewa insha Allahu ya tsammaci zuwa na a cikin satin nan to kuma yanzu da nake shedawa Kawun maganar yake cewa shi bai amince ba.
Tana sud'e hannunta tace."Khalid wace irin ball ce har sai anje america mai zai hana ka ka cigaba da buga abarka a cikin 'kasar ka nima wallahi sam bana sonka da wannan harkar.
Yace."Gwaggo kada kice haka mana zuwa na america matakin nasara ne domin kuwa zanje mu fafata da manya manyan 'yan ball wanda suka shahara sukayi suna duniya tasan dasu."
Hararasa tayi tace."Kai kuma shahara kake nema da makiya Allah da Annabi kenan."? Girgiza kansa yayi da sauri yace."Aa Gwaggo ai ba kafurai ne kawai ba harda musulmai a ciki kowa yana kokarin ya nuna bajintarsa ne."
Shuru tayi masa ya matsa kusa da ita gami da rike hannunta yana rarrashinta. Tace."Shikkenan ka kwantar da hankalin ka zan sameshi muyi magana Allah ya za'ba maka abinda yafi alkairi."
Cike da farin ciki ya amsa da ameeen Uwargidana." Harararsa tayi tace."Ina uwargidanka amma ka daina cin abincina ko da yake ai nasan uwarka ce take zuga ka." Cikin kulawa ya kalleta da fadin."Gwaggo babu ruwan Ummatu ni ne dai ba zanci wani abu da ya shafi aunty Sa'ida ba kin san haka tsarina yake ba tun yau ba.
Tace."In banda abinka kuma wane kishi za kayi bayan komai ya wuce kake cutar kanka." Yace."Kinga Gwaggo dan Allah a bar maganar duk nau'in abincin da nake so naci ina da kudin siya ba sai kin tursasa ni naci abincin ki ba.
Tace."To ai shikkenan tunda haka ka za'ba, mi'kewa yayi yana kallon agogon hannunsa yace."Ni zan fita gurin abokaina." Tace."To sai ka dawo." Fitowa yayi tare da sa takalmansa ya fita daga gidan.
Kullum ta Allah Yaya Aminu yakan kira waya ta sau biyu ko uku mu jima muna hira dashi al'amarin ya dinga bani mamaki ganin gabadaya baya nuna wani d'oki da zumud'in irin na angwaye idan ya kira waya ta hirar kasuwancinsa kawai yake min babu wata kalma mai dadi irin to so da nuna cewa ina bukatar ki abin ya dinga bani mamaki yana sani a cikin damuwa! a gaskiyar magana lamarin yana min ciwo sabida ni na kasance mace mai son soyayya inaso naga namiji na kula dani da nuna min so......Amma Yaya Aminu sam babu wannan a tare dashi shidai harkokinsa yasa a gaba.
Yau asabar Allah yayi nufin dawowarsa sosai nayi gayu cikin shaddan galila taji uban stone work nayi ado da gold wuya da hannu sai zuba kamshin tururuka nakeyi ni kaina dana tsaya gaban mirror sai da nayi mamakin uban kyawun da nayi......Amma abin mamaki wanda akayi kwalliyar dominsa bai wani kula sosai ba dan bayan na bashi abinci yaci dakinsa ya bude ya shiga ya kwanta, sai nayi tunanin binsa dakin koda na ta'ba kofar sai naji a kulle. jiki a sabule na bar gurin zama nayi kujerar falo abin duniya ya dame ni, ga Layuza da Karima sun tafi sai ya kasance ni kadai a gidan dana gaji da zaman falo mikewa nayi na shige dakina na kwanta kawai sai hawaye suka 'balle min wannan wane irin ango ne mara kula. sosai naci kuka na na koshi bacci ya dauke ni.
Sai daf da la'asar na tashi a gurguje nayi wanka na fito daure da alwala sai dana kimtsa jikina tukkuna na tsaya kan dadduma na tayar da sallah.
Ina sallama ya shigo dakin daga kai nayi ina kallonsa kamshin turaransa duk ya cika dakin a shirye yake da alama futa zaiyi.....zama yayi gefan gado har na shafa addua na juyo muka hada ido dashi, murmushi yayi min da fadin"Amarya." ya'ke kawai nayi naje na zauna kusa dashi tare da gaishe shi, ya amsa cikin kulawa ido ya tsira min kafin yace."Naga idanuwanki sunyi jawur ina fata ba wata matsala bace."
Daurewa nayi nace."Babu komai bacci nayi shiyasa idon ya sanja." Yace."Okey to ya kike ya zaman kadaici." Mirmushi kawai nayi ban tanka masa ba.
Ya kalli agogon hannunsa da fadin."Ni zanje babban gida mu gaisa dasu." Nace."To ka gashe min dasu." Mikewa yayi yana fadin."Insha Allahu zasuji sa'kon ki.
Bayansa nabi da kallo har ya bude dakin ya fita.....Jingina baya na nayi jikin gadon na shiga tunanin rayuwa.
Sai kusan tara da rabi ya shigo gidan, gani na a zaune a falo ya bashi mamaki yace."Baki bacci ba."? A nutse na mike da fadin."Eh na tsaya ka dawo ne." Murmushi yayi na kar'bi wayoyinsa ina masa barka da zuwa.
Amsawa yayi ya rike hannuna muka nufi dakinsa.