Sashe 11
Ga Irinta Nan Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Karo muka buga a lokacin da yake kokarin shigowa hannunsa rike da wata k'aramar bakar leda.
Yanda yaga jikinta na rawa yasa yayi saurin rike hannunta a nutse yace."Aunty Sa'ida ina zaki da sassafe haka? yau asabar babu makaranta."
Zuciyata ta karye na daure ban bari hawayen sun zuba ba nace."Khalid Sake ni." Girgiza kansa yayi a tausashe yace."Ba zan sake ki ba aunty dan na lura bakya hayyacinki."
Ido na tsira masa shima ya tsira min nasa, a haka Baba Iro ya shigo ya same mu....Gyaran muryar da yayi itace tasa muka ankara da shigowarsa yace."Lafiya na ganku a tsaye a soro."?
Hannuna dake cikin nasa ya sake ri'kewa yace."Baba da alama babu lafiya dan nima nazo shigowa mukayi karo da ita zata fita a gigice.''
A nutse ya kalleni da fadin"Sa'ida me yake faruwa ne.''? Hawayen da nake kokarin dannewa suka kucfe nace ."Kawu maganar dai guda d'aya ce."
Yace."Gwaggo ce ko.''? kaina na d'aga nace"Eh tun jiya ta hanani zaman lafiya a dakinta tace aljanu ne dani kawai yanzu ina kwance na ganta a kaina tana bunka min haya'ki."
Baba Iro ya shiga girgiza kansa yana mamakin halin rigima irin na mahaifiyarsa. yace."Sa'ida kiyi hakuri kinji ko mu shiga gidan za'a sasanta."
Nace."Kawu nifa idan ba haya'kin nan ta daina bunkawa ba ba zan shiga dakinta ba."
Khalid yace."Muje duk inda haya'kin yake zan daukeshi na yar dashi."
Jin abinda yace yasa na yarda muka shiga gidan a tare.
Suna tsaye ita da Ummatu suna magana......"Wallahi ajanu ne da ita gashinan daga jiya zuwa yau duk ta kasa nutsuwa sakamakon turaran da nake mata kinga yanzu tayi waje a gigice." Ummatu tace."To ai kuwa tunda dai an gano bakin zaren sai a cigaba da nema mata magani.....shigowarmu yasa duk suka kallemu.
Khalid kai tsaye dakin ya nufa yana neman maganin Gwaggo kamar ta sani ta dauka ta bawa Ummatu ta 'boye mata....Kawu Iro yace "Gwaggo wannan wace irin rayuwa ce dan Allah ya kike nema ki furgita yarinya kina cewa tana da aljanu a ina suke? Gwaggo na fad'a miki ki daina yarda da surutan mutane akan yarinyar nan shi aure lokaci ne dashi idan lokacinta yayi za tayi aure amma dan Allah ki daina d'ora mata lalura yanzu ina amfanin abinda kikayi Gwaggo da sassafe kin bunka a haya'ki a gida kin firgita yarinya tunda tace bata so ba sai ki k'yaleta ba."
"Kai Ibrahim ba fa zanyi asarar kudina ba dole sai nayi haya'kin nan tunda d'akina ne kuma idan ba aljanun ne da ita ba me yasa take guduwa mu da muke shak'ar haya'kin me yayi mana saboda haka ba zan fasa abinda nayi niyya ba idan tana da inda za taje ta tafi."
Khalid ya fito daga dakin fuska a murtuke yace."Gwaggo ina haya'kin naga irinsa." Kallonsa tayi lokaci guda ta fahimci abinda yake da akwai tace." Babu sauransa kenan nasa a wuta."
Kawu Iro yace."Gwaggo jiya ma fa haka kika ce sai gashi kuma yau da safe kin kuma kunnawa." Kuka ta fashe dashi tace."Yanzu dai kunyi min taron dangi kenan kuna kokarin 'karyata ni ko."?
Kawu Iro hankalinsa ya tashi ya dinga rarrashinta tace."Oh!oh! Ibrahim ai 'yar d'an uwanka ta fini a gurinka tunda gashinan a kanta kana nema ka 'kure ni."
Yace."Aa Gwaggo wallahi ba haka bane ina ni ina 'kure ki nayi laifi ki yafe mun." Ba tare da tace komai ba ta shiga dakinta ta bar mu a tsaye.
Kallonsa nayi naga duk hankalinsa ya tashi nace."Kawu ka kwantar da hankalin ka insha Allahu zan cigaba da hakuri da halinta." Yace."Yawwa Sa'ida dama abinda nake so kenan naji daga gurinki kiyi ta addua kinji ko komai mai wuce wa ne." Cikin dauriya nace."To Kawu nagode." Gurinsu ya nufa ya barmu nida Khalid a tsaye.....Yace."Aunty Sa'ida kada ki damu duk inda ta 'boye haya'kin zan bincika a dakin."
Nace."Khalid kyaleta dakinta ne fa tayi duk abinda take so da abunta." "Eh d'akina ne Sa'ida idan kinyi zuciya kada ki sake shigowa." Tana daga cikin dakin take magana.
Yace."Gwaggo wace irin magana ce wannan."?
"Haba Jarumi ai dole raina ya 'baci akan al'amarin nan ranar da naje 'karbo maganin nan sai da na yini banci ba bansha ba salloli na ma sai had'asu nayi amma saboda wukalancin Sa'ida ta dinga kokarin watsa min 'kasa a ido.
Yace." To wai waye ya saki ne? sai fa da nace dake kada kije okey to zanje har gidan ita Uwalen da take janki yawon gurin masu magani na gargad'eta akan hakan ni idan kinyi min baki ba zai kamani ba tunda dai ni ba Baba Iro ba ne."
Kuka tasa daga cikin dakin take fad'in "Khalid kada kaje kaci mutuncin Uwale bata cancanci hakaba." Ya d'aga labulan d'akin da fad'in."To idan bakya so naje gidan Uwale dauko min haya'kin."
Tace."Shigo ka kar'ba." da sauri ya shiga dakin nima naji wani sanyi a cikin raina.......Wani tsohon magani ta d'auko masa a 'karkashin gadonta a daure a wata tsuhowar leda ta mika masa da fad'in"Gashinan wannan jaraba ta isheni haka."
Kar'ba yayi ba tare da ya tanka mata ba ya fito daga dakin.
Yana fitowa yace." Ki kwantar da hankalinki ga maganin nan a hannuna zan fita dashi na zubar."
Hannunsa na kalla a take na gane ba maganin bane domin wancan a k'ulle yake b'akar leda wannan kuwa ledarsa yaluwa ce.....girgiza kaina kawai nayi na wuce na barshi a gurin, dakin na shiga na sameta tana murd'a redion ta ta dago kanta ta kalleni ta dauke kai tana cigaba da abinda take......gurin dana kwanta na nufa na dauki wayata na nemi gefan gado na zauna wayar na kunna na fara dube dube a ciki.......Ummatu ce ta shigo da jug d'in kunu da mai daidaiciyar silba da 'kosai a ciki.
Abin mamaki cikin mutuncin Gwaggo ta kar'ba "Sannu 'yar albarka ai Ibrahim yayi sa'ar mata Rabi wallahi ina jin dadin zama dake sabida kina mutunta ni Allah yayi miki albarka."
Ita kanta Ummatu sai da tayi mamaki da yake tasan halin Gwaggo sai tayi dariya kawai ta girgiza kanta ta fita daga dakin....Nima dana san dani take ban tanka mata ba na cigaba da duba text d'in da Alhaji Nura ya turo ina mamakin al'amarin.....Kiran wayarsa ne ya katseni da sauri na d'aga nasa a kunnena.
Yanda ya amsa gaisuwata yasa naji jikina yayi sanyi nace."Alhaji naga text dinka amma kuma ban fahimci abinda kake nufi ba."
A d'an fusace! yace."Sa'ida kada ki mayar dani 'karamin yaro mana, jiya kin turo min text din daya hanani bacci amma yanzu kina wata magana."
A nutse nace."Alhaji kayi hakuri kayi min bayanin da zan fahimta na dai ga text d'inka amma ban mayar maka da replay ba."
Ajiyar zuciya ya sauke yace."Haba Sa'ida kada kiyi wasa da hankalina mana, nifa ba yaro bane ballanatana kizo min da wasa da gaske nake auranki zanyi amma me yasa kin san akwai al'kawarin aure a tsakaninki da yaron nan Khalid kikayi wasa da hankalina."
Jikina yayi sanyi nace."Wace irin magana ce wannan waye kuma Khalid."? Lokacin da nayi maganar tayi daidai da lokacin daya shigo dakin shida Gwaggon suka zuba min ido....na cigaba da cewa."Alhaji ina tambayarka kayi shuru waye Khalid da har kake wata magana akansa yanzu a duniya na rasa mijin aure sai Khalid dan Allah ka daina wannan maganar sannan kuma text d'in daka gani mybe shine ya dauki wayata a bayan idona ya turo maka amma ni da hannuna wallahi ban tura maka wani text ba."
Ajiyar zuciya ya sauke yace."Okey to har naji dadi a cikin zuciyata yanzu a'ina maganarmu ta kwana."? nace."Insha Allahu yau ko gobe zan yanke shawara.'' Yace."Haba Sa'ida wace irin shawara ce wannan da har yanzu ba'ai yanke ba."?
Nace."Alhaji ka 'kara hakuri dan Allah." Yace."Shikkenan tom ina sauraranki." Sallama mukayi na kashe wayata rai a 'bace na kalleshi yana tsaye idonsa ya kad'a yayi jajazur!! sai wani irin kallo yake min.
"Khalid waye ya baka izinin d'aukar min waya."? Kai tsaye yace." Ni ne na bawa kaina izini ko kina da abinda zakiyi ne."? Cike da mamaki! nake kallonsa.
Ya zare min manyan idonsa da suka rine da 'bacin rai da 'bakin kishi yace."Ni kike ciwa fuska ko."? Nace."Meye abin cin fuska sarkin tsaurin ido ina kai ina Alhaji Nura da har zaka dauki wayata ka rubuta masa text kasan dai ya kusa haifarka ko."?
Yana 'kokarin magana Gwaggo tace."To daya kusa haifarsa mai zai nuna masa? namiji yake shima namiji yake sannan duk abinda yake dashi shima yana dashi sai me kuma."?
Kallonta nayi tace."Mara mutunci wacce bata san mai sonta ba, dame Alhaji Nuran yafi Khalid da har zaki dinga ci masa fuska."
Nace."Kinga Gwaggo ki cire kanki daga cikin wannan maganarki babu ruwanki ni babu wanda ya isa yayi min dole a gidan nan wanda nake so zan aura bana auran 'karamin yaro a kyaleni."
Gwaggo ta fashe da kuka had'e da fad'in "Zagi na Zakiyi ne naga kina zaburowa ko kuma dukana zakiyi butulu kawai."
Hawaye suka shararo min nace."Me nayi na butulci kuma? ina zaune a gado na mahaifina ina ciyar da kaina sai me? me nayi na butulci da har kike kirana da kalmar."
Jikinta ne kuma yayi sanyi ganin ina kuka.....Girgiza kansa yayi ya fita daga d'akin zuciyarsa kamar ta babbake saboda 'bacin rai.
Bayan fitarsa na share hawaye mi'kewa nayi na fara had'a kayan wanki, sai naga tana satar kallona cigaba nayi da abinda nake tace."Sa'ida kinga yau 'kosan yayi kyau gashi da zafinsa ki zuba kunun kisha sai kiyi wanki."
Nace."Aa Gwaggo ba zan sha kunu ba kisha kawai.'' Shuru tai tana kallona tsaf na gama had'a wankin na fita dashi can bakin rijiya na zubesu komawa dakin nayi na dauko indomee biyu 'karamin gas d'ina na kunna na d'ora tukunya da ruwa akai na zuba indomee a ciki.....ina zaune a gurin ta dahu na juye a plate kana na kashe gas d'in. Nan tsakar gidan na zauna a nutse naci na fara ci ina Nazarin rayuwa wai ni Gwaggo take kira da Butulu hummm! rayuwa kenan.
*Masoya a taimaka da sharing👏🏼*
Yanda yaga jikinta na rawa yasa yayi saurin rike hannunta a nutse yace."Aunty Sa'ida ina zaki da sassafe haka? yau asabar babu makaranta."
Zuciyata ta karye na daure ban bari hawayen sun zuba ba nace."Khalid Sake ni." Girgiza kansa yayi a tausashe yace."Ba zan sake ki ba aunty dan na lura bakya hayyacinki."
Ido na tsira masa shima ya tsira min nasa, a haka Baba Iro ya shigo ya same mu....Gyaran muryar da yayi itace tasa muka ankara da shigowarsa yace."Lafiya na ganku a tsaye a soro."?
Hannuna dake cikin nasa ya sake ri'kewa yace."Baba da alama babu lafiya dan nima nazo shigowa mukayi karo da ita zata fita a gigice.''
A nutse ya kalleni da fadin"Sa'ida me yake faruwa ne.''? Hawayen da nake kokarin dannewa suka kucfe nace ."Kawu maganar dai guda d'aya ce."
Yace."Gwaggo ce ko.''? kaina na d'aga nace"Eh tun jiya ta hanani zaman lafiya a dakinta tace aljanu ne dani kawai yanzu ina kwance na ganta a kaina tana bunka min haya'ki."
Baba Iro ya shiga girgiza kansa yana mamakin halin rigima irin na mahaifiyarsa. yace."Sa'ida kiyi hakuri kinji ko mu shiga gidan za'a sasanta."
Nace."Kawu nifa idan ba haya'kin nan ta daina bunkawa ba ba zan shiga dakinta ba."
Khalid yace."Muje duk inda haya'kin yake zan daukeshi na yar dashi."
Jin abinda yace yasa na yarda muka shiga gidan a tare.
Suna tsaye ita da Ummatu suna magana......"Wallahi ajanu ne da ita gashinan daga jiya zuwa yau duk ta kasa nutsuwa sakamakon turaran da nake mata kinga yanzu tayi waje a gigice." Ummatu tace."To ai kuwa tunda dai an gano bakin zaren sai a cigaba da nema mata magani.....shigowarmu yasa duk suka kallemu.
Khalid kai tsaye dakin ya nufa yana neman maganin Gwaggo kamar ta sani ta dauka ta bawa Ummatu ta 'boye mata....Kawu Iro yace "Gwaggo wannan wace irin rayuwa ce dan Allah ya kike nema ki furgita yarinya kina cewa tana da aljanu a ina suke? Gwaggo na fad'a miki ki daina yarda da surutan mutane akan yarinyar nan shi aure lokaci ne dashi idan lokacinta yayi za tayi aure amma dan Allah ki daina d'ora mata lalura yanzu ina amfanin abinda kikayi Gwaggo da sassafe kin bunka a haya'ki a gida kin firgita yarinya tunda tace bata so ba sai ki k'yaleta ba."
"Kai Ibrahim ba fa zanyi asarar kudina ba dole sai nayi haya'kin nan tunda d'akina ne kuma idan ba aljanun ne da ita ba me yasa take guduwa mu da muke shak'ar haya'kin me yayi mana saboda haka ba zan fasa abinda nayi niyya ba idan tana da inda za taje ta tafi."
Khalid ya fito daga dakin fuska a murtuke yace."Gwaggo ina haya'kin naga irinsa." Kallonsa tayi lokaci guda ta fahimci abinda yake da akwai tace." Babu sauransa kenan nasa a wuta."
Kawu Iro yace."Gwaggo jiya ma fa haka kika ce sai gashi kuma yau da safe kin kuma kunnawa." Kuka ta fashe dashi tace."Yanzu dai kunyi min taron dangi kenan kuna kokarin 'karyata ni ko."?
Kawu Iro hankalinsa ya tashi ya dinga rarrashinta tace."Oh!oh! Ibrahim ai 'yar d'an uwanka ta fini a gurinka tunda gashinan a kanta kana nema ka 'kure ni."
Yace."Aa Gwaggo wallahi ba haka bane ina ni ina 'kure ki nayi laifi ki yafe mun." Ba tare da tace komai ba ta shiga dakinta ta bar mu a tsaye.
Kallonsa nayi naga duk hankalinsa ya tashi nace."Kawu ka kwantar da hankalin ka insha Allahu zan cigaba da hakuri da halinta." Yace."Yawwa Sa'ida dama abinda nake so kenan naji daga gurinki kiyi ta addua kinji ko komai mai wuce wa ne." Cikin dauriya nace."To Kawu nagode." Gurinsu ya nufa ya barmu nida Khalid a tsaye.....Yace."Aunty Sa'ida kada ki damu duk inda ta 'boye haya'kin zan bincika a dakin."
Nace."Khalid kyaleta dakinta ne fa tayi duk abinda take so da abunta." "Eh d'akina ne Sa'ida idan kinyi zuciya kada ki sake shigowa." Tana daga cikin dakin take magana.
Yace."Gwaggo wace irin magana ce wannan."?
"Haba Jarumi ai dole raina ya 'baci akan al'amarin nan ranar da naje 'karbo maganin nan sai da na yini banci ba bansha ba salloli na ma sai had'asu nayi amma saboda wukalancin Sa'ida ta dinga kokarin watsa min 'kasa a ido.
Yace." To wai waye ya saki ne? sai fa da nace dake kada kije okey to zanje har gidan ita Uwalen da take janki yawon gurin masu magani na gargad'eta akan hakan ni idan kinyi min baki ba zai kamani ba tunda dai ni ba Baba Iro ba ne."
Kuka tasa daga cikin dakin take fad'in "Khalid kada kaje kaci mutuncin Uwale bata cancanci hakaba." Ya d'aga labulan d'akin da fad'in."To idan bakya so naje gidan Uwale dauko min haya'kin."
Tace."Shigo ka kar'ba." da sauri ya shiga dakin nima naji wani sanyi a cikin raina.......Wani tsohon magani ta d'auko masa a 'karkashin gadonta a daure a wata tsuhowar leda ta mika masa da fad'in"Gashinan wannan jaraba ta isheni haka."
Kar'ba yayi ba tare da ya tanka mata ba ya fito daga dakin.
Yana fitowa yace." Ki kwantar da hankalinki ga maganin nan a hannuna zan fita dashi na zubar."
Hannunsa na kalla a take na gane ba maganin bane domin wancan a k'ulle yake b'akar leda wannan kuwa ledarsa yaluwa ce.....girgiza kaina kawai nayi na wuce na barshi a gurin, dakin na shiga na sameta tana murd'a redion ta ta dago kanta ta kalleni ta dauke kai tana cigaba da abinda take......gurin dana kwanta na nufa na dauki wayata na nemi gefan gado na zauna wayar na kunna na fara dube dube a ciki.......Ummatu ce ta shigo da jug d'in kunu da mai daidaiciyar silba da 'kosai a ciki.
Abin mamaki cikin mutuncin Gwaggo ta kar'ba "Sannu 'yar albarka ai Ibrahim yayi sa'ar mata Rabi wallahi ina jin dadin zama dake sabida kina mutunta ni Allah yayi miki albarka."
Ita kanta Ummatu sai da tayi mamaki da yake tasan halin Gwaggo sai tayi dariya kawai ta girgiza kanta ta fita daga dakin....Nima dana san dani take ban tanka mata ba na cigaba da duba text d'in da Alhaji Nura ya turo ina mamakin al'amarin.....Kiran wayarsa ne ya katseni da sauri na d'aga nasa a kunnena.
Yanda ya amsa gaisuwata yasa naji jikina yayi sanyi nace."Alhaji naga text dinka amma kuma ban fahimci abinda kake nufi ba."
A d'an fusace! yace."Sa'ida kada ki mayar dani 'karamin yaro mana, jiya kin turo min text din daya hanani bacci amma yanzu kina wata magana."
A nutse nace."Alhaji kayi hakuri kayi min bayanin da zan fahimta na dai ga text d'inka amma ban mayar maka da replay ba."
Ajiyar zuciya ya sauke yace."Haba Sa'ida kada kiyi wasa da hankalina mana, nifa ba yaro bane ballanatana kizo min da wasa da gaske nake auranki zanyi amma me yasa kin san akwai al'kawarin aure a tsakaninki da yaron nan Khalid kikayi wasa da hankalina."
Jikina yayi sanyi nace."Wace irin magana ce wannan waye kuma Khalid."? Lokacin da nayi maganar tayi daidai da lokacin daya shigo dakin shida Gwaggon suka zuba min ido....na cigaba da cewa."Alhaji ina tambayarka kayi shuru waye Khalid da har kake wata magana akansa yanzu a duniya na rasa mijin aure sai Khalid dan Allah ka daina wannan maganar sannan kuma text d'in daka gani mybe shine ya dauki wayata a bayan idona ya turo maka amma ni da hannuna wallahi ban tura maka wani text ba."
Ajiyar zuciya ya sauke yace."Okey to har naji dadi a cikin zuciyata yanzu a'ina maganarmu ta kwana."? nace."Insha Allahu yau ko gobe zan yanke shawara.'' Yace."Haba Sa'ida wace irin shawara ce wannan da har yanzu ba'ai yanke ba."?
Nace."Alhaji ka 'kara hakuri dan Allah." Yace."Shikkenan tom ina sauraranki." Sallama mukayi na kashe wayata rai a 'bace na kalleshi yana tsaye idonsa ya kad'a yayi jajazur!! sai wani irin kallo yake min.
"Khalid waye ya baka izinin d'aukar min waya."? Kai tsaye yace." Ni ne na bawa kaina izini ko kina da abinda zakiyi ne."? Cike da mamaki! nake kallonsa.
Ya zare min manyan idonsa da suka rine da 'bacin rai da 'bakin kishi yace."Ni kike ciwa fuska ko."? Nace."Meye abin cin fuska sarkin tsaurin ido ina kai ina Alhaji Nura da har zaka dauki wayata ka rubuta masa text kasan dai ya kusa haifarka ko."?
Yana 'kokarin magana Gwaggo tace."To daya kusa haifarsa mai zai nuna masa? namiji yake shima namiji yake sannan duk abinda yake dashi shima yana dashi sai me kuma."?
Kallonta nayi tace."Mara mutunci wacce bata san mai sonta ba, dame Alhaji Nuran yafi Khalid da har zaki dinga ci masa fuska."
Nace."Kinga Gwaggo ki cire kanki daga cikin wannan maganarki babu ruwanki ni babu wanda ya isa yayi min dole a gidan nan wanda nake so zan aura bana auran 'karamin yaro a kyaleni."
Gwaggo ta fashe da kuka had'e da fad'in "Zagi na Zakiyi ne naga kina zaburowa ko kuma dukana zakiyi butulu kawai."
Hawaye suka shararo min nace."Me nayi na butulci kuma? ina zaune a gado na mahaifina ina ciyar da kaina sai me? me nayi na butulci da har kike kirana da kalmar."
Jikinta ne kuma yayi sanyi ganin ina kuka.....Girgiza kansa yayi ya fita daga d'akin zuciyarsa kamar ta babbake saboda 'bacin rai.
Bayan fitarsa na share hawaye mi'kewa nayi na fara had'a kayan wanki, sai naga tana satar kallona cigaba nayi da abinda nake tace."Sa'ida kinga yau 'kosan yayi kyau gashi da zafinsa ki zuba kunun kisha sai kiyi wanki."
Nace."Aa Gwaggo ba zan sha kunu ba kisha kawai.'' Shuru tai tana kallona tsaf na gama had'a wankin na fita dashi can bakin rijiya na zubesu komawa dakin nayi na dauko indomee biyu 'karamin gas d'ina na kunna na d'ora tukunya da ruwa akai na zuba indomee a ciki.....ina zaune a gurin ta dahu na juye a plate kana na kashe gas d'in. Nan tsakar gidan na zauna a nutse naci na fara ci ina Nazarin rayuwa wai ni Gwaggo take kira da Butulu hummm! rayuwa kenan.
*Masoya a taimaka da sharing👏🏼*